Sashe 79
Tubali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A can gidan Alhaji Idi Saleh Dakata kuwa.
A gajiye ya dawo gida, daga Tashar Arewa 24 TV da yaje, yanzu ya samu MD da kansa ya mishi bayanin ɓacewar Jannart da kuma hukuma da suka shiga lamarin kana yasa gidajen Rediyo su cekinta su kuma ya bawa gidan tv nasu cekiyar gaggawa.
Daga nan kuma asibitin Dr Lukman ya wuce inda anan sukayi tattaunawa mai yawa kana ya nufo gida.
Da sauri Mom tabi bayanshi.
Tana cewa.
“Alhaji anji lbrin Jannart kuwa?”.
Da sauri ta matsoshi ganin yadda ya dafe kanshi da hannaye bibbiyu yana mai jujjuya kanshi.
Kana ya tafi lu alamun zai fadi.
Cikin tsananin tashin hankali da kidima Mom ta saki ihu tare da isowa gareshi ta tallabeshi murya na rawa take kwarmawa Abdul kira.
da gudu Abdul ya shigo cikin tashin hankali tace.
“Abdul kira min Barrister Kabir Abbanku kace Daddynku ba lfy”.
Kafin ta ƙare mgnar kuma Alhaji idi Saleh Dakata ya sake gaba ɗaya naushin ya jata suka tafi kasa bisa carpet.
Ganin haka ne yasa Abdul gigicewa tare da zaro wayarsa ya kira Barrister Kabir.
Wanda shi kuma lokacin ya fito daga gida shi kenan.
Koda Abdul ya gaya masa abinda ke faruwa.
A firgici ya dauko ya wuce asibitin Dr Sajo ya dauko shi.
A gidan Alhaji Idi Saleh Dakata'n kuwa, suna cikin gigin suka jiyo muryar Dr Lukman yana sallama hakane yasa Mom sakin dogon numfashi tare da cewa.
“Dr ka shigo, kayi sauri shigo ka taimaka mana Alhaji zai fadi”.
Jin hakane yasa Dr Lukman kutsa kai cikin main falon nasu da hanzarin.
Daga nan shida Abdul suka tallabeshi suka a mota suka wuce asibitin Dr Lukman din.
Suna tafiya ba jimawa.
Barrister Kabir da Dr Sajo suka iso.
Bayan Ashiru ya musu bayanine suka nifi asibitin Dr Lukman ɗin.
A nan gidansu Rayyern kuwa.
Bacci Jannart tayi sosai dan Koda ta tashi tayi sallan la’asar sake komawa tayi ta kwanta.
Ahaka dai har magriba.
9:30 pm dai-dai ya shigo gidan, wanda kuma tun fitan da yayi da safe sai yanzu yake shigowa.
Da sallama abakinsa ya tura kofar main falon ya shigo.
Jin da yayi ko ina shiru babu alaman motsin kowa ne, yasa kaitsaye ya wuce sama, saboda yasan zuwa yanzu su Mamyn nasa sunyi bacci.
Yana haurawa saman kuwa, anan cikin falonsu ya samu Ramadan da Riyyam, ko wannensu rungume da waya ba abunda sukeyi sai chatting.
Kana ga TV a kunne tashar Arewa 24 TV.
Yayinda su basuma san me akeyi a TV'n ba.
A hankali ya ɗan juyo ya kalli TV'n sabida ganin program ɗin da Jannart tayi dashi ake haskawa.
Idanunshi ya zubawa rubutun dake tafiya kasan hotonsu mai motsin da yake fuskar TV'n.
*Daya daga cikin ma'aikatan wannan ma'aikata Mai gabatar da shirin Baƙon mako mai suna Jannart idi Saleh Dakata ta bata tun daren jumma'a, kana har yau babu ita babu lbrin ta, a madadin tashar Arewa 24 TV muna cekinta Tata ga duk wanda Allah yasa ya ganta ko yaji lbrinta, ya taimaka ya nemi ɗaya daga cikin wadannan numbers din... akwai tukuici mai girma ga duk wanda ya kawo ta ko lbrinta kimanin Naira million 5. Muna addu'a Allah ya baiyana ta ya kuma bawa mahaifinta lfyar jikinsa wanda sanadin batanta ya tada masa ciwonsa*
Wani irin numfashin ya fesar a hankali tare da mai-maita karanta rubutun a karo na barkatai.
Can cikin zuciyarsa yake nazari.
“Tabbas akwai gadar zaren da ake sakawa, wanda ake neman mai ruftawa a ciki.
Dole suna da manufa a kaina.
Amman manufar Barrister Kabir tafi ta kowa girmama a kaina, tabbas ba haka kawai ya zaɓeni ya lika min wannan mayataccen aurenba, nasani haƙƙun nasan akwai wata boyeyyiyar manufa da niyarsa ta liƙamin auren ya kawo diyarsu ya ajiye mana a cikin gida.”
Idonshi ya lumshe tare da buɗe kana yaci gaba da nazari.
“Wani wasane suke son bugawa dani, yarsu ta zamo yar leken asirinsu kenan itace zata basu duk wata damar cimma nasarar turani kan gadar zaren da suke saƙamin ko meye.
Itace mai iya buɗe musu kofa ta su shigo rayuwata.
Meyasa Abba na bai gane hakabanba ya akayi Abba na yayi saurin yarda dasu?”.
Numfashi mai nauyi yaja ya sauƙe tare da yin kwaffa.
Wanda sanadin hakane su Ramadan suka gane ya shigo.
Kallonsu kawai yayi tare da amsa sannu da dawowan da sukeyi masa.
Idonshi ya kuma maida kan TV inda ake haska fuskarsa data Jannart.
Batare daya ce musu komai ba, ya wuce zuwa dakinsa.
Yana shiga ya soma rage kayan jikinsa, tare ci gaba da nazari.
“Me Barrister Kabir yake nufi dani? Alhaji idi Saleh Dakata dai ɗan uwansa ne uwa ɗaya uba ɗaya.
Kana ita kuma wannan Jalila ne ko jalilu ne, yarsa ce ta cikinsa.
Haƙƙun Barrister Kabir medani tsanin hawa yake son yi!.”
A hankali ya tura ƙofar shiga toilet.
A fili yace.
“Me yasa Abbana ya yarda dashi, ya akayi yayi saurin gamsuwa dashi.
Bayan kuma shine ya dauramu kan turbar kebanta kai da mutane da gudunsu da rashin yarda dasu.
Sanadin haka muka taso ba abokai ba kawaye bama sakin jiki da kowa, daga ni har Ramadan, sabida horaswar Abbanmu ta gudun mu'amala da mutane,
Yasha cemin.
Rayyern ɗan adam abin tsorone kada ka yarda da kowa, mutun duhun darene Allah kadai ke saninsa!
To ya akayi yayi saurin yarda da Barrister Kabir?
Tabbas shima Abba na akwai manufar yardar sa”.
A hankali ya ɗago ƙafarsa ta hagu ya sa cikin Bathroom din.
Hannunshi duka biyu yasa ya matse kanshi da ƙarfi.
Dan yadda yakejin kansa na jujjuyawa nazarurrukansu na hautsinewa suna haɗe zaren suna curkudeshi.
Duk da azabebben sanyin da akeyi.
Ruwan sanyin ya sakarwa kansa.
Sabida jin kan nashi ya fara sarawar.
Bayan ya fito ne kuma, ya shirya kansa cikin wasu tattausun kayan bacci.
Wondon iya guiwa rigar irin mai hular nan.
Fridge d’insa dake cike da kayan ciye ciye ya bud’e, Apple goran swan water da kuma ledan diary milk ya d’auko.
Tare da komawa kan gadonsa ya zauna cikin sanyi yace.
“Ta yaya zan yarda da ita, a wani sashin ma zan ajiyeta bayan nasan ita ɗin makamin magautanane sun turora cikin rayuwata ne dan cin nasarar kansu a kaina.
Meyasa Abba na bai fahimci hakaba.
Itama da mugun nufinta a ranta fa, iyayenta zatayiwa aiki”.
Yayi mgnar yana mai ajiye Jannart a sashin da yake ajiye magautansa a cikin zuciyarsa da rayuwarsa da waɗanda yake zargi.
A hankali ya jujjuya kansa.
Kana ya ɗan gatsi apple din ya soma ci bayan ya gama ne kuma, ya daura chocolate d’insa da ruwa akai.
Numfashi ya ɗan fesar
Kana ya kwanta yana mai nazari.
A nan asibitin Dr Lukman kuwa.
Barrister Kabir ne da Mom ke zaune gaban table ɗin Dr Lukman.
“BP'nsa ne ya hau sama sosai, sabida tashin hankali rashin yarsa.
Kana kuma rashin baccin da baya samun yi, sai nazari da damuwa yasa zuciyarsa ta kumbura.”
Dr Lukman ya ƙare mgnar yana mai yin ƙasa da idonshi sabida wani irin tsareshi da ido da Barrister Kabir yayi.
Cikin zubda hawaye Mom tace.
“Innallahi wa innailaihi rajiun, zuciyarsa kuma ta kumbura?”.
Cikin murje ido yace.
“Hakkun kuwa, sabida damuwa tayi mishi yawa, Jannart ta bata kana shima Junaid yana hannun hukuma, wanda kuma ƙaninsa uwa ɗaya uba ɗaya yasa aka kama ɗan nashi da wanne abu ɗaya zaiji?”.
Cikin haɗe fuska Barrister Kabir yace.
“Shine yace ma ni na kai Junaid hannun hukuma?”.
Da sauri ya girgiza kai alamun a'a
Miƙewa tsaye yayi tare da cewa.
“Toh ka tsaya iya matsayinka, ka tabbatar da abu kafin kayi mgn”.
Yana faɗin haka ya mike ya fita.
Dakin da aka kwantar da Daddy ya nufa a bakin ƙofar shigowa yayi kiciɓis da Dr Sajo.
Hannunshi Dr Sajo yaja kana suka juya suka nufi parking lot.
Cikin motar Dr Sajo suka shiga.
Wani dogon numfashi Dr Sajo ya sauƙe kana a nitse yace.
“Dr Mina da Dr Lukman yayi aikin duba Alhaji tare da ita, ƙanwatace cousin sister na.
Na samu duk bayanin komai a wurinta”.
Da sauri Barrister Kabir yace.
“Dan Allah menene gskyan abun dake damun Yayana?”.
Kai Dr Sajo ya jinjina tare da yiwa Barrister Kabir duk abinda Dr Mina ta sanar masa...
A nan Office din din Dr Lukman Kuma Barrister Kabir na fita, itama Mom ta fita.
Ta koma wurin mijin nata.
Ba ji mawa Barrister Kabir ya dawo akan dole a sallami yayanshi zasu sauya asibiti.
Kuma dole haka akayi.
Aka medashi asibitin Dr Sajo.
Washegari.
Kamar dai jiya yaudinma Jannart ce ta-taya Mamy duk wasu aikace-aikacen gida, bayan sun kammala ne kuma suka zauna suna dan tab’a hira.
Kasan cewar yau Monday ne tushen aiki.
Yasa tuni Ramadan ya tafi.
Riyyam-nsra kuma Ahmad yazo sun tafi gidan Malam Mai-nasara.
Takwas saura kwata. Ya sauko falon.
Cikin shigar Suit red color masu masifar kyau.
Hannunsa riƙe da wayarsa yana mgn.
Cikin sauri ya kalli Mamy tare da cewa.
“Mamy na tafi”.
Kafin ma tace wani abu tuni ya nufi hanyar fita.
Kawai sai ta bishi da ido.
Har ya fita kuma sai ya juyo ya leƙe fuska ya kwaɓe tare da cewa.
“Mamy na tafi”.
Murmushi tayi dan dama tasan tabbas zai juyo muddin batace mishi.
Allah ya bada sa'a yayi muku al'baka.
Cikin sauri ya kuma cewa.
“Mamy zan tafi”.
Fuska ta tsuke tare da cewa.
“Ka dawo kayi breakfast”.
Cikin kwaɓe fuska yace.
“Mamy sai na dawo, kinga Ramadan keta kirana, wai akwai matar da aka kawo haihuwa yaƙi kuma dole sai anyi mata CS, dan Allah Mamy ce Allah ya bani Sa'a yayi min al'barka Please Mamy say something".
Ta sani in dai yace bazai ciba ko ta matsa mishi bazaici yadda take sonba.
Hakane yasa tace.
“Toh Babana Allah ya bada sa'a ayi aiki lfy rabbil yayi maka al'barka”.
Da sauri ya juya yana mai cewa.
“Yessss Mamy Amin Amin”.
Da ido ta bishi tana murmushi tana tuno wasu abubuwa masu tarin yawa.
A gajiye ya dawo gida, daga Tashar Arewa 24 TV da yaje, yanzu ya samu MD da kansa ya mishi bayanin ɓacewar Jannart da kuma hukuma da suka shiga lamarin kana yasa gidajen Rediyo su cekinta su kuma ya bawa gidan tv nasu cekiyar gaggawa.
Daga nan kuma asibitin Dr Lukman ya wuce inda anan sukayi tattaunawa mai yawa kana ya nufo gida.
Da sauri Mom tabi bayanshi.
Tana cewa.
“Alhaji anji lbrin Jannart kuwa?”.
Da sauri ta matsoshi ganin yadda ya dafe kanshi da hannaye bibbiyu yana mai jujjuya kanshi.
Kana ya tafi lu alamun zai fadi.
Cikin tsananin tashin hankali da kidima Mom ta saki ihu tare da isowa gareshi ta tallabeshi murya na rawa take kwarmawa Abdul kira.
da gudu Abdul ya shigo cikin tashin hankali tace.
“Abdul kira min Barrister Kabir Abbanku kace Daddynku ba lfy”.
Kafin ta ƙare mgnar kuma Alhaji idi Saleh Dakata ya sake gaba ɗaya naushin ya jata suka tafi kasa bisa carpet.
Ganin haka ne yasa Abdul gigicewa tare da zaro wayarsa ya kira Barrister Kabir.
Wanda shi kuma lokacin ya fito daga gida shi kenan.
Koda Abdul ya gaya masa abinda ke faruwa.
A firgici ya dauko ya wuce asibitin Dr Sajo ya dauko shi.
A gidan Alhaji Idi Saleh Dakata'n kuwa, suna cikin gigin suka jiyo muryar Dr Lukman yana sallama hakane yasa Mom sakin dogon numfashi tare da cewa.
“Dr ka shigo, kayi sauri shigo ka taimaka mana Alhaji zai fadi”.
Jin hakane yasa Dr Lukman kutsa kai cikin main falon nasu da hanzarin.
Daga nan shida Abdul suka tallabeshi suka a mota suka wuce asibitin Dr Lukman din.
Suna tafiya ba jimawa.
Barrister Kabir da Dr Sajo suka iso.
Bayan Ashiru ya musu bayanine suka nifi asibitin Dr Lukman ɗin.
A nan gidansu Rayyern kuwa.
Bacci Jannart tayi sosai dan Koda ta tashi tayi sallan la’asar sake komawa tayi ta kwanta.
Ahaka dai har magriba.
9:30 pm dai-dai ya shigo gidan, wanda kuma tun fitan da yayi da safe sai yanzu yake shigowa.
Da sallama abakinsa ya tura kofar main falon ya shigo.
Jin da yayi ko ina shiru babu alaman motsin kowa ne, yasa kaitsaye ya wuce sama, saboda yasan zuwa yanzu su Mamyn nasa sunyi bacci.
Yana haurawa saman kuwa, anan cikin falonsu ya samu Ramadan da Riyyam, ko wannensu rungume da waya ba abunda sukeyi sai chatting.
Kana ga TV a kunne tashar Arewa 24 TV.
Yayinda su basuma san me akeyi a TV'n ba.
A hankali ya ɗan juyo ya kalli TV'n sabida ganin program ɗin da Jannart tayi dashi ake haskawa.
Idanunshi ya zubawa rubutun dake tafiya kasan hotonsu mai motsin da yake fuskar TV'n.
*Daya daga cikin ma'aikatan wannan ma'aikata Mai gabatar da shirin Baƙon mako mai suna Jannart idi Saleh Dakata ta bata tun daren jumma'a, kana har yau babu ita babu lbrin ta, a madadin tashar Arewa 24 TV muna cekinta Tata ga duk wanda Allah yasa ya ganta ko yaji lbrinta, ya taimaka ya nemi ɗaya daga cikin wadannan numbers din... akwai tukuici mai girma ga duk wanda ya kawo ta ko lbrinta kimanin Naira million 5. Muna addu'a Allah ya baiyana ta ya kuma bawa mahaifinta lfyar jikinsa wanda sanadin batanta ya tada masa ciwonsa*
Wani irin numfashin ya fesar a hankali tare da mai-maita karanta rubutun a karo na barkatai.
Can cikin zuciyarsa yake nazari.
“Tabbas akwai gadar zaren da ake sakawa, wanda ake neman mai ruftawa a ciki.
Dole suna da manufa a kaina.
Amman manufar Barrister Kabir tafi ta kowa girmama a kaina, tabbas ba haka kawai ya zaɓeni ya lika min wannan mayataccen aurenba, nasani haƙƙun nasan akwai wata boyeyyiyar manufa da niyarsa ta liƙamin auren ya kawo diyarsu ya ajiye mana a cikin gida.”
Idonshi ya lumshe tare da buɗe kana yaci gaba da nazari.
“Wani wasane suke son bugawa dani, yarsu ta zamo yar leken asirinsu kenan itace zata basu duk wata damar cimma nasarar turani kan gadar zaren da suke saƙamin ko meye.
Itace mai iya buɗe musu kofa ta su shigo rayuwata.
Meyasa Abba na bai gane hakabanba ya akayi Abba na yayi saurin yarda dasu?”.
Numfashi mai nauyi yaja ya sauƙe tare da yin kwaffa.
Wanda sanadin hakane su Ramadan suka gane ya shigo.
Kallonsu kawai yayi tare da amsa sannu da dawowan da sukeyi masa.
Idonshi ya kuma maida kan TV inda ake haska fuskarsa data Jannart.
Batare daya ce musu komai ba, ya wuce zuwa dakinsa.
Yana shiga ya soma rage kayan jikinsa, tare ci gaba da nazari.
“Me Barrister Kabir yake nufi dani? Alhaji idi Saleh Dakata dai ɗan uwansa ne uwa ɗaya uba ɗaya.
Kana ita kuma wannan Jalila ne ko jalilu ne, yarsa ce ta cikinsa.
Haƙƙun Barrister Kabir medani tsanin hawa yake son yi!.”
A hankali ya tura ƙofar shiga toilet.
A fili yace.
“Me yasa Abbana ya yarda dashi, ya akayi yayi saurin gamsuwa dashi.
Bayan kuma shine ya dauramu kan turbar kebanta kai da mutane da gudunsu da rashin yarda dasu.
Sanadin haka muka taso ba abokai ba kawaye bama sakin jiki da kowa, daga ni har Ramadan, sabida horaswar Abbanmu ta gudun mu'amala da mutane,
Yasha cemin.
Rayyern ɗan adam abin tsorone kada ka yarda da kowa, mutun duhun darene Allah kadai ke saninsa!
To ya akayi yayi saurin yarda da Barrister Kabir?
Tabbas shima Abba na akwai manufar yardar sa”.
A hankali ya ɗago ƙafarsa ta hagu ya sa cikin Bathroom din.
Hannunshi duka biyu yasa ya matse kanshi da ƙarfi.
Dan yadda yakejin kansa na jujjuyawa nazarurrukansu na hautsinewa suna haɗe zaren suna curkudeshi.
Duk da azabebben sanyin da akeyi.
Ruwan sanyin ya sakarwa kansa.
Sabida jin kan nashi ya fara sarawar.
Bayan ya fito ne kuma, ya shirya kansa cikin wasu tattausun kayan bacci.
Wondon iya guiwa rigar irin mai hular nan.
Fridge d’insa dake cike da kayan ciye ciye ya bud’e, Apple goran swan water da kuma ledan diary milk ya d’auko.
Tare da komawa kan gadonsa ya zauna cikin sanyi yace.
“Ta yaya zan yarda da ita, a wani sashin ma zan ajiyeta bayan nasan ita ɗin makamin magautanane sun turora cikin rayuwata ne dan cin nasarar kansu a kaina.
Meyasa Abba na bai fahimci hakaba.
Itama da mugun nufinta a ranta fa, iyayenta zatayiwa aiki”.
Yayi mgnar yana mai ajiye Jannart a sashin da yake ajiye magautansa a cikin zuciyarsa da rayuwarsa da waɗanda yake zargi.
A hankali ya jujjuya kansa.
Kana ya ɗan gatsi apple din ya soma ci bayan ya gama ne kuma, ya daura chocolate d’insa da ruwa akai.
Numfashi ya ɗan fesar
Kana ya kwanta yana mai nazari.
A nan asibitin Dr Lukman kuwa.
Barrister Kabir ne da Mom ke zaune gaban table ɗin Dr Lukman.
“BP'nsa ne ya hau sama sosai, sabida tashin hankali rashin yarsa.
Kana kuma rashin baccin da baya samun yi, sai nazari da damuwa yasa zuciyarsa ta kumbura.”
Dr Lukman ya ƙare mgnar yana mai yin ƙasa da idonshi sabida wani irin tsareshi da ido da Barrister Kabir yayi.
Cikin zubda hawaye Mom tace.
“Innallahi wa innailaihi rajiun, zuciyarsa kuma ta kumbura?”.
Cikin murje ido yace.
“Hakkun kuwa, sabida damuwa tayi mishi yawa, Jannart ta bata kana shima Junaid yana hannun hukuma, wanda kuma ƙaninsa uwa ɗaya uba ɗaya yasa aka kama ɗan nashi da wanne abu ɗaya zaiji?”.
Cikin haɗe fuska Barrister Kabir yace.
“Shine yace ma ni na kai Junaid hannun hukuma?”.
Da sauri ya girgiza kai alamun a'a
Miƙewa tsaye yayi tare da cewa.
“Toh ka tsaya iya matsayinka, ka tabbatar da abu kafin kayi mgn”.
Yana faɗin haka ya mike ya fita.
Dakin da aka kwantar da Daddy ya nufa a bakin ƙofar shigowa yayi kiciɓis da Dr Sajo.
Hannunshi Dr Sajo yaja kana suka juya suka nufi parking lot.
Cikin motar Dr Sajo suka shiga.
Wani dogon numfashi Dr Sajo ya sauƙe kana a nitse yace.
“Dr Mina da Dr Lukman yayi aikin duba Alhaji tare da ita, ƙanwatace cousin sister na.
Na samu duk bayanin komai a wurinta”.
Da sauri Barrister Kabir yace.
“Dan Allah menene gskyan abun dake damun Yayana?”.
Kai Dr Sajo ya jinjina tare da yiwa Barrister Kabir duk abinda Dr Mina ta sanar masa...
A nan Office din din Dr Lukman Kuma Barrister Kabir na fita, itama Mom ta fita.
Ta koma wurin mijin nata.
Ba ji mawa Barrister Kabir ya dawo akan dole a sallami yayanshi zasu sauya asibiti.
Kuma dole haka akayi.
Aka medashi asibitin Dr Sajo.
Washegari.
Kamar dai jiya yaudinma Jannart ce ta-taya Mamy duk wasu aikace-aikacen gida, bayan sun kammala ne kuma suka zauna suna dan tab’a hira.
Kasan cewar yau Monday ne tushen aiki.
Yasa tuni Ramadan ya tafi.
Riyyam-nsra kuma Ahmad yazo sun tafi gidan Malam Mai-nasara.
Takwas saura kwata. Ya sauko falon.
Cikin shigar Suit red color masu masifar kyau.
Hannunsa riƙe da wayarsa yana mgn.
Cikin sauri ya kalli Mamy tare da cewa.
“Mamy na tafi”.
Kafin ma tace wani abu tuni ya nufi hanyar fita.
Kawai sai ta bishi da ido.
Har ya fita kuma sai ya juyo ya leƙe fuska ya kwaɓe tare da cewa.
“Mamy na tafi”.
Murmushi tayi dan dama tasan tabbas zai juyo muddin batace mishi.
Allah ya bada sa'a yayi muku al'baka.
Cikin sauri ya kuma cewa.
“Mamy zan tafi”.
Fuska ta tsuke tare da cewa.
“Ka dawo kayi breakfast”.
Cikin kwaɓe fuska yace.
“Mamy sai na dawo, kinga Ramadan keta kirana, wai akwai matar da aka kawo haihuwa yaƙi kuma dole sai anyi mata CS, dan Allah Mamy ce Allah ya bani Sa'a yayi min al'barka Please Mamy say something".
Ta sani in dai yace bazai ciba ko ta matsa mishi bazaici yadda take sonba.
Hakane yasa tace.
“Toh Babana Allah ya bada sa'a ayi aiki lfy rabbil yayi maka al'barka”.
Da sauri ya juya yana mai cewa.
“Yessss Mamy Amin Amin”.
Da ido ta bishi tana murmushi tana tuno wasu abubuwa masu tarin yawa.