← Book details Ƙauna Biyu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 14 OF 56

Sashe 14

Ƙauna Biyu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Abba fitowar sa daga masallaci keñan yaji wayarsa na Ring alamar shigowar ƙira, rass yaji gabansa ya buga tare da wani irin tsoro daya ji ya kanainaye shi loƙaci guda. Cikin mazari ya fito da wayar dake gaban rigarsa, *ALIYU* shine sunan daya gani.
Wata irin tsinkewar zuciya ne ya ziyarcesa loƙaci guda cikin jarumtaka yayi picking tare da kara wayar a kunnensa, daga cen bangaren masu ƙiran kuwa bayan sunyi sallama sun gaisa da Abba, a nutse suka ce dashi. "Malam ko kana da alaƙa da wannan me wayar?” cikin mahaukacin bugun da zuciyarsa Abba ke yine ya amsa da.
”Ehhhhhhh! Ehhhhhhhhh!! Nine mahaifin mai wayar. Jin a yadda ya amsa sune a kiɗeme ya san masu ƙiran ƙara nutsuwa da ƙyau kafin cikin son kwantar masa da hankali suka ce dashi, ”wannan me wayar ya sami ɗan ƙaramin accident ne, amma alhamdulillah komai yazo da sauƙi, yanxu haka yana Muslim specialist hospital zaria”
Cike da fawwala Allah al'amurransa ya datse qiran bayan yace musu gasu nan xuwa. Yana ƙoƙarin tafiya domin sanar da iyalinsa halin da ake ciki ne saiga Abban Fatima shima ya fito a masallacin ganin Abban aliyun duk a ruɗe ya sanya shi dakatawa, yana tambayar sa abinda ke faruwa, Cikin tashin hankali yace ”aliyu ne yayi accident a zaria,shine ƙiran da akimin yanxu. "Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, Aliyu kuma Bashir” kansa kawai ya daga masa yana shirin shiga gidansa, "a ahhh dawo Bashir ba'ayi haka ba, kawai kazo mu wuce zarian! barin ƙira jabiru yazo ya kai mu ” yana shirin ƙiran yaya jay ɗinma saiga shi ya sanyo kansa cikin anguwar. Dawowarsu kenàn da Aliyu daga inda suka je ya biya ya sauke shi a gida, shine shima ya iyo nasu gidan, ganin iyayen nasu a tsaitsane na ya sashi yin parking tare da fitowa da sauri yana tambayar abinda ke faruwa. ”kaga jabiru ba loƙaci muje ka sauke mu a Zaria ƙanin kane Aliyu ya sami accident a yayin tafiyarsa abuja” da sauri yaya jay ya ɗago kansa ba shiri yana duban mahaifinsa da yayi maganar.
”abba Aliyu fa kace naga nine da kaina ɗazu na kaishi tasha ya hau mota!”. kansa kawai Abba ya iya gyaɗa mishi ”jabiru in banda abinka to ya za'a yi da ikon Allah, koda kai ɗin ne kuwa ka kaishi da kanka dole hakan saiya faru!, domin rubutaccen al'amari tun daga rabbis samati wal'arat” Abban aliyun ya bashi cikakkiyar amsa cikin nuna jarumta.
”ba loƙacin ɓatawa loƙaci loƙacinsa bane jabiru muje kawai” Abban Fatima ya faɗi maganar suna shiga cikin motar da sauri shima yaya jay ɗin ya faɗa motar tare dayin reverse yana jan motar da wani irin mugun gudu. Yana ɗaukar hanya ɗoɗar. Ganin shirun yayi yawa ne ya sanya yaya Nurien dake zaune a parlour shida mahaifiyarsa sai Fatima dake zaune dab dashi ya sanyata a tsakanin ƙafafunsa yana bata maganin ciwon kai, domin fatiman taku badai shegen ƙin maganin masifa gareta sai anyi da gaske take sha, kuma dama yaya Nurien shike sanyata sha dole. Kai tsaye dialing Number'n yaya jay yayi daga ce mishi gashi nan yama shigo cikin anguwar amma shine har yanxu shiru shiru bai ƙaraso ba, gashi yana ɗan son fita da motar ne shine ma dalilin zaman jiran nashi da yake. A handsfree ya sanya wayar yana ɗaurata saman cinyarsa shi kuma yaci gaba daba queen magani. Yana tuƙin hankali tashe ƙiran ƙanin nasa ya shigo masa, kai tsaye ya danna picking tare da kara wayar a kunnensa.
Ba tare daya bari nurien ɗin yace komai bayane yace,”hello nurien kana jina yanxu haka muna hanyar zuwa Zaria nida Abba da kuma abban aliyu, Aliyu shureim ne ya sami accident a hanyarsa ta zuwa Abuja!, amma kada ka faɗawa kow....... uban Ihun da fatiman ta ƙwala ne ya sanya shi dakatawa da sauran maganar da yayi niyyar faɗa. Kafin kowa ya ankare tuni Fatima har ta bar parlourn da mugun gudu, don daga ummien har yaya Nurien mutuwar zaune su kayi. (Aliyu!, Aliyun dai da yazo ya mata sallama ɗaxun shine yayi accident) haka ta shiga nanata wa acikin zuciyarta.
Mama da fareedah dake zaune a kan akan darduma mama tasbaha rike a hannun ta ita kuma fareedah Alqur'ani ne a hannunta tana karatu, cikin wani irin sanyi jiki domin daga ita har Maman sun gaza matsawa koda. Nan da cenñnn ne, shigowar Fatima a guje da kuma irin uban kukan da take yine ya sanya Mama miƙewa a firƙice, a ɗimauce cike da tsantsarn tashin hankali ta shiga tambayar ta.
”fati! Fatima!! Ke fati mene ne?, meya faru? Mutuwa akayi!, wani abu y faru da kowa ne” sammm ita kanta Maman ba'a cikin hayyacin take mata duk waɗan nan tambayoyin ba, cikin sarƙewar numfashi tace ”Mah mah Mama Aliyu ne ” a fusge ta ƙwato kalmomin ta haɗe su wuri guda. Take jikin Mama ya shiga wani irin mazari ta ƙara riƙo fatiman tsam a jikin ta tace, ”ya mutu ko, dama naji a jikina wannan tafiyar ba Alkhairi bace innalillahi wa'innah ilair rajiun!, Fatima karki cuceni ki faɗa min mene ya faru da Aliyu na?”.
Cikin galabaituwa tace, ”Mama wai yayi hadari ne shi ne!, shine yaya jay ya ƙira yaya Nurien wai karya faɗawa kowa amma sun tafi daukosa” sakin Fatima maman tayi tare da komawa zaune a sulale. "Shike Nan!, shike Nan, Allahu yaji ƙanka Aliyu shureim, yaron kirki ɗan albarka Ilahi ya karɓi baƙuncinka” sune kawai kalaman da mama ke nanata wa, fareedah kuwa sumewar zaune tayi ba tare da kowa ya san ta sume ɗin ba. ”bafa mutuwa yayi ba A'isha accident ne kawai ya samu, kuma alhamdulillah har ma sunje zarian zasu taho dashi ne gida domin mun fisu kayayyakin aiki masu ƙyau” ummien Fatima ce tayi maganar tana dafa ƙafaɗun Maman. Ita dai ƙala bata kuma cewa ba sai zuru da tayi ta zubawa guri guda ido. Fatima kuwa ajiyar zuciya kawai take sauƙewa a kai akai, da sauri ummie ta shiga girgiza fareedah domin taga tunda ta shigo ko motsi bataga tayi ba. A razane ta ce ”yaya Aliyu Naaaaaa!" Sai kuma a loƙacin ta samu damar fashewa da wani irin kuka mai azabar ƙarfin gaske. Yaya Nurien ne cikin zafin rai ya daka musu tsawa, yana faɗin "ku dallacen ku mama shiru idan bazaku masa addu'a ba ku tashi kuba mutane wuri” tsittt sukayi tamkar anyi ruwan sama an ɗauke.
Anan Mama taci gaba da zama dasu maman Aliyu har zuwa loƙacin da yaya jay ya ƙira nurien yake shaida masa sun ɗau shi, suna asibitin Aminu Kano loƙacin wajajen magriba ne. duba da cewar accident ne a cenñnn ma Saida suka yi ta fafatuka kafin a basu aliyun donma da yaya jay, kasancewarsa sananne kuma ƙwararren likitan dake aiki a waje, badan haka Bama da abin baizo da sauƙi har haka ba. Tuni suka kwaza suka yi asibitin Aminu Kano su dukansu.
Duk idan ka dubi kowannensu zuwa loƙacin yayi wujiga wujiga, sai dab da isha'i aka ba su Mama damar ganinsa.
Wani irin kwantaccen murmushi ne kwance saman fuskarsa loƙacin da hannun na dame ke cikin na Mama na hagu kuma ke cikin na Fatima. Cikin ƙarfin hali da kuma dauriya da nuna jarumtaka ya matse hannun mama dakyau yana dubanta. ”mama kin manta nace banson ganin kukan ki!, kukan ki yana ƙona zuciya ta fiye da tarin raunikan dake cikin jikina a yanxu, Lumshe Idanunsa yayi tare da taune lips ɗin sa da ƙarfi yace.
“Ki daina zubar min da hawayenki Mamana!, ko kinason azabar ƙabari ya tabbata akaina, bayan kuma gashi cennn ina hango irin tarin ni'imomin da aka danatar min?,Mama inaji raɗaɗi da zafin ciwo dako ta ina dake jikina kimin min addu'a, ba kuka ba!” amsa

Cikin sheshsheƙan kuka ta kallesa still hawaye na zuba daga cikin Idanunta cikin wata raunan'niyar murya tace.
”na dai na!, na dai na amma kaima ka daina raunana min zuciya mana da irin kalaman ka wanda suka fi zafi zafi!, wanda suka fi ruwan dalma narka zuciya!, kalaman da nake jinsu tamkar sauƙar mashi acikin ƙahon zuciyata”

inaji raɗaɗi Mama!, Mama ko ina fa ciwo yake min zafi nake ji da zafin ciwo kafin wasu irin zafafan hawaye su zubo mishi, duk kuwa ƙoƙarin sa na son ganin ya hana hawayen nashi sauƙa, amma Saida suka saƙko ɗin.

da sauri fareedan tace, ”Toh Yaya Aliyu me yake saka kuka?, ina da ina ne suka maka zafi da ciwon Idan muna da iko zamu raba ka dashi”
Girgiza kai yayi tare da rintse idanunsa kana yace.
“Ba zai rabu ba fareedah domin Allah ya riga da ya fimu sanin abinda shine mafi Alkhairun mu, kuma bana fatan ɗaya daga cikin ku ya gaza amsan ƙaddarar rashina a cikin ku!, na riga da nasan wa'adin da Ubangijiin sammai da qassae ya ɗibar minne yazo ƙarshe.
Badan faɗa da ƙaddararta ba, a'a saidan dama nasan dole zan mutu!, zan tafiiiiiiiiiii na barku tafiya tahar abada, fatana da burina kowa ya karɓi ƙaddarar rashina data zo muku!,lumshe idonsa yayi yana mai jin wani irin yanayi azuciyar kana ya buɗe su tare da duban Fatima yana damkar hannunta da wani irin mugun karfin gaske, rinannun idonsa ya zuba mata kafin wani irin murmushi ya wanzu saman kyakkyawar fuskarshi yace mata.

”kin gani ko?, dama ai nace miki bai zama lalle Allah ya tsara dani ne kaɗai zakiyi rayuwar aure dani ba, wata ƙila wanda Allah ya tsara Miki zakuyi rayuwar auren dashi nanan na dakon tsimayin zuwansa cikin rayuwarsa” da wani irin bala'in ƙarfi ta fusge hannunta daga cikin nashi. Cikin ƙaraji da masifar ƙarfi ta shiga faɗin.
Chapter 14 · 0% Book details