← Book details Yar Bangar Siyasa Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 4 OF 108

Sashe 4

Yar Bangar Siyasa Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Suna tafiya suna zan can Ahamad dashi da taurinka kansa Alhaji Ma'aruf na fada musu yanda suke dauki ba dad'i a kan suga bayanshi amma abun yaci tura yace shi har jinin kad'angare ya sha duk saboda yaga bayan Ahamd amma asirin bai kar'beshi ba a lokacin ma so yayi ya dawo kansa sai da bokan da ya kulla asirin ya warware tukkuna ya samu lafiya.

Wasila tace"Ka rabu dashi Alhaji duk ku daina wahalar da kanku da kudinku da yawon bin malamai a kanshi sharrina ma kad'ai ya isheshi sai nayi fata-fata da rayuwarshi."

Alhaji Ma'aruf yaji dadi maganar ta yace.''Mu kuma munyi miki alkawarin baki dadin duniya *Yar gaske* zaki fantama sosai da kudi sai dai ki bawa wasu."

Da jin wannan magana tashi sai Wasila ta sake daukar aniyar babu gudu babu ja da baya a kan Ahmadu Musa *(Ba iyak ka)* har sai taga abunda ya turewa buzu nadi.

'Karfe goma sha biyu saura na dare ya ajiyesu a kofar gidansu Ledoji cike da kayan dadi ya bawa Wasila rafar kudi ta dubu dari camas ya bata dubu hamsin sukayi sallama da juna kan cewar zasu fito da wurwuri domi zuwa yawon kamfen........

'Yar 'kofar da suke karawa Wasila ta tura firgigit Uwani ta mike zaune dama ba baccin take ba tana zaune tana dakon dawowar 'yar tata.

Wasila ta mayar da 'kofar ta kare gidan kana ta saki buhun dake sakale suka shiga cikin gidan suna ihu! kamar ba dare ba.

Uwani da Rashida suka fito a guje! Wasila ta farke rafar kudin dake hannunta ta soma mannawa Uwani a saman goshi.....Uwani na ganin Sabbin 'yan dubu-dubu na watsi a a tsakar gida sai ta fasa ihu! ta rungume! 'yar tata suka kama rawa wata lafiyayyar gud'a ta dinga rangadawa tana sakarwa 'yar tata kirari......Ita kuwa Rashida kudin take bi tana tsince tana ta faman kyalkyala Dariya sai kace mahaukaciya.

Sai da suka gama murnarsu sannan suka dauki ledojinsu suka shige ru'babbiyar rumfarsu da ta kusa ruftawa Rasida ta samo katon faranti suka baje wasu 'kosassan kaji guda shida wanda komai zulamar mutum bai iya cinye guda saboda girmansu ga had'ddaun lemuka masu sanyi nan suka baje suka dinga yagar kaza suna yi mata cin ala tsine uwar me karya, wai! yaushe rabon duniya da ayya raye."!! Uwani ta fada tana shigowa dakin bayan taje ta wanko hannunta........Wasila tace"Yanzu dai mu kwanta muyi bacci dare yayi sai gobe in yaso sai kuji labarin abunda yake faruwa.

Uwani tace"Ki d'an gutsira min wani abu mana na kwana dasu a karkashin filona anya ma kuwa yau zan iya bacci oh! duniya kenan."

Wasila tace"Uwani kwanta kiyi bacci harda munsharri ai insha Allahu mu da talauci munyi hannun riga." Uwani ta dinga wata mahaukaciyar dariya tana fad'in"Ai dama ni nasan jari na haifa ke ba 'karamar mace bace idan ba'aso ki dan komai ba a so ki dan 'kirar jikinki ita kuma Rashida wannan farar fatar tata itace jarina."

Wasila tace"Uwani nifa ba karuwanci naje nayi ba sana'a muka fita mukayi ko ba haka ba Camas!." Tafada tana kallon Camas! dake irga kudinta.

Camas tace"Kwarai kuwa sana'ar mukaje mukayi ta siyasa gobe zamu fita da wurwuri shiyasa ma ban wuce gida ba."

Uwani tace"Kai amma wannan sana'a ta karbeku wallahi Allah ya bada sa'a ya taimake ku."

Suka amsa da "ameen." Sannan ko wacce ta gyara shimfida ta yada ha'karkari ta kwanta ana jira kuma gari ya waye a fita *Sana'a*

_Muje Zuwa_
*BINTA UMAR ABBALE*
[7/13, 1:07 AM] Bintu: *'YAR BANGAR SIYASA!!*
🌺 romantic love story🌺
*NA:*
*BINTA UMAR ABBALE 🍒*
*🌍Manazarta Writes asso*
_'Kungiyar masu nazari da aiki da Ilimi_
~~~~~~~~
*NA KUDI NE.......!*
_Ga masu bukatar karanta book din zasu tura #300 Vip gruop #600 accont din da za'a tura kudin.0542382124.......Binta Umar gtbank....Idan katin waya mutum zai tura sai ya same ni ta wannan numbars din....07084653262_08089965176 sai na fad'i yanda za'a biya kud'in.....Mutanan mu na Nijar idan kuna bukatar book din zaku tura dala dari ta wannan numbars.......90899076_88137740 katin airtal ko orange

*Free Pege6*
Da safe suka tashi da wurwuri sukayi wanka tsaf suka shirya tuni Uwani ta ta fasa musu shayi Rashida ta siyo su madara da milo da bread har da su kwai Uwani ta soya musu yau karin kullamo sukayi rigijib suka karasa cinye sauran kajinsu na jiya....Wasila ta kalli Camas! dake gyara daurin dankwali tace"Ya kamata kije gida mamanku ta ganki kafin mu tafi ko." Camas! tace"Ke kin san idan na shiga gida yanzu babanmu nanan ba zai bari na sake fita ba kawai ki kyalesu idan na dawo ma had'u."

Tace"Shikkenan ke Rashida zan bada dubu talatin ayi aikin gidanan a sanya kokafi data waje data bandaki saboda bana so in doso layin nan wallahi in hango ku kamar tumaki a akurki wai sunan kuna cikin gida a zaune amma jama'ar dake waje na ganinku wannan gidan ai sunansa kango ba gida ba.

Uwani tace"Naji kinyi maganar dubu talatin duk a aikin gidan anya kuwa basuyi yawa ba." Tace"Na fiso ayi komai da inganci a sa kofofi masu kyau insha Allah yau ma idan mun fita zamu samo kudi.' Uwani tace"To Allah yasa." Wasila ta irga dubu talatin da biyar ta bawasu Uwani talatin na gyaran gida biyar kuma tace su dan auno kwanan shinkafa suyi cefane kafin ta dawo.......Haka sukayi musu sallama suka kama hanya suka tafi can guest house din Alhaji Ma'aruf dake a can yace su had'u.

Suna shiga harabar gurin suka wasu gugun matasa rukuni rukuni! amma 'yan daba da shaye-shaye sunfi yawa.....Alhaji Ma'aruf da wani mutumi suna tsaye a kansu suna magana dasu.

Kai tsaye can suka nufa Alhaji Ma'aruf na ganinsu ya washe baki ya kalli Alhaji Tasi'u "Yawwa kaga 'yan halak! ko yanzu yanzu mu ka gama zancensu ashe suna tafe.

Wasila tace" Aikuwa dai muna hanya wallahi kun san matsalar abun hawa sai a hankali." Alhaji Tasi'u ya kalli abokinsa yana nuna Wasila da bakinsa yace"Ko baka fada mun ba na gane wannan ce *Wasila 'Yar gaske!"* Yace."Kwarai kuwa Alhaji kayi mamakin ganinta 'yar karama ko." Yace."Dai-dai kenan duk da kankantar ta nasan zata bamu gudumawar da muke bukata daga gareta Wasila naji kina maganar abun hawa da sauransu ki kwantar da hankalinki zan siya miki mota ta kece raini ke dai kawai ki bamu goyon baya domin zamuyi amfani dake domin cimma manufarmu.''

A dake! tace"Kar ka damu Alhaji a shirye nake wallahi domin harkar na shigo gadan gadan duk inda nasan zan samu nan zan nufa in zaku sakar min kudi magana ta 'kare."

Alhaji Ma'aruf da Alhaji Tasi'u suka fashe da dariya suna tafawa, Sai bayan sun tsaigata da dariyar ne Alhaji Tasi'u yace."Kunga wad'ancan mutanan dake zazzaune ko."? Suka ce."Eh." yace."To zaku fita dasu yawon kamfen saboda mun samu labarin *Ahamadu (Ba iya ka)* zai fita zagaye gari domin yad'a munufarsa a kan talakawa to muna so duk inda suka shiga suna yad'a manufarsu su shi ku soke! ku watsa jama'a akwai kayan aiki a tare dasu Lauje karkuji komai kuyi aiki sosai mune muke da mulki a hannunmu babu wani abu da zai same ku."

Wasila tace"Kar ka damu alhaji nayi maka al'kawari bakin rai bakin fama." Alhaji Ma'aruf ya kalli Camas yana lumshe mata ido yace."Kefa baki ce komai ba."

Tace"Haba karfa ku damu nima na dauki alkawari insha Allah sai mun rusa shirin *Ba iya ka."*

Alhaji Tasiu ya nunawa matasan nan su Wasila yace sune abokanan tafiyarsu su kula dasu a matsayinsu na mata, har bakin mota suka rakasu suka shishhiga a'kalla sai da suka cika motaci hud'u irin na haya saboda yawansu sun kai su ashirin da wani abun....Kai tsaye suka dauki titin da zai futar da mutun cikin gari.

Cikin shadda fara kal ya fito yana daura agogon silvar a hannunshi hularshi ya kar'ba daga hannun Garba ya d'ora a kanshi *Ba kano* zallah yayi kyau har ya gaji ya zaune gefan gujera yana sanya safa Garba ya gama goge masa takalminsa sawu ciki ya mika masa ya sanya a kafafunsa yana mikewa Khalifa babban amininsa ya shigo shima yana sanya da manyan kaya shi harda babbar riga cikin kamala da mutumta juna suka gaisa kai kana ganin mu'amularsu zaka gane masu ilimi ne suna kuma aiki dashi........suna fita harabar gidan suka tadda matasa sun kai su goma duk suna jiran fitowarsa....Aikuwa ya dinga amsa gaisuwarsu yana daga musu hannu su kuma sun rud'e da fad'in" Sai kayi Ko garin ba kowa mu muna tare da kai kane za'bin talakawa, Kano sai *Dan Musa."*
Ahamad ya d'aga dukanin hannuwasa biyu sama da 'karfi yace." *CPC."!* Suka amsa da *"Sa'a!!!"* Yace."Sa'a ta mai rabo ce." Sukace "Kaine kake da Sa'a mai Sa'a." Ya saki murmushi da fad'in "Allah ya bawa mai rabo Sa'a." Suka amsa da "ameeen."!!!" Da sauri Garba ya bude masa bayan wata had'addiyar mota ya shiga Khalifa yabi bayanshi Garba da Dan uwanshi Hadi suka shiga sai direba ya shiga mazauninsa.....Kafin kice kwabo kin nemi jama'ar gurin nan kin rasa duk sun shisshige motocin dake fake a gurin domin su raka dan takararsu yad'a munufarshi.....Kai tsaye titin da zai sadaka da wata unguwa a cikin gari suka nufa mai suna *Jakara* nan yake so ya fara zuwa saboda yanda yake jin labarin unguwar babu kyau ga ta'bar'barewar al'amura da yawa tarbiyar yara matasa ta lalace babu sana'ar yi sai jagaliya da harkar gwan-gwan da sauransu yana so ya fara zuwa unguwar ya yad'a munfarashi kafin ya shiga sauran unguwanni.
Chapter 4 · 0% Book details