Sashe 67
Yar Bangar Siyasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Littafin na kudi ne.....!
Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah Whasap numbar
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
[14/08, 12:04 pm] Farida Books: 'Yr Bngr Sys
*58*
Cike da farin ciki da walwala ya shiga gidan nashi yana kwalawa matarshi kira..........Kuluwa ta fito daga wani guri wanda alamu suka nuna cewar madafi ne (khicin) hannunta da wata katuwar mara da alama kwasar towo take, tace"Malam ganin nan Allah yasa lafiya irin wannan kira hak.....Kafin ta rufe bakinta sai idanunta ya sauka kansu Uwani da 'yayanta, lokacin 'kan'kani ta kirne fuska tana fad'in "A'a yau kuma Uwani ce a garin."? Uwani dasu Wasila duk sunga sauyin fuska a tare da ita, lokacin da take maganar da alama dai batayi maraba da zuwan su garin ba.......Kawu Madu yana washe hakoransa yace." Wallahi kau nima nayi mamaki sosai dan baki ji dadin da nakeji ba, abinci zamuci dasu malam tsalha na taso domun in shigo dasu gidan." Kuluwa tace"To sannunku da zuwa ku shigo ciki." Kawu Madu yace."Uwani ku shiga ciki a baku abinci ku huta ai da alama ma kun kwaso rana." Uwani tace"Aikuwa wallahi munsha zaman mota da gajiya." Kawu Madu ya juya ya fita yana fad'in "Bari nasa Ayuba yaje can cikin kasuwa ya siyo muku ruwan sanyi."
Uwani da Rashida suka shiga daukan jakkunansu dake yashe a tsakar gidan suka nufi dakin Kuluwa, suna shiga katuwar rumfa ce sai dai babu shinfida a cikinta sai guntattakin tabarmi da ledoji ko ina kaca kaci da kwari ka 'kananin kyankyasai ga wani uban 'kuda da yake tashi a rumfar da wani kafirin zarnin fitsarin yara......Tun lokacin da suka shiga rumfar Wasila ke yatsine ya tsinen fuska zuciya sai masifar tashi takeyi aikuwa kafin tayi wani yun'kuri amai ya kece mata! a guje! tayi waje ta nemi bakin rariya ta tsuguna ta dinga kelayashi tana kwallah......Rashida ce tsaye a kanta tana mata sannu duk ta shiga damuwa. Bayan ta gama aman ta bata ruwa ta wanke bakinta da fuskarta kana ta mike jiri na d'ibarta......Rashida ta rike hannunta wai su koma cikin d'akin girgiza kanta tayi da kyar tace"Rashida rabu dani don Allah zuciya tashi takeyi idan na koma gurin nan zan iya yin wani aman." Aikuwa karaf a kunnan Kuluwa ta rike baki tana fad'in "Ke ja'ira yarinyar me kike nufi? daga zuwa zaki fara yiwa mutane sanabe da iyayi kina nufin kazama ce ni kome." Rashida tayi saurin girgiza kanta tana fad'in "Ba haka take nufi ba baba." Kuluwa tace"To me take nufi da har zata shiga dakina ta rugu waje da gudu tana kwara amai." Rashida tace "bata da lafiya ne dama tun a mota cikin ta ke ciwo." Kuluwa ta girgiza kanta tana fad'in "Maji ma gani dai idan tusa zata hura wuta, kome kuke tafe dashi dai-dai nake daku to kaji."! Tana gama maganar ta ta shige madafi domin cigaba da aikinta.
Uwani na cikin dakin abin duniya yayi mata yawa, tunani takeyi yanzu wace irin rayuwa zasuyi cikin gidanan! tun da can baya tasan Kuluwa macace mara mutunci da muguwar kaxanta sam bata so kowa yazo inda take tabi ta asirce Kawu Madu sai abinda tace yayi yake ji shima wani lokacin tsoranta yake yi, Ta dinga tunanin irin wuyar da zasu sha ita da 'yayanta a gidan dan ga dukanin alamu Kuluwa ba tayi maraba da zuwansu ba, tunani take ko su tafi gidan Kawu Isa ne? sai ta tuno shi kuma ai bai da gidan kanshi haya yake kuma daki guda ne suke gamutsuwa dashi da matarshi da 'yayanshi.....Iya mai waina kuma ba ita kadai bace a gidanta tana da kishiyoyi kuma babu wadataccen gurin zama, dole dai gidan Kawu Madu din shine gurin zamansu, Kwallace ta taru a kwarmin idanunta tayi saurin gogewa, lokaci guda duniya ta juya musu baya, sun fara d'and'anar jin dadin rayuwa kuma sun koma gidan jiya............Sai a lokacin nadama mara amfani ta kamata ta dinga tunanin abubuwan da suka dinga faruwa a baya da irin kud'ad'en da 'yarta ta rike da samun nasarar auran Ahamdu tayi, Yanzu ne ta gane auran Ahamdu da 'yarta shine rufin asirinsu tasan da Wasilan na gidanshi har yanzu da tuni basu shiga wannan gararanbar ba.
Kuluwa ta shigo dakin hannunta rike da wata katuwar langa tana kallon Uwani tace"Naga kamar kema kina cikin alhini da damuwa to Allah yasa dai ba abin kunya kukayi a can ba kuka gudo nan dan naga alamun ciki a tattare da waccan 'yar taki."
Uwani ta kalleta ranta ya 'baci da maganarta amma saboda sanin halinta yasa tace"Eh kuluwa ki daina shakka ko kokwanto Wasila na da ciki amma kuma da Ubanshi."
Kuluwa ta ta'be bakinta tana fad'in "To yanzu naji zance Allah ya rabasu lafiya sai ki kira su kuci abinci gashinan babu yawa dai aci da hakuri tunda ban san da zuwanku ba." Uwani tace"To mungode." Kuluwa ta fita daga dakin, tana gyara daurin zaninta wanda yayi da'kal! da'kal da daud'a!
Uwani ta le'ko tana kiransu Wasila dake zaune jikin bishiyar darbejiya dake gidan.........Rashida da kyar ta lalla'bata suka koma dakin....suna shiga ta fito da sauri tana fad'in "Rashida ba zan iya ba wallahi mutuwa zanyi zuciyata tashi takeyi." Karaf a kunnan Kuluwa cikin fusata tace"Ke! buhun ubanki nace! Buhun ubanki kaji min shegiyar yarinya ciki haukane da zaki zo min gida kina min iskanci! har ki dinga cewa zuciyarki tashi takeyi to bari malam ya shigo wallahi kinji na rantse ba zaki zauna min a gida ni ba'a kawo min iskanci ehe! dama ai baku bane tilashin mu ita Uwanin itace tilas dinmu dan haka sai ku koma inda kuka fito abin arziki baya zama na tsiya." Takarashe maganar tana kumfar baki kai daka ganinta a fusace take! Uwani ta fito daga daki tana bata hakuri saboda tasan halin ta zata iya cewa su Wasilan baza su zauna a gidan ba kamar yanda ta fad'a, Hakuri take bata tana karyar dai muryarta sai rawa take! Kuluwa ta cigaba da aikinta tana sababi! da zagin Wasila
Uwani ta dauko langar abinci ta dire a gabansu tana fad'in " Ku kiyaye da wannan matar idan kuna son zaman lafiya bana son abinda kikeyi Wasila kinga bamu da gatan da yafi nan, Kuluwa macace mara hakuri zata iya sa Kawu yace ku bar mishi gida kamar yanda ta fad'a saboda haka duk abinda zakiji na tashin zuciya ki dinga daurewa kina hakuri haka take muguwar kazama ce tun tana da kuruciyarta gashi har girmanta......Wasila bata iya magana ba rashida ce mai magana tace"Gaskiya Uwani gidan nan baiyi wallahi duba fa ki gani ko ina kazanta da kashin dabbobi dubi bandaki babu kofa sai buhu kiji warin masai dake tasowa har nan kawai mu zamu tafi Garko ke kiyi zamanki nan tunda kece tasu."
Uwani ta marairaice fuskarta muryarta na rawa tace"Rashida kin san yanda nake son ku kuwa ? bana so kuyi nesa dani shiyasa na'ki aure na 'kare rayuwata tare daku, ina 'kaunarku saboda nasan bani da kowa sama daku, Uwata ta mutu Ubana ya mutu mijina ya mutu sai ku kawai nake kallo naji dadi idan kuka tafi Garko kuka barni wace irin rayuwa kuke tunanin zanyi a cikin garin nan."!?
Tausayin mahaifiyar tasu ne ya kama su, sai suka hau goge hawaye, suna adduar Allah ya kawo musu dauki da gaggawa amma hak'ikanin gaskiya mahaifiyar tasu tasha wuyar rayuwa ta kuma yi wahala dasu bai kamata su guje mata ba,
Zama tayi kusa dasu tana bud'e langar abincin aikuwa sai wani irin towon dawa ba'ki'kikirin yayi musu sallama! towon sai shaining yake ga wata uwar miya kamar fitsarin jaka, sai wake guda guda a cikin miyar tana ta warin daddawa......A guje Wasila ta mike ta nufi bakin rariya ta dinga kakarin amai tana zubar da kwalla! Kuluwa tayi azamar fitowa daga kicin da ludayi a hannunta....Wannan karon Uwani da kanta taje ta rirrik'e 'yar tata tana mata sannu ita kuwa sai rike ciki take tana mur'kususu da kiran sunan Allah! Kuluwa ta dinga kallonsu bakin cikin duniya kamar ya kasheta 'Kwafa tayi ta koma kicin din! Yau ba gobe ba zasu bar mata gidanta dan bata ciki da iskanci da wulakanci......Kawu Madu ya shigo gidan yana sa'be babbar riga sai kawai ya gansu cirko cirko Uwani da Rashida kan Wasila dake durkushe tana kakari......Yace."A'a Uwani meke faruwa ne Me yasa me ta take amai haka."? Kafin Uwani tace wani abu Kuluwa tayi zuruf ta fito daga kicin fuskarta a murtuke tace" 'Kyankyamina takeyi shine take amai tunda suka shigo gidanan basu shiga dakina ba can bakin bishiya suka zauna saboda suna kyankyamina saboda haka yau ba gobe ba zasu bar min gidana dan wallahi ba zan dauki wannan iskancin ba." A take Kawu Madu ya sha kunnu yana kallonsu rai a bace yace."Ashe baku da tarbiya dama? matar tawa kuke 'kyankyami!? to shikkenan dama ai baku ne tilas dina ba Mahaifitarku ce saboda haka zaku bar min gidana tunda baku da mutunci." Uwani ta shiga share hawaye tana fad'in "Kawu ba haka bane wallahi yarinyar nan nada ciki mai laulayi yana bata wuya dama tun a mota take amai har yanzu ba wai suna 'kyankyamin Kuluwa bane."
Yace."Uwani."! ta amsa yace."Shin yaushe kikayi wa yarinyar ki aure babu labari gashi nace tana da ciki."! Kuluwa tace"Nifa malam ban yarda ba wallahi wannan yarinya cikin shege tayi shine suka kwaso jiki suka gudo nan sabida gudun abin kunya dan haka wallahi ba'a gidan nan ba idan kuma kace tilas sai sun zauna to ni zan fice na baku guri."
Hankalin Kawu Madu ya tashi, Yace."A'a ba za'ayi hakaba Kuluwa ai duk wannan magana ma bata taso ba, ke Uwani zo ki zauna kiyi min bayanin abinda ke faruwa."
Kika futar min da book keda Allah! Kika karanta baki biya ba kema keda Allah Whasap numbar
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
[14/08, 12:04 pm] Farida Books: 'Yr Bngr Sys
*58*
Cike da farin ciki da walwala ya shiga gidan nashi yana kwalawa matarshi kira..........Kuluwa ta fito daga wani guri wanda alamu suka nuna cewar madafi ne (khicin) hannunta da wata katuwar mara da alama kwasar towo take, tace"Malam ganin nan Allah yasa lafiya irin wannan kira hak.....Kafin ta rufe bakinta sai idanunta ya sauka kansu Uwani da 'yayanta, lokacin 'kan'kani ta kirne fuska tana fad'in "A'a yau kuma Uwani ce a garin."? Uwani dasu Wasila duk sunga sauyin fuska a tare da ita, lokacin da take maganar da alama dai batayi maraba da zuwan su garin ba.......Kawu Madu yana washe hakoransa yace." Wallahi kau nima nayi mamaki sosai dan baki ji dadin da nakeji ba, abinci zamuci dasu malam tsalha na taso domun in shigo dasu gidan." Kuluwa tace"To sannunku da zuwa ku shigo ciki." Kawu Madu yace."Uwani ku shiga ciki a baku abinci ku huta ai da alama ma kun kwaso rana." Uwani tace"Aikuwa wallahi munsha zaman mota da gajiya." Kawu Madu ya juya ya fita yana fad'in "Bari nasa Ayuba yaje can cikin kasuwa ya siyo muku ruwan sanyi."
Uwani da Rashida suka shiga daukan jakkunansu dake yashe a tsakar gidan suka nufi dakin Kuluwa, suna shiga katuwar rumfa ce sai dai babu shinfida a cikinta sai guntattakin tabarmi da ledoji ko ina kaca kaci da kwari ka 'kananin kyankyasai ga wani uban 'kuda da yake tashi a rumfar da wani kafirin zarnin fitsarin yara......Tun lokacin da suka shiga rumfar Wasila ke yatsine ya tsinen fuska zuciya sai masifar tashi takeyi aikuwa kafin tayi wani yun'kuri amai ya kece mata! a guje! tayi waje ta nemi bakin rariya ta tsuguna ta dinga kelayashi tana kwallah......Rashida ce tsaye a kanta tana mata sannu duk ta shiga damuwa. Bayan ta gama aman ta bata ruwa ta wanke bakinta da fuskarta kana ta mike jiri na d'ibarta......Rashida ta rike hannunta wai su koma cikin d'akin girgiza kanta tayi da kyar tace"Rashida rabu dani don Allah zuciya tashi takeyi idan na koma gurin nan zan iya yin wani aman." Aikuwa karaf a kunnan Kuluwa ta rike baki tana fad'in "Ke ja'ira yarinyar me kike nufi? daga zuwa zaki fara yiwa mutane sanabe da iyayi kina nufin kazama ce ni kome." Rashida tayi saurin girgiza kanta tana fad'in "Ba haka take nufi ba baba." Kuluwa tace"To me take nufi da har zata shiga dakina ta rugu waje da gudu tana kwara amai." Rashida tace "bata da lafiya ne dama tun a mota cikin ta ke ciwo." Kuluwa ta girgiza kanta tana fad'in "Maji ma gani dai idan tusa zata hura wuta, kome kuke tafe dashi dai-dai nake daku to kaji."! Tana gama maganar ta ta shige madafi domin cigaba da aikinta.
Uwani na cikin dakin abin duniya yayi mata yawa, tunani takeyi yanzu wace irin rayuwa zasuyi cikin gidanan! tun da can baya tasan Kuluwa macace mara mutunci da muguwar kaxanta sam bata so kowa yazo inda take tabi ta asirce Kawu Madu sai abinda tace yayi yake ji shima wani lokacin tsoranta yake yi, Ta dinga tunanin irin wuyar da zasu sha ita da 'yayanta a gidan dan ga dukanin alamu Kuluwa ba tayi maraba da zuwansu ba, tunani take ko su tafi gidan Kawu Isa ne? sai ta tuno shi kuma ai bai da gidan kanshi haya yake kuma daki guda ne suke gamutsuwa dashi da matarshi da 'yayanshi.....Iya mai waina kuma ba ita kadai bace a gidanta tana da kishiyoyi kuma babu wadataccen gurin zama, dole dai gidan Kawu Madu din shine gurin zamansu, Kwallace ta taru a kwarmin idanunta tayi saurin gogewa, lokaci guda duniya ta juya musu baya, sun fara d'and'anar jin dadin rayuwa kuma sun koma gidan jiya............Sai a lokacin nadama mara amfani ta kamata ta dinga tunanin abubuwan da suka dinga faruwa a baya da irin kud'ad'en da 'yarta ta rike da samun nasarar auran Ahamdu tayi, Yanzu ne ta gane auran Ahamdu da 'yarta shine rufin asirinsu tasan da Wasilan na gidanshi har yanzu da tuni basu shiga wannan gararanbar ba.
Kuluwa ta shigo dakin hannunta rike da wata katuwar langa tana kallon Uwani tace"Naga kamar kema kina cikin alhini da damuwa to Allah yasa dai ba abin kunya kukayi a can ba kuka gudo nan dan naga alamun ciki a tattare da waccan 'yar taki."
Uwani ta kalleta ranta ya 'baci da maganarta amma saboda sanin halinta yasa tace"Eh kuluwa ki daina shakka ko kokwanto Wasila na da ciki amma kuma da Ubanshi."
Kuluwa ta ta'be bakinta tana fad'in "To yanzu naji zance Allah ya rabasu lafiya sai ki kira su kuci abinci gashinan babu yawa dai aci da hakuri tunda ban san da zuwanku ba." Uwani tace"To mungode." Kuluwa ta fita daga dakin, tana gyara daurin zaninta wanda yayi da'kal! da'kal da daud'a!
Uwani ta le'ko tana kiransu Wasila dake zaune jikin bishiyar darbejiya dake gidan.........Rashida da kyar ta lalla'bata suka koma dakin....suna shiga ta fito da sauri tana fad'in "Rashida ba zan iya ba wallahi mutuwa zanyi zuciyata tashi takeyi." Karaf a kunnan Kuluwa cikin fusata tace"Ke! buhun ubanki nace! Buhun ubanki kaji min shegiyar yarinya ciki haukane da zaki zo min gida kina min iskanci! har ki dinga cewa zuciyarki tashi takeyi to bari malam ya shigo wallahi kinji na rantse ba zaki zauna min a gida ni ba'a kawo min iskanci ehe! dama ai baku bane tilashin mu ita Uwanin itace tilas dinmu dan haka sai ku koma inda kuka fito abin arziki baya zama na tsiya." Takarashe maganar tana kumfar baki kai daka ganinta a fusace take! Uwani ta fito daga daki tana bata hakuri saboda tasan halin ta zata iya cewa su Wasilan baza su zauna a gidan ba kamar yanda ta fad'a, Hakuri take bata tana karyar dai muryarta sai rawa take! Kuluwa ta cigaba da aikinta tana sababi! da zagin Wasila
Uwani ta dauko langar abinci ta dire a gabansu tana fad'in " Ku kiyaye da wannan matar idan kuna son zaman lafiya bana son abinda kikeyi Wasila kinga bamu da gatan da yafi nan, Kuluwa macace mara hakuri zata iya sa Kawu yace ku bar mishi gida kamar yanda ta fad'a saboda haka duk abinda zakiji na tashin zuciya ki dinga daurewa kina hakuri haka take muguwar kazama ce tun tana da kuruciyarta gashi har girmanta......Wasila bata iya magana ba rashida ce mai magana tace"Gaskiya Uwani gidan nan baiyi wallahi duba fa ki gani ko ina kazanta da kashin dabbobi dubi bandaki babu kofa sai buhu kiji warin masai dake tasowa har nan kawai mu zamu tafi Garko ke kiyi zamanki nan tunda kece tasu."
Uwani ta marairaice fuskarta muryarta na rawa tace"Rashida kin san yanda nake son ku kuwa ? bana so kuyi nesa dani shiyasa na'ki aure na 'kare rayuwata tare daku, ina 'kaunarku saboda nasan bani da kowa sama daku, Uwata ta mutu Ubana ya mutu mijina ya mutu sai ku kawai nake kallo naji dadi idan kuka tafi Garko kuka barni wace irin rayuwa kuke tunanin zanyi a cikin garin nan."!?
Tausayin mahaifiyar tasu ne ya kama su, sai suka hau goge hawaye, suna adduar Allah ya kawo musu dauki da gaggawa amma hak'ikanin gaskiya mahaifiyar tasu tasha wuyar rayuwa ta kuma yi wahala dasu bai kamata su guje mata ba,
Zama tayi kusa dasu tana bud'e langar abincin aikuwa sai wani irin towon dawa ba'ki'kikirin yayi musu sallama! towon sai shaining yake ga wata uwar miya kamar fitsarin jaka, sai wake guda guda a cikin miyar tana ta warin daddawa......A guje Wasila ta mike ta nufi bakin rariya ta dinga kakarin amai tana zubar da kwalla! Kuluwa tayi azamar fitowa daga kicin da ludayi a hannunta....Wannan karon Uwani da kanta taje ta rirrik'e 'yar tata tana mata sannu ita kuwa sai rike ciki take tana mur'kususu da kiran sunan Allah! Kuluwa ta dinga kallonsu bakin cikin duniya kamar ya kasheta 'Kwafa tayi ta koma kicin din! Yau ba gobe ba zasu bar mata gidanta dan bata ciki da iskanci da wulakanci......Kawu Madu ya shigo gidan yana sa'be babbar riga sai kawai ya gansu cirko cirko Uwani da Rashida kan Wasila dake durkushe tana kakari......Yace."A'a Uwani meke faruwa ne Me yasa me ta take amai haka."? Kafin Uwani tace wani abu Kuluwa tayi zuruf ta fito daga kicin fuskarta a murtuke tace" 'Kyankyamina takeyi shine take amai tunda suka shigo gidanan basu shiga dakina ba can bakin bishiya suka zauna saboda suna kyankyamina saboda haka yau ba gobe ba zasu bar min gidana dan wallahi ba zan dauki wannan iskancin ba." A take Kawu Madu ya sha kunnu yana kallonsu rai a bace yace."Ashe baku da tarbiya dama? matar tawa kuke 'kyankyami!? to shikkenan dama ai baku ne tilas dina ba Mahaifitarku ce saboda haka zaku bar min gidana tunda baku da mutunci." Uwani ta shiga share hawaye tana fad'in "Kawu ba haka bane wallahi yarinyar nan nada ciki mai laulayi yana bata wuya dama tun a mota take amai har yanzu ba wai suna 'kyankyamin Kuluwa bane."
Yace."Uwani."! ta amsa yace."Shin yaushe kikayi wa yarinyar ki aure babu labari gashi nace tana da ciki."! Kuluwa tace"Nifa malam ban yarda ba wallahi wannan yarinya cikin shege tayi shine suka kwaso jiki suka gudo nan sabida gudun abin kunya dan haka wallahi ba'a gidan nan ba idan kuma kace tilas sai sun zauna to ni zan fice na baku guri."
Hankalin Kawu Madu ya tashi, Yace."A'a ba za'ayi hakaba Kuluwa ai duk wannan magana ma bata taso ba, ke Uwani zo ki zauna kiyi min bayanin abinda ke faruwa."