← Book details Yar Bangar Siyasa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 16 OF 108

Sashe 16

Yar Bangar Siyasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

***
Cikin Shiri ya fito daga bedroom dinshi, Garba da Hadi na zaune a katafaran palon nashi suna ganin fitowarshi suka mike a tare gaisuwa suka mika amsa yana mika musu hannu sukayi musabaha da juna Ahamadu bashi da girman kai da d'agawa........Yana mutumta dan adam!! Garba ya isa inda yake yana gyara masa babbar rigarshi da yake yau shigar manya kaya yayi dakarkiyar galila ce a jikinshi green color wuyan babbar rigar anyi masa aiki na manya mutune wanda mafi aka sari masu sarauta keyi, yana gyara links dinshi Garba ya miko mishi hula zanna bukar 'yar gasken ya d'ora saman kanshi a sai ya sake wankuwa da kyau gyaran fuskarshi yayi dai-dai da tsarin askin dake kanshi saisaye yake yi bai fiye tara suma ba amma baya kwal kwabo ana masa saidaye ne agyara masa fuskarsa dai-dai da zamani....Duk wanda ya kalleshi sai ya sake kallo babu wanda zaice ya kai matakin shekurun da yake kai a yanzu.....tare suka futa dasu Garba mutukar ba nisa zaiyi ba baya tafiya da securities su Garba kadai yake dauka su raka shi, Garba ya bude masa bayan mota ya shiga ya zauna Hadi ya zauna kusa dashi ya mayar da murfin motar ya rufe.....Da sauri Garba ya zauna maxaunin direba tun kafin su iso bakin gate din mai gadi ya bude gate din.....Securities din dake zaune a bakin gate suka dinga daga masa hannu da fadin "A sauka lafiya Allah ya tsare a dawo lafiya." Shima hannunsa ya daga musu yana amsawa da "ameen." Har suka futa daga gidan......Sai da suka hau kwalta tukkuna Garba ya tambayi inda suka nufa, ya shaida masa inda zai suje gidan Hajiya Babba dake Zooroad. Garba ya dauki hanya kamar yanda aka umarce shi.
*'YAR BANGAR SIYASA!!*
🌺 romantic love story🌺
*NA:*
*BINTA UMAR ABBALE 🍒*
*🌍Manazarta Writes asso*
_'Kungiyar masu nazari da aiki da Ilimi_
~~~~~~~~
*NA KUDI NE.......!*
_Ga masu bukatar karanta book din zasu tura #300 Vip gruop #600 accont din da za'a tura kudin.0542382124.......Binta Umar gtbank....Idan katin waya mutum zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din....07084653262_08089965176 sai na fad'i yanda za'a biya kud'in.....Mutanan mu na Nijar idan kuna bukatar book din zaku tura dala dari ta wannan numbars.......90899076_88137740 katin airtal ko orange_

*Free Pege17*
Hajiya Babbah na xaune a palonta tare da wasu 'yan mata guda biyu Suhairat da Salimat 'Yayan mutun d'aya ne wato Hajiya Maryam wacce ta kasance 'kanwa ga Hajiya Babbah! kasancewar Allah bai bata haihuwa ba har mijinta ya rasu.mutane ke ta nani'ka mata 'yayansu mussaman 'yan uwanta waccan ta turo 'yarta gobe waccan ma ta turo 'yayanta jibi duk dan ganin daular dake tattare da gidan....Suhairat ce mai nacin zuwa gidan saboda kawai tayi katari da Ahamdu mutumin da ta kwallafa ranta a kanshi take masifar sonsa shi kuma bai san tana yi ba sai tayi zuwa goma gidan ba ganshi ba dan bai fiye zuwa da safe ko da yamma ba sai dare yake zuwa gaisheta, to yau dai sunji dadi jin Hajiya tace sunyiwa waya dashi yace zai shigo da wuri Suhairat ta sake gyara fuskarsa ta fesa turare ta 'kame! a kan mujera Salimat kuwa sai dariya takeyi mata tana fad'in"Allah yasa dai ya kyasa dan na lura kinyi masifar matowa a kan mutumin nan." Suhairat tace"Ke dai bari 'yar uwa ni wallahi da zai aureni da gudu zan yarda ina masifar sonsa komai nashi yana burgeni mutum kamili ga nutsuwa kamshin turaransa ma abin alfahari ne." Salimat ta dinga 'kyalkyala dariya tana tsokanar yar uwar tata......Cikin nutsuwa da kamala ya shigo palon bakinsa dauke da sallama. Dukaninsu suka mike tsaye suna masa barka da zuwa, kamshin turaransa ne ya cika musu hanci Suhairat sai murmushi takeyi tana gyara masa gurin zama....Ya zaune a nutse yana fadin" Suhairat kune yau gidan? ina Hajiyata." Wani fari tayi da ido tace"Wallahi kuwa Mune yau a gidan Hajiya na daki bari na kirata." Ta juya tana tafiya cikin wata iriyar siga.....Oho bai san tanayi ba dan idanunsa na kasan kafet, Tare suka fito da Hajiya babbah tana masa barka da zuwa ya amsa yana tambayar ta gida.....Suhairat ta dauko mishi lemo da ruwa ta tsiyaya masa ta mika mishi.....Ba tare da ya kar'ba yace."Bana jin zansha komai yanzu nagode Suhairat." Jiki a sanyaye ta ajiye cup din ta nemi guri ta zauna kusa da Hajiya......Yace."Ina ta son zuwa Allah bai nufa abubuwa sunyi yawa hajiya a gafarce ni." Tace."Ai babu komai Ahamdu dole ne ayi muku uziri saboda yanayin harkar taku ta jama'a bayan nan kuma nasan akwai hidimomi da yawa Allah dai ya taimaka." Ya amsa da "ameen." Palon yayi shiru Yana so yayi mata maganar dake tafe dashi amma zaman su Suhairat a gurin ya hanashi shi mutum ne mai sirri yafi son komai nashi a cikin tsari dan ya lura da yarinyar kanta rawa yake yasan dai zancen gizo baya wuce na koki ga yanayin yanda take masa kwarkwarsa za tace itama sonsa takeyi.

Gyaran mirya yayi a nutse yace."Hajiya muhimiyar magana ce take tafe dani dan daga nan ma idan na tashi can gidan Kawu Almu zan nufa." Hajiya Babba tace "To babu laifi Ahamadu Allah dai yasa maganar dake tafe da kai irin wacce take bakina ce da nayi mutukar jin dadi." Murmushi ya saki wanda yasa Suhairat shagala gurin kallonsa Yace."Yana da kyau yaran nan su dan bamu guri." Hajiya ta kalli su Suhairat da suka kasa kunne suna so suji maganar ko kunya babu tace."Suhairat ku shiga ciki mana." Simi simi suka mike sam basu so hakan ba mussaman Suhairat tafi so ya fadin maganar a gabanta da jikinta na bata wani abu.

"Hajiya na samu matar aure insha Allahu ranar juma'a ta jibi za'a daura aure." Maganar data fito daga bakinsa kenan.....Fuskarta da yalwataccan murmushi tace"Alhamdullihi Ahamdu baka ta'ba zuwa da labarin da yayi min dadi kamar wannan ba masha Allahu to amma kuma al'amarin baiyi sauri ba kuwa ko bazawara ce ne."? Ya girgiza kai "Budurwace Hajiya." Tace."To to masha Allah amma kuma abun yazo min bagatatan banyi shirin komai ba ko da yake dama haka aure yake dashi da mutuwa ba'a shirya musu in lokaci yayi sai anyi, shin yarinyar 'yar wace unguwa ce kuma." Yace." Yar wata karamar hukama ce a wannan jahar sunan garin nasu Garko amma anan tayi rayuwarta Unguwar dorayi daurin auran dai Can Garko zamuje ayi." Tace."To Ubangiji Allah yasa za'ayi damu ya tabbatar mana da alkairi." Ya amsa da "ameen Hajiyata, ni zan wuce can gidan Kawu Almu babu wani abu da kike bukata ko."? Tace." Alhamdullahi Ahamdu bana bukatar komai ka wadatani da duk abun bukata kafin wani ya kare kasa an kawo wani babu abunda zance sai da nace Allah ya saka maka da alkairi ya jikan iyayenka." Yace."ameen Hajiyata Ubangiji Allah ya barmin ke na dinga ganinki ina jin dadi." Tayi dariya da fadin"Wace ni Ahamdu ai mutuwa rigar kowa ce zan mutu kaima zaka mutu." Ya mike yana kallon a gogon dake daure a hannunsa yace."Duk da haka dai Hajjah ina fatan kiyi rayuwa mai tsayi a duniya tace."To Allah yasa Ahamdu Allah yayi maka albarka ya baka 'yaya masu albarka." ya amsa da ameen yana mata sallama har bakin kofa ta rakoshi tana sanya masa albarka

Suhairat dake la'be bakin kofa ta silale 'kasan daki ta fashe da kuka "Shikkenan na mutu ni suhairat shikkenan karyata ta kare zaiyi aure ina zaune duk na kori masu sona saboda dashi bai san inayi ba na shiga uku na lalace." Kuka take sosai Salimat na bata hakuri Hajjah ta shigo dakin.

Tace"Ke suhairat lafiya kike wannan kukan." Rungumeta tayi tana shashsheka take fada mata tsayin shekarun da tayi tana jiran Ahamdu amma yanzu yazo yace zai auri wata.

Hajjah tace"Inda Ahamdu zai aureki da tuni ya aure ki Suhairat ni da kaina nace ki hakura dashi ki zabi miji cikin manema auranki ki aura kikaji ni ba zanyi masa tilas ba, saboda yaron ya daukeni a matsayin uwa yana min biyayya komai nake so yanayi min ban haihu ba amma an haifar min addua ce tsakanina dashi ni dai shawarar da zan baki shine ki hakura dashi ki fito da miji cikin ma nema auranki ki aura magana ta wuce."

Suhairat ta mike daga jin hajjah tana kuka mayafinta ta figa ta dauki handbang dinta ta fice....Salimat ce kawai tayi wa Hajjah sallama tana bata hakuri kan abunda Suhairat din tayi mata.....Tana fitowa harabar gidan taga Suhairat ta figi mota a guje ta fice daga gidan....Girgiza kai kurrum tayi ta sanya direba ya dauketa domin kaita gida.....' Yan asalin unguwar galadanci ne.

****
Wasila ta tashi da wata iriyar kasala da mutuwar jiki, dan ta jima ma a daki kafin ta fito cikin kayatacciyar kwalliya gold kamar yayi magana a jikinta har yatsun 'kafafunta gold ne tana sanye da legos less dan gasken tayi daurin ture kaga tsiya gashinta ta daure shi da katon ribbon ya kwanta a kafadarta idan ka kalleta sai ka dauka irin masu shegen karatun nan ce saboda yanda takeyin mu'amula cikin jan aji da isa......Uwani da Rashida sai girki suke su sauke su dora suci wannan su sha wannan duniya ta samu.
Chapter 16 · 0% Book details