← Book details Ƙauna Biyu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 18 OF 56

Sashe 18

Ƙauna Biyu Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read

Saurin girgiza kai queen tayi kana cikin murya kuka tace.
”Har r abada ummie!, har abada bazan taɓa samun wanda ya kai yaya Aliyu sona da kuma ƙaunata ba, saboda ko tantama banayi cewar irinsa shi kaɗaine! Ummie tayaya kike tunanin zan SO wanin yaya Aliyu?, taya kike tunanin zan iya rayuwa irin ta aure tare da wanin yaya Aliyu? That will never happen again, forever and ever!”
Ta ƙarashe maganar tana me lumshe idanunta zafafan hawayen sukaci gaba da saƙƙo mata.
Tuni itama ummien hawayen suka cika idanun nata, na tsananin tausayin ƴar nata, sallamar da fareedah tayi ne ya sanya ummie saurin tashi domin hana hawayen ta damar sauƙa, da sauri tabar ɗakin tana cewa ”yawwa fareedatu ƙara da kika zo maza ki lallahi ƙawarki”. A raunace fareedah ta zauna tana zubama Fatima Idanunta da loƙaci guda suma suka yi ja.
”yaya Aliyu na gaza riƙe amanar ƴar amanarka!, na gaza yaya Aliyu!” tayi maganar cikin wata irin raunatacciyar murya, kafin taci gaba da faɗin.
”gata nan samm samm Fatima bata jin maganar kowa har yau ta gaza rungumar rashin ka da tayi yaya!, ina tsoron Allah ya kama Ni da laifin gaza cika ma alƙawarin dana ɗaukar ma kaina mai girman gaske!, pls fatyyyy ki taimaka ki daina zubar ma yaya Aliyunki ruwan hawaye haka nan. Roƙan sa na ƙarshe maganarsa na ƙarshe kece!, kece Fatimah yace na kula dake fiye da yadda zan kula da tawa rayuwar!”
Dakatawa tayi tare dajan ajiyar zuciya mai ɗan qarfi, kafin cikin sheshsheƙar kuka taci gaba da faɗin, ”saidai kinƙi bani damar hakan! kinƙi bani damar hakan taya kike tunanin idan da yaya Aliyu yana raye zai barki cikin ƙunci haka?, na riƙe ki da girman Allah ya zama wannan shine hawayenki na karshe akan mutuwar yaya Aliyu!”. Cikin kuka sosai ta ƙareshe faɗar maganan tana miƙe wa da sauri don barin ɗakin, Cikin sauri itama fatiman ta miƙe tare da faɗawa jikin fareedah.
”taya wai kuke tunanin zan iya mantawa da nurul qalb!?, taya kuke tunanin zuciyana zata ci gaba da zama cikin farin ciki!?, bayan mai bata farin cikin baya raye! Kowa haushi na yake ji na sani, kowa yana ganin na gaza karɓar ƙaddarar rashin nurul qalb ne. Ta ya ya zuciyana da ruhina zasu mantawa da mutum mafi muhimmanci acikin rayuwata?” ,kafin wani irin kuka mai ƙarfin gaske ya kwace mata. Kafaɗunta fareedah ta ɗago idonta cikin na Fatima tace, ”ba cewa akayi ki manta da yaya Aliyu ba, ba cewa akai ki daina tuna shi ba, cewa akai ki daina masa kuka kin san Mea yace min? A ranar dazai tafi.
” cikin zubda wahaye ta kuma duban Fatiman tace.
” cewar Ga Amanar ƴar Amana na Nan na bar miki, ki kula min da ita, fiye da yadda zaki kula da taki rayuwar!, ki kula min da ita har zuwa sanda zan dawo, ko sau ɗaya kada ki taɓa barinta ta zubar da ruwan hawaye ata dalilin rashina!, Duk da haka bai yi shiru ba duk kuwa da irin yadda Mama ta ringa ƙoƙarin hana shi maganar, bai haƙuru ba har yaje bakin qofa ya kuma duba na cikin muryarn dana kasa tance ta har kwanan gobe yace._ ki cika min alƙawarin da nabar Miki fa_ cikin zubda wahaye na dube shi kinsan me ne ce masa?”
Ta dubi tsakiyar idanun Fatiman tace.
”ce masa nayi_ I promise you! yaya nayi alƙawari” cikin ƙunar zuciyar da ɗacin tuno da ƴaƴanta tace, ”saidai kin gaza taya ni cika alqawarin yayana Fatima!” tayi maganar cikin wata raunatacciyar murya.
Wani irin ɗamke Hannuwanta Fatima tayi daura kanta a Ƙirjinta fareedah, kafin cikin sauri ta ɗago tana goge hawayen dake kwance saman fuskarta cikin murya mai kama da a zauce take.
”tace waye?" Inji wayeeeee yace Miki na gaza tayaki cikon alkawarin nurul qalb!, Insha Allah wannan shine ruwan hawayen da zai kuma sauƙa ata dalilin mutuwar yaya Aliyu Naaaaaa ” sosai itama fareedah ya rungume Fatiman kamin cikin zallar farin ciki tace. ”alhamdulillah! Alhamdulillah fatyyyy Naaaaaa yaya zai yi farin ciki dajin hakan da yana raye, Ubangijii Allah yaji ƙanka yayanmu” suka faɗa a tare, kafin su kalli juna sai kuma kowa ya shiga nuna ɗan uwansa suna sakin murmushi mai tafe da ruwan hawaye.

___________

*Amnah*
Cikin murna da tsantsan farin cikin dake ɗauke a fuskanta ta ce "Ammiey papiey ya kusa dawowa” amnah faɗa tana faɗawa jikin Ammiey cikin tsagwaron zallar farin ciki.
jan kumatunta ammiey ta yi tare da cewa "duk wannan murnarn dawowan papieyn kine?, to tsaya ma waina waya faɗa miki?” ammiey ta tambaye ta tare da zare farin siririn glass ɗin dake Idanunta.
”uncle Irfan mana ammiey, kuma murnarn ya kusan kawo min new Mamie ne manaaaaa” ta yi maganar tana sauka daga jikin ammien tare dayin woje a guje tana faɗin. ”ammiey kar nayi let na tafi school” wani irin murmushin tausayin amnah ammiey ta saki. Tana hasaso ranarn da ALIEYON TA zaiyi Aure.
da kuwa ita ne wacce zatafi kowa farin ciki da kuma murnarn wannan abu, Irfan dake tsaye tun ɗaxun ya zauna kusa da ammieyn, ”wanne irin farin ciki ne ya sanya ammiey na sakin murmushi ita kaɗai har haka?”, shine abinda Irfan ya faɗa yana ƙarasa zaunawa kusa da ammieyn nashi, still ta kuma sakin wani murmushin tare da kallon sashen da Irfan ɗin ke zaune, cikin tsananin zallar farin cikin haɗin da yanxun yazo mata cikin zuciyarta ne yasa kai tsaye tace da Irfan ɗin.
”yayanka nawa Mata” ba tare da fargaban komai ba ammien tayi maganar still dai murmushin na nan d
Shimfiɗe saman kyakkyawar fuskarta. Cikin shiga alamar ruɗu Irfan ya ce ”ammiey me ki kace? Kamar fa jinin jiki naji kina maganar yima mata?” wani irin murmushin baka da wayo ammien ta masa tare da cewa. ”shakku ka cire Irfan yayanka ALIEYO! Na yima mata wacce ta dace daidai da shi Insha Allah”
Murmushin ya saki shima domin ya riga da yasan halin yayan nashi cikin bayyana tsantsar gaskiyar sa yace, ”haba ammiey ya kamata kina ɗan jin tausayin jinin jiki haka nan mana, tun dai ba wani mugun abu yake mara ƙyaun da zai bada shaidar kasa riƙe kansa yayi ba!, pls sweetheart Ammeynmu kiyi haƙuri har zuwa loƙacin da yaya ALIEYON zai kawo matar da yake so da kansa har gida mana” , kallon baka da hankali ammiey ta jefi Irfan dashi tare da miƙewa tana barin main Parlourn tare da nufar upstairs nata.
Da kallo kawai Irfan yabi ammien yana jin wani irin bala'in tausayin É—an uwansa yayansa alieyonsa.
______________
Chapter 18 · 0% Book details