Sashe 93
Yar Bangar Siyasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Wasila tace" Kinga dama abinda nake ta so ki gane krnan nima nasan da bai sameni da budurci ba da tuni ya sakeni wallahi." Uwani ta goge hawaye tace"A koda yaushe ina alfahari dake Wasila kuma kullum cikin shi miki albarka nake shiyasa kike ta samun cigaba a rayuwarki, nasihata zuwa gareki shine kiyi wa mijinki biyayya ku zauna lafiya da juna kada naji kada kuma nagani yanzu wannan mutumin shine uwarki da ubanki kuma shine gatanki duk wani umarni da zai baki kibi mutukar bai sa'bawa addinin Allah ba." Wasila tace"Insha Allah Uwani zanyi kokari nagode....... Wasila ta irgi kudi kimanin dubu dari biyu ta zuba mata cikin akwatin tace "Uwani gashinan ki siyi waya kiyi sana'a da sauran ga numbar wayata zan rubuta miki idan kun koma gida sai ki kirani mu dunga gaisawa duk kuma abinda kike so ki siya kici abinda baki dashi kiyi min waya insha Allah zamu zo nida rashida bada jimawa ba." Uwani tace"Kudin da kika bani basuyi yawa ba kuwa kada na aje Kuluwa ta sace." Wasila tace"Kada ki aje akwatin a gidanta ki kai kayanki kidan Inna Tabawa." Uwani tace"Yawwa to hakan zanyi." Mi'kewa sukayi a tare suka fito palo, suka tarar da Rashida da Kuluwa sai musayar yawu sukeyi Hajja na musu dariya Kuluwa da dai taga kowa nayi mata kallon mahaukaciya sai ta shiga taitayinta ta kimtsa kanta sai dai har yanzu ba ta daina mamaki da al'ajabi ba.
Uwani tace"To Hajja mun fito mu zamu tafi." Hajja tace"A'a ba zaku tsaya maigidan yazo ba ku gaisa." Uwani tace"Ai yamma tayi." Hajja tace"Kuma da naji Kuluwa tace kwana biyu zakuyi." Uwani tace"Haba Hajja kamar wasu marasa hankali ai tunda munga lafiyar yarinya da abinda ta haifa zaman me zamuyi." Kuluwa tayi saurin kallonta tana so tayi magana, Uwani tayi bala'in shan kunu babu fuska, Kuluwa ta sunkuyar da kanta 'kasa ranta duk a 'bace! lallai idan sun koma gida sai ta shukawa Uwani rashin mutunci tunda tana ba'kin cikin su zauna suyi kwana biyu su dandali arziki.
Hajja tace"To ke Wasila baki kira mijin naki a waya ba, ai be dace ba ace su zo baizo sun gaisa ba." Tace."Hajja kina ji fa Inna Tabawa tace shine ya tura aka d'aukosu ai yasan da zuwansu."
Hajja tace"Eh 'kwarai kam amma kika sani ko wani abune ya dauke masa hankali tunda kinga kwana biyun nan abubuwa da yawa suna dauke masa hankali, yana da kyau ki sanar masa da zuwan nasu watakila ko mantawa yayi." Tace"Shikkenan Hajja." Daki ta nufa domun kiran wayarshi kamar yanda Hajjan ta umarceta sam bata so suyi ta jayayya da matar.
Suna tare d
a khalifa yaga kiran wayarta sai ya aje wayar suka cigaba da abinda sukeyi shi da Khalifan wanda har ya shiga mamakin ganin bai daga wayar ba ya sanya yace."Da alama dai 'yan mata da zawaran dake damunka ne tunda naga baka dauki wayar ba.'' ba tare da ya bawa maganar mahimanci ba yace."Wasila ce." Khalifa ya kalleshi cike da mamaki yace."Lefi tayi kenan ake hukuntata ta wannan hanyar." Murmushin takaici yay mai tafe da bacin rai yace."Khalifa na ta'ba ganin wanda ya samu damar da wannan yarinyar ta samu a kaina kuwa."? Khalifa ya girgiza kansa yace."Gaskiya ban ta'ba gani ba nima kana sonta sosai dan duk wasu alamu sun nuna." Ya girgixa kanshi cikin takaici yace."Nima nasan da haka khalifa wannan damar data samu ce ta sanya take takani yanda ranta yake so yarinya 'kankanuwa ta dinga nuna ni da yatsa tana daga mun murya gurin magana tamkar zata zageni."
Khalifa yace."Subahanallahi! me ya janyo hakan." ?Tsaki yaja yace."Saboda kawai na nemi hakkina shikkenan cibi ya zama 'kari."
Khalifa yace."Ban gane ba."? A nutse ya kalleshi ya dan gyara zamansa ya soma warware masa abinda yake faruwa tsakaninsu."
Khalifa yace."Kai nifa shiyasa sam bana son wannan zaman jegon wallahi duk daga wannan zaman ake lalata maka mata , yanzu ita wannan matar abinda tayi shine dai-dai da girmanta da komai ta dinga d'ora yarinya kan turba mara kyau, idan bata sauke maka bukatarka ba gurin wa zakaje tunda kai ba manemin mata bane."
Ya sauke ajiyar zuciya ransa a 'bace yace."Allah Khalifa yarinyar nan tayi wasa sai na 'kara aure bana son hauka da da'ki'kanci wallahi kuma zata gane bata da wayo." Khalifa yace."A'a kayi hakuri dai ka cigaba da rarrashinta kasan yarinya ce."Tsaki yaja yace."Allah ya sawa'ke khalifa bazan kuma zuwa gunta sa wata bukata ba taje ra rike kayanta nima na rike nawa zan kuma fara neman aure."
Khalifa yace"Yanzu ka sauka daga kan ra'ayinka kenan."?
Yace."Duk wani abu da zanyi itace ta jawowa kanta ni babu ruwana." Khalifa yace."To Allah ya za'ba abinda yafi alkairi." Ya amsa sa ameen." Lokacin kiran ta ya sake shigowa wayar tashi yana ganin sunanta ya kashe wayar yana jan tsaki.
Cike da takaici da mugun ba'kin ciki ta fito daga d'akin murya na rawa Tace"Hajja bai dauki wayar ba watakila ko baya kusa da wayar ne." Hajja tace"E to hakan na iya kasancewa." Mikewa tayi ta shiga daki tana fad'in "Ku dan jirani na fito."
Uwani dasu Inna Tabawa suka mike Wasila ta jagorace su suka fita Ita Kuluwa zama tayi har sai da Hajja ta fito daga daki ta mi'ka mata karuwar ledar dake hannunta tace"Gashinan turaman atamfofine da mayafai da sabulai sai ku kasafta a tsakaninku." Kuluwa ta kar'be da sauri jikinta na kyarma sai washe bakinta take tana ta zabga godiya, Hajja tace."Babu komai Kuluwa ku gaida gida mungode."
Suna can parking spece Kuluwa takaraso hammatar ta ma'kale da ledar kayan da Hajja ta basu sai murna takeyi tace"To Wasila da Rashida mu mun tafi sai mun sake zuwa ke Wasila idan maigadan nawa ya dawo to ki mi'ka gaisuwata gurinsa tunda dai rowarsa kike mana." Wasila tana daure fuska tace"Zai ji ku gaida gida ku gaishe da Kawu Madu." Suka dinga amsawa da "ameen." Duk suka shiga cikin motar Garba yaja suka fita daga cikin gidan......Wasila da Rashida suka juya jikinsu a sanyaye suka koma ciki To itama Uwanin dai daurewa kawai takeyi amma zuciyarta babu dad'i sam! tana bala'in 'kaunar 'yayanta kamar yanda suke 'kaunarta.
Littafin na kudi ne......!
Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya kema keda Allah Whasap numbar
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*alliya:
'Yr Bngr Sys
*78*
_*Sa'ko na mussaman zuwa gareka Amadu 'kawayen Wasila irin su Mumy Farhan, Bomis Zainab kankara Mrs Aliyu Nafisa Buhari Hauwa Chindo, Sakina Ummee da dai sauransu, sunce kayi hakuri dan Allah karkayiwa Wasila kishiya kayi mata uziri saboda yarinya ce, idan kuma ka kuskura ka 'kara aure to zaka gane baka da wayo dan duk wacce zaka aura ba zata kama 'kafar Wasila ba, zaka dawo inda kake salati kana kiran sunan Allah😅🤭 babu ruwana Sistar Sakina ce tafad'a🕺🕺 sannan Sistar Jamila tace duk wacce zaka aura sunanta salamatu salam dan ba zata iya da jarabarka ba🕺 babu ruwana! Jamila da Ummee ne suka fad'a ni dai 'yar aike ce......Momyna tace kayi auranka dan ba Wasila ce kadai mace ba, takwara Fatima Yakubu ma haka tafad'a Sai sistar Hadiza Shall itama haka tace ka more rayuwarka, Shafa'a S Yari da Bilba sunce kayi aure ka more rayuwarka💃🏼🔥 ni dai na isar da sa'kona Amadu sai ka yanke shawarar da zata fishe ka, nima nace ba Wasila ce kad'ai autar mat.......🙊😌*_
Cikin sanyin jiki suka koma cikin gidan Hajja ta gansu duk babu kuzari a tare dasu tace"Ai kam ni kaina naso su zauna su danyi kwana biyu ku samu sakewa da mahaifiyarku amma ace daga zuwa sai su tafi wallahi banji dadin hakan ba sai kace wad'anda ake kora."
Rashida ta goge hawaye tace"Nima naso su zauna wallahi yanzu anti Wasila yaushe zamuje to." Wasila ta kalleta ranta duk babu dad'i tace."Sai an d'an kwana biyu baby tayi 'kwari zamuje insha Allahu." Hajja tace"Kwarai kuwa hakan yana da kyau, Allah ya kaimu ya bamu lafiya mai amfani." Duk suka amsa da "ameen."
Uwani tace"To Hajja mun fito mu zamu tafi." Hajja tace"A'a ba zaku tsaya maigidan yazo ba ku gaisa." Uwani tace"Ai yamma tayi." Hajja tace"Kuma da naji Kuluwa tace kwana biyu zakuyi." Uwani tace"Haba Hajja kamar wasu marasa hankali ai tunda munga lafiyar yarinya da abinda ta haifa zaman me zamuyi." Kuluwa tayi saurin kallonta tana so tayi magana, Uwani tayi bala'in shan kunu babu fuska, Kuluwa ta sunkuyar da kanta 'kasa ranta duk a 'bace! lallai idan sun koma gida sai ta shukawa Uwani rashin mutunci tunda tana ba'kin cikin su zauna suyi kwana biyu su dandali arziki.
Hajja tace"To ke Wasila baki kira mijin naki a waya ba, ai be dace ba ace su zo baizo sun gaisa ba." Tace."Hajja kina ji fa Inna Tabawa tace shine ya tura aka d'aukosu ai yasan da zuwansu."
Hajja tace"Eh 'kwarai kam amma kika sani ko wani abune ya dauke masa hankali tunda kinga kwana biyun nan abubuwa da yawa suna dauke masa hankali, yana da kyau ki sanar masa da zuwan nasu watakila ko mantawa yayi." Tace"Shikkenan Hajja." Daki ta nufa domun kiran wayarshi kamar yanda Hajjan ta umarceta sam bata so suyi ta jayayya da matar.
Suna tare d
a khalifa yaga kiran wayarta sai ya aje wayar suka cigaba da abinda sukeyi shi da Khalifan wanda har ya shiga mamakin ganin bai daga wayar ba ya sanya yace."Da alama dai 'yan mata da zawaran dake damunka ne tunda naga baka dauki wayar ba.'' ba tare da ya bawa maganar mahimanci ba yace."Wasila ce." Khalifa ya kalleshi cike da mamaki yace."Lefi tayi kenan ake hukuntata ta wannan hanyar." Murmushin takaici yay mai tafe da bacin rai yace."Khalifa na ta'ba ganin wanda ya samu damar da wannan yarinyar ta samu a kaina kuwa."? Khalifa ya girgiza kansa yace."Gaskiya ban ta'ba gani ba nima kana sonta sosai dan duk wasu alamu sun nuna." Ya girgixa kanshi cikin takaici yace."Nima nasan da haka khalifa wannan damar data samu ce ta sanya take takani yanda ranta yake so yarinya 'kankanuwa ta dinga nuna ni da yatsa tana daga mun murya gurin magana tamkar zata zageni."
Khalifa yace."Subahanallahi! me ya janyo hakan." ?Tsaki yaja yace."Saboda kawai na nemi hakkina shikkenan cibi ya zama 'kari."
Khalifa yace."Ban gane ba."? A nutse ya kalleshi ya dan gyara zamansa ya soma warware masa abinda yake faruwa tsakaninsu."
Khalifa yace."Kai nifa shiyasa sam bana son wannan zaman jegon wallahi duk daga wannan zaman ake lalata maka mata , yanzu ita wannan matar abinda tayi shine dai-dai da girmanta da komai ta dinga d'ora yarinya kan turba mara kyau, idan bata sauke maka bukatarka ba gurin wa zakaje tunda kai ba manemin mata bane."
Ya sauke ajiyar zuciya ransa a 'bace yace."Allah Khalifa yarinyar nan tayi wasa sai na 'kara aure bana son hauka da da'ki'kanci wallahi kuma zata gane bata da wayo." Khalifa yace."A'a kayi hakuri dai ka cigaba da rarrashinta kasan yarinya ce."Tsaki yaja yace."Allah ya sawa'ke khalifa bazan kuma zuwa gunta sa wata bukata ba taje ra rike kayanta nima na rike nawa zan kuma fara neman aure."
Khalifa yace"Yanzu ka sauka daga kan ra'ayinka kenan."?
Yace."Duk wani abu da zanyi itace ta jawowa kanta ni babu ruwana." Khalifa yace."To Allah ya za'ba abinda yafi alkairi." Ya amsa sa ameen." Lokacin kiran ta ya sake shigowa wayar tashi yana ganin sunanta ya kashe wayar yana jan tsaki.
Cike da takaici da mugun ba'kin ciki ta fito daga d'akin murya na rawa Tace"Hajja bai dauki wayar ba watakila ko baya kusa da wayar ne." Hajja tace"E to hakan na iya kasancewa." Mikewa tayi ta shiga daki tana fad'in "Ku dan jirani na fito."
Uwani dasu Inna Tabawa suka mike Wasila ta jagorace su suka fita Ita Kuluwa zama tayi har sai da Hajja ta fito daga daki ta mi'ka mata karuwar ledar dake hannunta tace"Gashinan turaman atamfofine da mayafai da sabulai sai ku kasafta a tsakaninku." Kuluwa ta kar'be da sauri jikinta na kyarma sai washe bakinta take tana ta zabga godiya, Hajja tace."Babu komai Kuluwa ku gaida gida mungode."
Suna can parking spece Kuluwa takaraso hammatar ta ma'kale da ledar kayan da Hajja ta basu sai murna takeyi tace"To Wasila da Rashida mu mun tafi sai mun sake zuwa ke Wasila idan maigadan nawa ya dawo to ki mi'ka gaisuwata gurinsa tunda dai rowarsa kike mana." Wasila tana daure fuska tace"Zai ji ku gaida gida ku gaishe da Kawu Madu." Suka dinga amsawa da "ameen." Duk suka shiga cikin motar Garba yaja suka fita daga cikin gidan......Wasila da Rashida suka juya jikinsu a sanyaye suka koma ciki To itama Uwanin dai daurewa kawai takeyi amma zuciyarta babu dad'i sam! tana bala'in 'kaunar 'yayanta kamar yanda suke 'kaunarta.
Littafin na kudi ne......!
Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya kema keda Allah Whasap numbar
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*alliya:
'Yr Bngr Sys
*78*
_*Sa'ko na mussaman zuwa gareka Amadu 'kawayen Wasila irin su Mumy Farhan, Bomis Zainab kankara Mrs Aliyu Nafisa Buhari Hauwa Chindo, Sakina Ummee da dai sauransu, sunce kayi hakuri dan Allah karkayiwa Wasila kishiya kayi mata uziri saboda yarinya ce, idan kuma ka kuskura ka 'kara aure to zaka gane baka da wayo dan duk wacce zaka aura ba zata kama 'kafar Wasila ba, zaka dawo inda kake salati kana kiran sunan Allah😅🤭 babu ruwana Sistar Sakina ce tafad'a🕺🕺 sannan Sistar Jamila tace duk wacce zaka aura sunanta salamatu salam dan ba zata iya da jarabarka ba🕺 babu ruwana! Jamila da Ummee ne suka fad'a ni dai 'yar aike ce......Momyna tace kayi auranka dan ba Wasila ce kadai mace ba, takwara Fatima Yakubu ma haka tafad'a Sai sistar Hadiza Shall itama haka tace ka more rayuwarka, Shafa'a S Yari da Bilba sunce kayi aure ka more rayuwarka💃🏼🔥 ni dai na isar da sa'kona Amadu sai ka yanke shawarar da zata fishe ka, nima nace ba Wasila ce kad'ai autar mat.......🙊😌*_
Cikin sanyin jiki suka koma cikin gidan Hajja ta gansu duk babu kuzari a tare dasu tace"Ai kam ni kaina naso su zauna su danyi kwana biyu ku samu sakewa da mahaifiyarku amma ace daga zuwa sai su tafi wallahi banji dadin hakan ba sai kace wad'anda ake kora."
Rashida ta goge hawaye tace"Nima naso su zauna wallahi yanzu anti Wasila yaushe zamuje to." Wasila ta kalleta ranta duk babu dad'i tace."Sai an d'an kwana biyu baby tayi 'kwari zamuje insha Allahu." Hajja tace"Kwarai kuwa hakan yana da kyau, Allah ya kaimu ya bamu lafiya mai amfani." Duk suka amsa da "ameen."