Sashe 106
Yar Bangar Siyasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yana sane ya'ki kiranta a waya sabida yana so yaga shin zata manta dashi ko a'a bini bini zai duba wayarshi babu text dinta babu kiran wayarta gashi sha biyu na dare har ta wuce........Allah sarki Wasila tana can network ya sakata a gaba tun bayan tafiyar Inna Hajara take ta kiran numbarshi tana 'kin shiga ko kuma data fara ringing sai ta katse har kuka tayi saboda bakin ciki kowa na kwance a daki cikin dare ta fito tsakar gida wai ko dakin ne babu network nan ma tayi tayi kiran baya tafiya, sai ta koma daki ta kwanta lamo tamkar mara lafiya bini bini ta duba wayarta ko zataga test dinshi shuru duk ta rasa abinda ke mata dadi da kyar bacci ya dauketa.
To shima nashi 'bangaran hakane, da kyar bacci ya daukeshi wanda tun yana saka ran ganin test dinta ya cire ya rungume filo kamar wani maraya yana fizgo bacci da karfi, gabadaya gani yay dare yayi mishi tsayi, dan haka uku da rabi nayi ya tashi yaje ya dauro alwala ya hau dadduma yay nafila, kafin ta dauki cazbaha ya wuce masallaci.
Da safe da kyar ta karya duk takaici ya isheta, ga mutane sai shigowa sukeyi wai sunzo gaisheta sai kawai ta koma daki ta kwanta tace da Rashida duk wanda yazo tace musu bacci takeyi.
Haka kuwa Rashida ta dinga sallamarsu, da cewar bacci take wasu masu naci zama sukeyi wai sai ta tashi sun gaisa da ita Wasu kuwa sai suce bari su tafi sa dawo da yamma.
Wasila na ciki tana ta famar kiran wayar tashi wannan karon tana shiga sai dai kuma bai daga ba, nan ma zuciyarta ta sake hasala ta goge hawaye tana mikewa zaune......Sake kiran wayar tayi a karo mara adadi dai-dai lokacin da ya fito daga toilet da alama wanka yay dan ga jikinsa nan duk ruwa, da sauri ya karasa inda wayar take ya dauka, ajiyar zuciya ya sauke ya zauna gefan bed kana ya daga wayar.
Kuka ta fashe dashi harda shashsheka, yaji duk jikinsa yay sanyi gabakidaya a rayuwarsa ya tsani yaji tana kuka....
A tausashe yace."Menene."? Tace"Me yasa ka ki daukar waya zuciyata kamar zata fashe."
Ya sauke ajiyar zuciya yana furzar da wani huci daga bakinsa, yace."Sai kuma kiyi kuka babu sallama da gaisuwa da tambayar yaya na kwana."?
Tace."Duk hankalina ne a tashe wallahi zuciyata sai sa'ke sa'ke take min."
Yace."Ina Mommyna." A hankali tace"Tana can gurin Bitan."
Yace."Kun tafi kun barni da damuwa ko."? Tace."Wallahi nima da kyar nayi bacci ban san haka nake sonka ba sai da na kasa samunka a waya ji nake kamar nayi tsuntsuwa nazo inda kake."
Yaji wani irin dadi na ziyartasa, yace."Nima haka naji na kuma gane kece mahad'in rayuwata." Dariya tayi tace"Nagode mijina, yanzu kayi break fast ko."
Yace."Nakasa komai tunda na tashi kinga ni da kyar ma nayi wanka." Tace."Wayyo babyna da ina nan Wallahi ni zanyi maka wanka in rungumeka in shafa maka mai in saka maka kaya."
Yayi wani killer smile kafin yace."Tunda ni baby ne idan kinyi min wanka kin shafa min mai kuma kin sa min kaya sai ki bani nono nasha ko."
Ta saki dariya da shashsheka tace"Allah da ina kusa zan baka kasha."
Yaji tsigar jikinsa ta tashi Yace."Mu bar wannan maganar kada kisa nazo inda kike yanzu."
Ta 'kyal'kyale masa da dariya tace"Ai dama kaina ka fara maganar." Yace."Tom na daina maganar." ya cigaba da cewa yau zan tafi katsina amma kuma komai dare zan dawo insha Allah." Tace"Wayyo Habibi Katsina me zakaje kayi."? Yace."Zanje Gurin abokina mana mutumin da yazo dubaki lokutan da baki da lafiya."
Jiki a sanyaye tace"To Allah ya tsare min kai ya dawo da kai lafiya." Ya amsa da "ameen." Yace."Kinga yanzu na dan samu sassauci zan iya cin abinci sabida kin bani kulawa duk da bakya gabana naji dadi sosai Allah yay miki albarka."
A nutse tace"Ameen." Bari na bari ka nutsu kayi break sai na sake kiranka ko."
Yace."Okey my Princess! Murmushi tayi ta kashe wayar tana fad'in "Nazama gimbiya kenan.....Cike da nishadi ta fito tsakar gidan gidan malam ta cigaba da hada hada da jama'a masu shigowa.
Gangami!! da turnu'kun!! haya'ki!!! nake hangowa kan titin zuwa gidan gomnati wato government house, mutane sunfi dari biyu sun kashe titi sai 'kone -'kone sukeyi suna tada 'kura gami da 'kona tayoyi suna watsa fetur suna 'kyasta ashana, sai ihu sukeyi suna buga ganguna, guri ya hargitse da hayaniya gami da haya'kin! wuta, dan wasu ma har sun soma galabaita duk da sune suka saka kansu abunda sukeyi din basu sare ba so sukeyi su shiga cikin government house din domin su cimma manufarsu kan mai girma governor Lawan Rabo, mafi akasarin jama'ar da suka tada wannan tarzomar iri-iren wad'anda aka rusawa gidaje ne da masana'antu gurun aikin titin jirgin 'kasa wanda ko rabin aikin ba'ayi ba an dakata gashi su kuma anyi musu al'kawari za'a biya su diya shuru kakeji malam yaci shirwa kullum 'karya daban ta gobe daban sam basa gajiya da shiga gidan redio suyi karya, sukuwa suka ga rainin hankalin yay yawa kawai suka yanke wannan hukuncin duk da sun san wannan abun da sukeyi din xai iya barazana ga rayuwar wasu daga cikin amma dai duk da haka sukaji suka gani domin suna so su kwaci hakkinsu da'aka danne musu,
Mai girma governor Lawan Rabo hankalinsa yay masifar tashi sosai ya lura Jama'ar Jahar kano suna so su ga karshen sa dan duk abinda ke faruwa a kan titin yana gani ta cikin CCTV Dan haka sai kawai ya umarci Securities kan suje suyi aman wuta da alburusai a gurun wanda kwanansa ya 'kare shi ya jawo kansa.
Ba tare da 'bata lokaci ba kuwa, Police din gidan gomnatin suka shiga motocinsu suka durfafi kan titin suna sakin harbi ko ta ina!
Littafin na kudi ne.....!
Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah! Whasap numbar
07084653262
*BINTA UMAR ABBALE*alliya:
*'YAR BANGAR SIYASA!!*
*END🔚*
*ALHAMDULILLAHI*
*85*
Gurin ne ya sake hargitsewa da hayaniya dalilin zuwan Securities din, kafin kice kwabo jama'ar da sukayi dafifi a kan titin sun soma gudu saboda gabakidaya harbin bindigar da Police din keyi yayi masifar razanasu, sai kowa ya soma kokarin ceton ransa, amma dai duk da haka sai da harbin ya samu wasu daga cikinsu suna kwance a gurin suna ihu jini tamkar yay magana kan titin yayi kaca kaca sai hayaki ne yake tashi a gurin gashi gari ya soma duhu magariba ta gabato.....Governor na ganin abinda ke faruwa ya kira d'aya daga cikin mutanan da ya tura yace."Maza a kwashi wa'inda suka jikkata akai su asibiti, Allah sarki mutum kusan bakwai sun mutu 'yan uwansu sai kuka suke suna d'ora hannu aka hade da tsinewa Lawan Rabo albarka suna tur da wannan mulki nashi....Amadu na katsina tare da Abokinshi Alh Muktari labari ya samesu dan sai da suka ga abinda ke faruwa a labarai, hankali a tashe sukayi sallama da abokinshi ya dauko hanyar dawowa gida.....Koda ya iso bai nufi gida ba kai tsaye gidan redio na *Salama* ya umarci Garba ya saukeshi, abinda bai ta'ba faruwa ba kenan wai ya shiga gidan redio dan ya yad'a manufarshi,
Tashar redion Salama taji dad'i sosai da zuwanshi, kafin kice me sun fara sanarwa yanzu yanzu d'an takarar governor kano mai girma *Amadu Musa* zaiyi magana dangane da abubuwan dake faruwa a wannan jahar.
Jama'a duk suka maida hankalinsu gurin sauraran jawabinsa.....Ya fara da bisimillah had'e da addua kamar yanda annabi ya koya mana kana yace."
*Hak'ika banji dad'in wannan abunda ya faru ba a yau! hankalina ya tashi matuka! ganin yanda jama'a suka jikkata wasu har suka rasa ransu, Duk abinda wannan gomnati tayi muku bai kamata ku dauki irin wannan mataki ba, don yin hakan ba zai amfanar daku komai ba sai 'bacin rai gami da nadama da dana sani, na tabbata yau wasu daga cikinku suna nan cikin bakin ciki da damuwa rashin Iyaye da 'yan uwa mata na gida suna kuka saboda wannan tashin hankalin Wata mijinta ya mutu wata mijinta ya 'kone ko ya karya, duk saboda wannan hatsaniyar data afku, wannan abun da jama'ar wannan jaha sukayi bai dace ba shi wanda kukeyi dominsa din baza ku ganshi ba ballanta ku cimma burinku akansa, duk abinda hakuri bai baku ba rashin sa ba zai baku ba, kuyi hakuri ku barshi da Allah bisa ga zalintarku da yayi sannan kuma cigaba da yi mana addua kan Allah ya cika mana burinmu a cikin wannan tafiya, mutukar Ubangiji Allah ya dam'ka min mulki wannan jahar zan share muku hawaye zakuyi mamaki sannan dukanin wanda yay asarar gidanshi ko masana'antar sa wannan gomnatin insha Allahu Ni Amadu! na kar'bi wannan mulki nayi muku alkawarin biyanku hakkinku, wannan titin kuma da suka d'auko gadan! gadan! sunayi ni dama nasan ba iyawa zasuyi ba ku zuba musu ido, mu idan muzo namu salon daban yake da nasu, babu wani abu nasu da suka bari wanda zamu d'ora aikinmu akai komai sabo zamu 'kir'kira! babu algus babu almundahana a ciki, zamuyi mulki bisa amana da tsoron Allah Insha Allah! Daga karshe nake muku fatan alkairi al'ummar wannan jaha mai albarka ku cigaba da addua kan Allah ya kawo mana sauyi mafi alkairi sannan kuma na umarce ku da kada ku kara tada wata tarzoma, saboda yin hakan bashi ne mafita ba, mafita shine ku bamu had'in kai aranar za'be! kowa ya fito ya za'bi Jam'iyyar mu mai albarka tun daga sama har 'kasa, ku za'bi Jam'iyyar CPC Sa'a! Wasalamu alaikum."*
To shima nashi 'bangaran hakane, da kyar bacci ya daukeshi wanda tun yana saka ran ganin test dinta ya cire ya rungume filo kamar wani maraya yana fizgo bacci da karfi, gabadaya gani yay dare yayi mishi tsayi, dan haka uku da rabi nayi ya tashi yaje ya dauro alwala ya hau dadduma yay nafila, kafin ta dauki cazbaha ya wuce masallaci.
Da safe da kyar ta karya duk takaici ya isheta, ga mutane sai shigowa sukeyi wai sunzo gaisheta sai kawai ta koma daki ta kwanta tace da Rashida duk wanda yazo tace musu bacci takeyi.
Haka kuwa Rashida ta dinga sallamarsu, da cewar bacci take wasu masu naci zama sukeyi wai sai ta tashi sun gaisa da ita Wasu kuwa sai suce bari su tafi sa dawo da yamma.
Wasila na ciki tana ta famar kiran wayar tashi wannan karon tana shiga sai dai kuma bai daga ba, nan ma zuciyarta ta sake hasala ta goge hawaye tana mikewa zaune......Sake kiran wayar tayi a karo mara adadi dai-dai lokacin da ya fito daga toilet da alama wanka yay dan ga jikinsa nan duk ruwa, da sauri ya karasa inda wayar take ya dauka, ajiyar zuciya ya sauke ya zauna gefan bed kana ya daga wayar.
Kuka ta fashe dashi harda shashsheka, yaji duk jikinsa yay sanyi gabakidaya a rayuwarsa ya tsani yaji tana kuka....
A tausashe yace."Menene."? Tace"Me yasa ka ki daukar waya zuciyata kamar zata fashe."
Ya sauke ajiyar zuciya yana furzar da wani huci daga bakinsa, yace."Sai kuma kiyi kuka babu sallama da gaisuwa da tambayar yaya na kwana."?
Tace."Duk hankalina ne a tashe wallahi zuciyata sai sa'ke sa'ke take min."
Yace."Ina Mommyna." A hankali tace"Tana can gurin Bitan."
Yace."Kun tafi kun barni da damuwa ko."? Tace."Wallahi nima da kyar nayi bacci ban san haka nake sonka ba sai da na kasa samunka a waya ji nake kamar nayi tsuntsuwa nazo inda kake."
Yaji wani irin dadi na ziyartasa, yace."Nima haka naji na kuma gane kece mahad'in rayuwata." Dariya tayi tace"Nagode mijina, yanzu kayi break fast ko."
Yace."Nakasa komai tunda na tashi kinga ni da kyar ma nayi wanka." Tace."Wayyo babyna da ina nan Wallahi ni zanyi maka wanka in rungumeka in shafa maka mai in saka maka kaya."
Yayi wani killer smile kafin yace."Tunda ni baby ne idan kinyi min wanka kin shafa min mai kuma kin sa min kaya sai ki bani nono nasha ko."
Ta saki dariya da shashsheka tace"Allah da ina kusa zan baka kasha."
Yaji tsigar jikinsa ta tashi Yace."Mu bar wannan maganar kada kisa nazo inda kike yanzu."
Ta 'kyal'kyale masa da dariya tace"Ai dama kaina ka fara maganar." Yace."Tom na daina maganar." ya cigaba da cewa yau zan tafi katsina amma kuma komai dare zan dawo insha Allah." Tace"Wayyo Habibi Katsina me zakaje kayi."? Yace."Zanje Gurin abokina mana mutumin da yazo dubaki lokutan da baki da lafiya."
Jiki a sanyaye tace"To Allah ya tsare min kai ya dawo da kai lafiya." Ya amsa da "ameen." Yace."Kinga yanzu na dan samu sassauci zan iya cin abinci sabida kin bani kulawa duk da bakya gabana naji dadi sosai Allah yay miki albarka."
A nutse tace"Ameen." Bari na bari ka nutsu kayi break sai na sake kiranka ko."
Yace."Okey my Princess! Murmushi tayi ta kashe wayar tana fad'in "Nazama gimbiya kenan.....Cike da nishadi ta fito tsakar gidan gidan malam ta cigaba da hada hada da jama'a masu shigowa.
Gangami!! da turnu'kun!! haya'ki!!! nake hangowa kan titin zuwa gidan gomnati wato government house, mutane sunfi dari biyu sun kashe titi sai 'kone -'kone sukeyi suna tada 'kura gami da 'kona tayoyi suna watsa fetur suna 'kyasta ashana, sai ihu sukeyi suna buga ganguna, guri ya hargitse da hayaniya gami da haya'kin! wuta, dan wasu ma har sun soma galabaita duk da sune suka saka kansu abunda sukeyi din basu sare ba so sukeyi su shiga cikin government house din domin su cimma manufarsu kan mai girma governor Lawan Rabo, mafi akasarin jama'ar da suka tada wannan tarzomar iri-iren wad'anda aka rusawa gidaje ne da masana'antu gurun aikin titin jirgin 'kasa wanda ko rabin aikin ba'ayi ba an dakata gashi su kuma anyi musu al'kawari za'a biya su diya shuru kakeji malam yaci shirwa kullum 'karya daban ta gobe daban sam basa gajiya da shiga gidan redio suyi karya, sukuwa suka ga rainin hankalin yay yawa kawai suka yanke wannan hukuncin duk da sun san wannan abun da sukeyi din xai iya barazana ga rayuwar wasu daga cikin amma dai duk da haka sukaji suka gani domin suna so su kwaci hakkinsu da'aka danne musu,
Mai girma governor Lawan Rabo hankalinsa yay masifar tashi sosai ya lura Jama'ar Jahar kano suna so su ga karshen sa dan duk abinda ke faruwa a kan titin yana gani ta cikin CCTV Dan haka sai kawai ya umarci Securities kan suje suyi aman wuta da alburusai a gurun wanda kwanansa ya 'kare shi ya jawo kansa.
Ba tare da 'bata lokaci ba kuwa, Police din gidan gomnatin suka shiga motocinsu suka durfafi kan titin suna sakin harbi ko ta ina!
Littafin na kudi ne.....!
Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah! Whasap numbar
07084653262
*BINTA UMAR ABBALE*alliya:
*'YAR BANGAR SIYASA!!*
*END🔚*
*ALHAMDULILLAHI*
*85*
Gurin ne ya sake hargitsewa da hayaniya dalilin zuwan Securities din, kafin kice kwabo jama'ar da sukayi dafifi a kan titin sun soma gudu saboda gabakidaya harbin bindigar da Police din keyi yayi masifar razanasu, sai kowa ya soma kokarin ceton ransa, amma dai duk da haka sai da harbin ya samu wasu daga cikinsu suna kwance a gurin suna ihu jini tamkar yay magana kan titin yayi kaca kaca sai hayaki ne yake tashi a gurin gashi gari ya soma duhu magariba ta gabato.....Governor na ganin abinda ke faruwa ya kira d'aya daga cikin mutanan da ya tura yace."Maza a kwashi wa'inda suka jikkata akai su asibiti, Allah sarki mutum kusan bakwai sun mutu 'yan uwansu sai kuka suke suna d'ora hannu aka hade da tsinewa Lawan Rabo albarka suna tur da wannan mulki nashi....Amadu na katsina tare da Abokinshi Alh Muktari labari ya samesu dan sai da suka ga abinda ke faruwa a labarai, hankali a tashe sukayi sallama da abokinshi ya dauko hanyar dawowa gida.....Koda ya iso bai nufi gida ba kai tsaye gidan redio na *Salama* ya umarci Garba ya saukeshi, abinda bai ta'ba faruwa ba kenan wai ya shiga gidan redio dan ya yad'a manufarshi,
Tashar redion Salama taji dad'i sosai da zuwanshi, kafin kice me sun fara sanarwa yanzu yanzu d'an takarar governor kano mai girma *Amadu Musa* zaiyi magana dangane da abubuwan dake faruwa a wannan jahar.
Jama'a duk suka maida hankalinsu gurin sauraran jawabinsa.....Ya fara da bisimillah had'e da addua kamar yanda annabi ya koya mana kana yace."
*Hak'ika banji dad'in wannan abunda ya faru ba a yau! hankalina ya tashi matuka! ganin yanda jama'a suka jikkata wasu har suka rasa ransu, Duk abinda wannan gomnati tayi muku bai kamata ku dauki irin wannan mataki ba, don yin hakan ba zai amfanar daku komai ba sai 'bacin rai gami da nadama da dana sani, na tabbata yau wasu daga cikinku suna nan cikin bakin ciki da damuwa rashin Iyaye da 'yan uwa mata na gida suna kuka saboda wannan tashin hankalin Wata mijinta ya mutu wata mijinta ya 'kone ko ya karya, duk saboda wannan hatsaniyar data afku, wannan abun da jama'ar wannan jaha sukayi bai dace ba shi wanda kukeyi dominsa din baza ku ganshi ba ballanta ku cimma burinku akansa, duk abinda hakuri bai baku ba rashin sa ba zai baku ba, kuyi hakuri ku barshi da Allah bisa ga zalintarku da yayi sannan kuma cigaba da yi mana addua kan Allah ya cika mana burinmu a cikin wannan tafiya, mutukar Ubangiji Allah ya dam'ka min mulki wannan jahar zan share muku hawaye zakuyi mamaki sannan dukanin wanda yay asarar gidanshi ko masana'antar sa wannan gomnatin insha Allahu Ni Amadu! na kar'bi wannan mulki nayi muku alkawarin biyanku hakkinku, wannan titin kuma da suka d'auko gadan! gadan! sunayi ni dama nasan ba iyawa zasuyi ba ku zuba musu ido, mu idan muzo namu salon daban yake da nasu, babu wani abu nasu da suka bari wanda zamu d'ora aikinmu akai komai sabo zamu 'kir'kira! babu algus babu almundahana a ciki, zamuyi mulki bisa amana da tsoron Allah Insha Allah! Daga karshe nake muku fatan alkairi al'ummar wannan jaha mai albarka ku cigaba da addua kan Allah ya kawo mana sauyi mafi alkairi sannan kuma na umarce ku da kada ku kara tada wata tarzoma, saboda yin hakan bashi ne mafita ba, mafita shine ku bamu had'in kai aranar za'be! kowa ya fito ya za'bi Jam'iyyar mu mai albarka tun daga sama har 'kasa, ku za'bi Jam'iyyar CPC Sa'a! Wasalamu alaikum."*