← Book details Ƙauna Biyu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 13 OF 56

Sashe 13

Ƙauna Biyu Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

”nurul qalb!" Ta ƙirayi sunan shi cikin wani irin sauti mai ɗan amo kaɗan, bai amsata ba kuma baima san ranayi ba. Jin yayi shiru ne ta ta ɗago kanta wani irin karyar da wuyan ta tayi tare da zuba masa nata idanun itama, haka kawai yau ɗin ta tashi da wani irin sanyin jiki.
A raunace ta kuma ƙiran sunan shi”nurul qalb!” aɗan firgice ya ɗago kansa yana sakin ajiyar zuciya mai qarfin gaske, nazo muyi bankwana ne Queen ” da sauri tace "ban kwana kuma qalb?, to ina zaka je da zaka min bankwana?," da sauri ya dawo seti tare da faɗin, "au na manta nazo muyi sallama ne ki yafe ni,na yafe ki Insha Allah yau loƙacina ya cika".
Cikin tsare shi da ido tace "nifa ƴan kwanakin Nan samm bana gane kalamanka yaya Aliyu, wanne loƙacin naka ne kuma yayi?" Tayi Maganar da alamar tambaya.
"Ina nufin loƙacin zuwa wurin aikina ne yayi kinsa da tuni a wancen satin naje, sai aka sami ɗan akasi tafiyar ya fasaya, to shine fa jiya bayan nabar Nan ƙiran gaggawa ya same ni, na lalaaie ana nema na yau!".
Wata iriyar ajiyar zuciya ta sauke tana jin yadda duk wasu nau'o'in jijiyoyin dake jikinta suka mimmiƙe, tsintar kanta tayi dajin wani irin azababben tsoro, tsoro na tashin hankali marar misaltawa, cikin wani irin wahalallen yanayi tace "inajin tamkar kada kayi tafiyar nan, ina jin tamkar kana shirin rabuwa da nine nahar gaban abada, inajin tsoro inajin tsoron wani abu da bansan ko miye shi ba"
”MUTUWA”
Ya bata amsa, a kiɗime ta miƙe tsaye ta soma jijjaga kanta”bana so bana son jin kalmar ka dene min zancen abinda zai nisantaka dani pls, ka dena min batun mutuwa haka nan mana!, ba kaga muna shirin mallakar juna bane!! Ba kaga AUREN mu saura kwanaki biyar suka rage mana ba?" Pls na tsani kalmar ma tsani jin kalmar daga gareka I HATE YOU!” cikin ƙaraji ta ƙarishe maganar tana rushewa da wani irin kukan bala'i irin mai ƙona zuciyar nan. Jikinsa kawai ya janyota yana jin ƙaunar ta tamkar yau ya fara sonta, amma shi ya riga da ya sani ba tun yauba ƙaddara ta riga fata.
Cikin wani irin yanayi yace, ”ya zamu yi da ƙaddarar da ke shirin tunkaro mu!, batun mutuwa kona Miki,ko karna Miki ya zama dolen doliya, tabbas zan tafiiiiiiiiiii saidai yaushe ne?" Yaune?, yanxune?,gobe ne?" Allah ne masani queen, idan yaso kuma sai kiga ya barmu munyi rayuwar aurenmu mai cike da annushuwa da tsantsarn farin ciki, idan ya so kuma ya tanaja miki mijin daya fini nagarta,sanin Chanchanta,wanda zai kula dake fiye da yadda Ni zan kula dake!, wanda zai baki soyayya fiye da soyayyar da xan baki, wanda zai soki fiye da yadda nake SONKI, wanda zai ƙaunaceki fiye da yadda nake ƙaunarki queen!” cikin sheshsheƙar kuka tace,
” babu! Ba 'ayi wanda zai soni ba bayan kai yaya Aliyu, bana son rayuwa da kowa idan harba kai bane, da kuwa daga wannan loƙacin na daina ganin ko wanne Namiji a matsayin miji Saidai na kalleshi a matsayin ƴar uwata mac....

Kukan daya ci ƙarfin ta shi ya hanata ƙarasa magan ganunta, ”kada kiyi butulci ga mahaliccin mu FATEEMERH,Ki sani ruwa Iska tsanani babu abinda ya Isa ya sanja ZANEN ƘADDARAR MU, zaki iya dole zaki amshi baƙuncin wani na bani ba” da wani irin masifar qarfi ta fisge jikinta a nashi tana yin ɗakin ta masifar gudu. Duk yadda yakai ga tsayar da ita amma taƙi tsayawa. Kuka take tamkar wadda aka ce mata ya mutu, bayan kuma gashi a gabanta, gidansu, parlourn ummienta.....
Hawayen da suka cika idon sane suka sami damar zuba masa, cikin raɗaɗin zuciya ya goge yana barin gidan baki ɗaya, a bakin get ya haɗu da yaya jay, bayan sun gaisa yake sanar dashi zai je Abuja ne an ƙira shi akan batun aikinsa, anan yaya jay ya juya kan motarsa tare dacewa suje ya kaishi tasha ya hau mota, har yake sanar dashi badan ƴar fita ce ta kamasu ta gaggawa ba shida aliey daya kaishi, shidai kawai Aliyu shureim murmushi ne nashi, suna ɗan taɓa fira kaɗan kaɗan a haka harya mika shi tasha ya hau mota, kafin ya jiyo gida.
Da addu'ar shiga Mota a bakinsa ya shiga, bayan motar ta gama cika driver yaja motar tare da yin reverse yana ɗaukar hanya. Wani irin murmushi tare da hawaye ne suka saƙka mishi lokaci guda, a daidai sanda suke barin cikin garin na Kano baki ɗayaaaaa.

(Ya Ilahi ya mujibud da'awati) Allah ya saukeƙa lafiya Aliyu shureim, sai mun zo amsar tsara ba🤞🤞👌

A gimtse 🫰💪🥰

*BY AMMEY LAYLERH ✍️*

08104493215

*💘🌺ƘAUNA BIYU 🌺💘*

~Heart touching love, with love a side 🤍🤍~

Page 15&16

*BY*
*AMMEY LAYLERH*

✯ *~🌠 OFFICIAL MIRRAH 💫~*

*Alhamdulillah forever and always 👏*
__________________________

♥️🤍♥️

Da sauri Mama ta dafe daidai setin zuciyarta jin wani irin mummunan bugu data mata, zaune takai gefen gadon da take shirin tashi. ”Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un” ta furta tana jin yadda gaba ɗaya wata iriyar kasala ta mamaye ta. Acikin jikinta taji tamkar wani sashi na jikinta na dab da rabuwa da ita.
Adda'oi ta shiga gurtawa a ƙasan ranta tana neman tsari da koma meke shirin tunkarota yazo mata da sauƙi. Kasa fita tayi domin bata jin zata iya tashi ma adai yadda take ji ɗin nan.

*Queen*
Zaune takai tana rabka uban tagumi domin wani irin masifaffan da taji zuciyarta na mata. Ummie dake faman zabga mata ƙirane taji shirun yayi yawa ya sanya ta shig ɗakin nata kai tsaye.
”fatimah” ummie ta ƙirata da ɗan ƙarfi ganin tamkar ba'a hayyacin ta take ba, jin ummienta na ƙiran ta ya sanya firgigit tadawo da ita natsuwarta, da sauri tanufi wurinta, jikinta kawai ta faɗa domin wani irin rauni taji mai wuyar misaltuwa tattare da ita, ita kanta bata san mene hasalin abinda ya haifar mata da hakan ba.
”fatimah! Lafiyar ki kuwa? dubi yacce kikai zuru² loƙaci guda, baki da lafiya ne?, kodai period naki ne zai zo?, to kuma ai baki daɗe dayin wanka bama acikin ƴan sati kan nan kikayi al'adarki" haka ummie ta shiga jero mata tambayoyi, domin tasan babbar ciwon dake galabaita Fatima shine ciwon mara yayin period nata.

Bata da takamaiman amsa da zata ba ummienta nata domin ita kanta bata san meke damunta ba, kuka kawai ta fashe dashi tana jin yadda zuciyarta keci gaba da bugun bala'i. Hannun mahaifiyarta ta kamo ta ɗora akan Ƙirjinta tare da faɗin. "Ummie ƙirjina gaba na!, gaba na f...…. Kasa ƙarasawa tayi sakamakon wani irin harbawa da zuciyarta tayi da ƙarfin masifa. Cikin tsananin kiɗima ummie ta rungume yarinyanta tana faɗin, ”innalillahi wa'inna ilair raji'un, meke shirin faruwa damu har haka?"
Cikin fusgar numfashi tace "bah bah ban sani ba Nimaaaaa ummieeeee" a fisge tayi maganar, sunayen Allah ummie ta fara tofe Fatima dashi, tare da duk wasu nau'o'in adda'ar da yazo bakinta.

”Innalillahi wa'inna ilair raji'un” mutane suka shiga faɗa a tare a kuma ɗimauce ganin wani irin mugun accident da akayi tsakani wata babbar mota, irin masu ɗibar fetur ɗin nan wani irin mugun ƙarane ya kuma karaɗe wurin sakamakon sake bi ta kan motar da wannan babbar motar tayi. Wannan Mummunan hatsarin shine ya ja hankulan mutane da yawa harda ma wanda ke nesa da wurin. Tuni bayin Allah jama'ar Annabi suka cika wurin domin ceto rayukan bayin Allahn dake cikin motar, ganin bututun gas ɗin ya ɓalle ya fara fidda wani irin turniƙakken hayaƙi ne ya sa cikin azama da tashin hankali,suka fara kiciniyar fito da mutanen dake cikin motar.
Driver suka fara ciro babu alamun rai tattare da shi, sun ciro na biyun kenan gas na motar ya fashe, ji kake wani irin tushhh rududu, da masifar ƙarfi da kuma son ceto rayukan su mutane kowa ya fara neman hanyar tsira, amma duk da haka waɗan nan mutanen Saida suka sami nasarar guduwa da gawar drivern da kuma wannan mutum ɗayan da suka ciro.
Baki ɗaya gurin ya dauka salatin jama'a da kuma hayaniyarsu. Ganin ɗaya daga cikin mutane biyun da suka ciro ɗaya ƙafarsa na motsa wa ne ya sanya sukayi kansa a guje, tabbas motsini yake kafin jama'ar wurin su cika da al'ajabin gani wasu ƴan raunuka ne kaɗai a jikinsa, daidai Nan kuma ƴan kwana-kwana suka iso wurin. A take suka shiga ƙoƙarin kashe wutar dake ci kamar wacce ake ƙara rurata. Sukuma sauran jama'ar ne suka yi kan wannan bawon Allah da yake motsi sosae zuwa loqacin, Ambulance suka ƙira na kusa da cikin garin dake zaria, cikin abinda bai wuce mintuna goma ba motar ambulance ta iso, kai tsaye suka sanya su duka biyun a motar ambulance ɗin. Bayan sun sami damar cire wayar dake jikin wanda yake motsin nan, acikin aljihun wandon dake jikinsa. Kai tsaye suka shiga cikin contact nashi, *ABBANA* itace numbern da sukayi dialing kai tsaye.

***********
Chapter 13 · 0% Book details