Sashe 72
Yar Bangar Siyasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tana fita dalleliyar motarshi ta karyo kwana zata shigo cikin layin......Yara yaran dake wasa a bakin hanya suka watse suna ihu da bin motar da kallo, Rashida na tsaye a bakin kofar gidan motar tayi parking a wani fili dake gefen gidan.....Wucewa take kokarin yi yay gaggawar bud'e motar ya fito gabanshi na wani irin fad'uwa, babu abinda yake fad'i cikin zuciyarshi sai alhamdullihi."!!! Rashida tayi saurin dafe kirjinta tana kallonshi Sai kuma ta washe baki wanda kana ganinta kasan tana cikin farin ciki.......Garba ne ya bud'ewa Hajja mota ta fito tana mita da fad'in " Zaman mota ai sai ya saka ciwo tafiya ba tafiya ba 'kafafuna duk sunyi tsami.'' Hannunta ya d'an ri'ke kana ta gyara sa takalminta da lullubin mayafin ta da ya sauka kafadarta........Rashida ta karaso gurin cike da nauyi da jin kunya take musu barka da zuwa! Ya dinga amsawa da sakakkiyar fuska kamar bashi ba sai wani dariya yake yana godewa Allah lallai Khalifa Waliyi ne ashe dai da gaske a maganarshi , ya tabbata tunda yaga 'yar uwarta itama tana ciki........Ya kalleta a nutse yace."Ina fata mai allo na nan." Tace."Eh yana nan yau bai fita da wuri ba ya tsaya yiwa anti Wasila rubuta." Da jin maganarta sai yaji tamkar an tsiyaya mishi ruwan sanyi mai madara a ranshi yaji duk wani kunci da tashin hankalinsa ya kau! sai ya dinga zumud'in shiga gidan, yana fad'in "To kije ki shaida mishi cewar mune muke tafe." Da sauri Rashida ta nufi cikin gidan cikin murna da farin ciki sai kace wacce akace ga mahaifinta ya dawo duniya......... Lokacin da shiga gidan Wasila ta tashi hakanan Bitan ma tana kicin tana gyara tukunya, ta zube a gabanshi da walwala a fuskarta tace"Kawu ga Alhaji Ahamdu mijin anti Wasila nan shida mahaifiyarshi yace a sanar maka da zuwansu." Mai allo ya jinge allon dake hannunshi yana kallonta Yace."To Masha Allah sune suke tafe cikin wannan ranar? maza karkade tabarmar nan ki gyara musu guri bari na shigo dasu Allah yasa ma ban fita ba da munyi sa'bani." Rashida ta shiga karkad"e tabarma tana sake share gurin da marmatsar da abubuwan dake kan hanya.....Mai allo ya sanya takalmansa a nutse ya fita daga gidan.........Tana 'kokarin fitowa daga band'akin ne hancinta ya sha'ko mata masifaffen 'kamshin turaransa da ba zata ta'ba mancewa dashi ba......Gabanta ya yanke ya fad'i lokacin da ta tsinkayi muryarshi yana sallama a gidan ta kuma tsinkayi muryar mai allo yana fad'in "Sannunku da zuwa Alhaji sannu kun d'auko rana Hajiya sannu da hanya, ku shigo ciki......'Kyauran band'akin ta ri'ke gam! jikinta na kyarma! ta dinga fad'in innalilihi wa'ina ilaihi raji'un! me ya kawo shi? me yazo yayi mana? me yake nema kuma? babu wanda zai bata amsa, ta cigaba da rike kyaure tana rawar jiki tana kuma juyo muryoyinsu a lokacin da suke gaisawa da juna. Jikinta ta duba daga ita sai zanin atamfa dan da zafi ya isheta bayan fitar rashida ruwa ta cika a bokiti taje ta kwara a jikinta wai ko ta samu sassauci babu abinda ke jikinta sai zanin atamfar da dankwalinshi, kamar za tayi kuka yanzu ni ya zanyi na fito ga mutane gashi ba suttura a jikina? tunanin da take kenan ta juyo muryar Mai allo na fad'in " Rashida shiga ki kira 'yar uwarki mana ni kaina a 'kasa ina rubutu ban san sanda ta tashi daga gurin nan da tana kwance a gurin nan da kake zaune." Yafad'a yana nuna masa inda yake zaune, sai ya shiga bin gurin da kallo kamar zai ganta a gurin......Rashida ta duba dakin bata ciki, Bitan dake kokarin fitowa daga d'aki tace"Ai inajin tana band'aki wanka take kasan dama yini take watsa ruwa bata son zafi ai." Mai allo yace."To to koda naji." Ahmadu kuwa jin abinda Bitan tace sai kawai ya shiga rarraba idanunsa a cikin gidan yana laluben ta ina zata fito......Aikuwa sai yaji motsin 'kyaure a wani 'bangare da sauri ya mai da idanunshi gurin......Ta fito a hankali kamar wacce 'kwai ya fashewa a ciki take tafiya, zanin jikinta ya d'angale saboda daurin kirji da tayi sai tayi amfani da dankwalin gurin kare kirjinta da fuskarta.......Gogon ya wani susuce a gurin ya dinga kallonta tin daga kafafunta har zuwa kanta, jikinsa yay wani bala'in sanyi lokacin da ya hango tudun cikinsa dake jikinta, rintse idonsa yayi yana tasbihi ga Allah ya sauke wata gawurtacciyar ajiyar zuciya, Ya bud'e idanunsa da sauri a dai-dai lokacin da take 'kokarin shiga d'akinsu santsin takalmin dake kafarta ya kusa kayar da ita, tayi axamar rike kyauran d'akin tana salati zubewa tayi bakin kofar lokaci guda zanin jikinta ya kusa sa'bulewa dankwalin da ta rufe kanta da kirjinta tuni yayi nashi guri, wani irin 'kullewa marar tayi tana murd'a mata.........kawai ganinsa tayi tsaye a kanta ya wani gigice yana sa'be babbar riga dama manyan kaya ya saka tunda duk sanda zaije gurin mai allo baya zuwa da tazarce na shadda ko yadi riga da wando da malin malin yake sanya........Shine yay bake bake a gurin yana fad'in "Subahanallahi! Kafin ta juyo miryar Bitan na fad'in " Haba Wasila sai da fa na hanaki saka takalmin nan saboda santsin sa sau nawa yana kokarin kayar dake dan dai kawai Allah na kiyayewa ne, kinga ni dai yau ga abinda ya ja miki." Bitan ta 'karashe maganar tana kokarin mikar da ita! Rintse idonta tayi tana fad'in "Wayyo cikina mara ta ciwo Bitan Ya Allah."!!!! Da sauri yay nufi shiga dakin zufa na karyo mishi Hajjah ta dakatar dashi tana hararshi, ita ta shiga dakin suka kama Wasilan suka janye ta daga bakin kofa! Shi kuma ya cire hularshi yana fifita da ita! Wannan wane irin tsautsayi ne? daga zuwanshi yana murna Allah dai ka taimake ni."! Abinda yake fad'a kenan ya koma ya zauna yana cigaba da fifita da hularshi fargaba duk ta cika masa zuciya......Mai allo ya kalleshi cikin naxari sai kawai ya girgiza kanshi yana murmushi a cikin zuciyarshi ya cigaba da d'auraye rubutun dake jikin allon hannunshi, Yace." Tuntuni naji Bitan nayi mata magana kan ta daina saka takalmin nan saboda rashin ji ta'ki dainawa, gashi yana so ya cutar da ita, tunda abin ya kasance da haka da kaina zan dauke takalman na fita dashi.''
Ya aje hular dake hannunshi a gefe yana fuskantar mai allon sosai, Yace."Shine babban damuwar dama, akwai kuruciya da rashin sanin ciwon kai a tare da ita shiyasa take aikata komai yanzu daba dan Allah ya takaita ba da mummunar faduwa za tayi." Mai allo yace."Allah dai ya kikeye." Mikewa yay hannunshi rike da rubutun ya nufi dakin......Binsa yay da kallo yana ji kamar yabi bayanshi sai dai kallon da Hajjah tayi mishi a d'azu yake tunawa.
Mai allo ya tsaya bakin 'kofar dakin yana mikawa Bitan rubutun hannunshi da fad'in "Bata tasha kana kuma ki shafe mata jikinta dashi, za taji sassauci rashin jin magana ne irin na mutan yau, takalma zan daukesu yanzu in fita dasu idan ya kasance ta shiga bandakin babu takalmi sai ta shiga haka ai lalurace tunda shi takalmin na baraxana da lafiyarta" Hajjah babah tace"Kwarai kuwa malam ka kwashe takalman a fita dasu tunda suna neman cutar da ita kuma mutukar tana ganinsu to ba zata daina sakawa ba."
Mai allo ya sunkuya bakin kofar ya kwashe sabbin takalman 'yan madina ya samu leda ya zuba a ciki ya daure ya rataye jikin wata kusa dake bangon gidan yana fad'in "Anjima idan zan fita zan fita dasu in bawa yara sayi amfani dashi."
Yana zaune yana kallon mai allon duk ya rasa abinda ke damunshi hankalinshi na cikin dakin burinshi ya sake tozali da ita da cikin jikinta, jikinsa ne yay sanyi ganin babu wata sakewa irin tada a tare da mai allon yasan dai sun gaisa cikin girma da mutunci amma duk wannan rawar jikin da mai allon keyi masa ya daina magana ma ba sosai sukeyi ba......Hajjah babbah da Bitan suka fito daga dakin, Hajja na fad'in "Ciki fari dama ai kyaga wauta iri iri Allah dai ya rabasu lafiya.'' Duk suka amsa da " ameen." Har dashi gogan da yabi ya zubawa hajja ido yana so yayi magana sai dai yayi shiru ya sunkuyar da kanshi 'kasa, tunda khalifa baya gurin to yanzu hajja itace garkuwa a gurinshi amma shi kanshi yanzu ya gane ya tafka babban kuskure sosai mugun kunyar mai allon ne ma ya rufeshi yanzu da wane ido xai kalleshi yayi mishi bayani dangane da abinda yake tafe dashi.
Hajjah ta gyara zamanta a nutse tace"Malam gurinka nazo domin magana mai muhimanci nake tafe da ita.'' mai allo ya gyara zamanshi yana kallonta a nutse yace."Hajiya ina sauraranki." Hajja tace"Malam da farko dai ina me baka hakuri a bisa abinda ya faru, nasan dole rayukan ku su 'baci saboda duk mutumin da akece an saki d'anshi dole ne ranshi ya 'baci mussaman idan anyi bunkice an duba anga babu 'kwakkwaran dalilin da ya sanya aka aikata sakin kamar dai yanda al'amarin nan faru, yarinyar nan wasila an saketa ba tare da wani dalili me karfi ba, tabbas an shiga hakkinta mutuka!! kuma irin wannan sakin shine ubangji baya so.....To amma nasan dai kai mai ilimi ne kuma kasan kaddara dai- dai gwargwado kasan cewar duk abinda Allah ya kaddara sai ya faru a kan bawanshi to sai ya faru, saboda haka ina so dukaninmu mu dauki wannan abun a matsayin kaddara wacce ta riga fata......Kuma hakika naji dad'i sosai da ya kasance cewa sakin an aikata irin wanda musulunci yake so, akwai sauran dama a halin yanzu, dan haka muke ro'ko ayi hakuri yarinyar nan ta koma d'akinta."
Ya aje hular dake hannunshi a gefe yana fuskantar mai allon sosai, Yace."Shine babban damuwar dama, akwai kuruciya da rashin sanin ciwon kai a tare da ita shiyasa take aikata komai yanzu daba dan Allah ya takaita ba da mummunar faduwa za tayi." Mai allo yace."Allah dai ya kikeye." Mikewa yay hannunshi rike da rubutun ya nufi dakin......Binsa yay da kallo yana ji kamar yabi bayanshi sai dai kallon da Hajjah tayi mishi a d'azu yake tunawa.
Mai allo ya tsaya bakin 'kofar dakin yana mikawa Bitan rubutun hannunshi da fad'in "Bata tasha kana kuma ki shafe mata jikinta dashi, za taji sassauci rashin jin magana ne irin na mutan yau, takalma zan daukesu yanzu in fita dasu idan ya kasance ta shiga bandakin babu takalmi sai ta shiga haka ai lalurace tunda shi takalmin na baraxana da lafiyarta" Hajjah babah tace"Kwarai kuwa malam ka kwashe takalman a fita dasu tunda suna neman cutar da ita kuma mutukar tana ganinsu to ba zata daina sakawa ba."
Mai allo ya sunkuya bakin kofar ya kwashe sabbin takalman 'yan madina ya samu leda ya zuba a ciki ya daure ya rataye jikin wata kusa dake bangon gidan yana fad'in "Anjima idan zan fita zan fita dasu in bawa yara sayi amfani dashi."
Yana zaune yana kallon mai allon duk ya rasa abinda ke damunshi hankalinshi na cikin dakin burinshi ya sake tozali da ita da cikin jikinta, jikinsa ne yay sanyi ganin babu wata sakewa irin tada a tare da mai allon yasan dai sun gaisa cikin girma da mutunci amma duk wannan rawar jikin da mai allon keyi masa ya daina magana ma ba sosai sukeyi ba......Hajjah babbah da Bitan suka fito daga dakin, Hajja na fad'in "Ciki fari dama ai kyaga wauta iri iri Allah dai ya rabasu lafiya.'' Duk suka amsa da " ameen." Har dashi gogan da yabi ya zubawa hajja ido yana so yayi magana sai dai yayi shiru ya sunkuyar da kanshi 'kasa, tunda khalifa baya gurin to yanzu hajja itace garkuwa a gurinshi amma shi kanshi yanzu ya gane ya tafka babban kuskure sosai mugun kunyar mai allon ne ma ya rufeshi yanzu da wane ido xai kalleshi yayi mishi bayani dangane da abinda yake tafe dashi.
Hajjah ta gyara zamanta a nutse tace"Malam gurinka nazo domin magana mai muhimanci nake tafe da ita.'' mai allo ya gyara zamanshi yana kallonta a nutse yace."Hajiya ina sauraranki." Hajja tace"Malam da farko dai ina me baka hakuri a bisa abinda ya faru, nasan dole rayukan ku su 'baci saboda duk mutumin da akece an saki d'anshi dole ne ranshi ya 'baci mussaman idan anyi bunkice an duba anga babu 'kwakkwaran dalilin da ya sanya aka aikata sakin kamar dai yanda al'amarin nan faru, yarinyar nan wasila an saketa ba tare da wani dalili me karfi ba, tabbas an shiga hakkinta mutuka!! kuma irin wannan sakin shine ubangji baya so.....To amma nasan dai kai mai ilimi ne kuma kasan kaddara dai- dai gwargwado kasan cewar duk abinda Allah ya kaddara sai ya faru a kan bawanshi to sai ya faru, saboda haka ina so dukaninmu mu dauki wannan abun a matsayin kaddara wacce ta riga fata......Kuma hakika naji dad'i sosai da ya kasance cewa sakin an aikata irin wanda musulunci yake so, akwai sauran dama a halin yanzu, dan haka muke ro'ko ayi hakuri yarinyar nan ta koma d'akinta."