Sashe 53
Tubali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Akaro na biyu kenan yanzun da suka sake shigewa duniyar Mazinata, duniyar da muninta ya wuce misali, kyamatacciyar duniya marar kyaun gani mai cike da masifu wanda duniyar TIKTOK ya zamo kawali'unsu.
Bayan Riyyam din ya fito awankane kuma, ya shirya kansa cikin shigar daya saba yi ta kananan kaya.
Wayarsa dake aje kan table ya d’auka tare da Kallon yarinyar da take kokarin saka kayanta.
Bandir din fararen y’an one one k dake hannunsa ya cilla mata.
Tare da d’alewa saman table din ya zauna, hakanan yakejin wani irin haushi, takaici, da kuma kunci acikin zuciyarsa, Yayinda yaji ko ganin yarinyar baya mason sake yi.
Sometimes kuma baisan Meyasa yakejin hakan ba, aduk lokacin da yayi sex da mace, bayan ya samu biyan bukatarsa sai yaji duk duniyar ma batayi masa dadi.
Itakuwa Yarinyar ganin da tayi mood d’insa ya sanja ne, yasa ta tattare kudin daya watso matan ta zuba acikin Jakarta.
Bayan ta gama kimtsa kanta ne kuma tayi masa sallama ta tafi.
Kamar kuwa dama jiran tafiyan nata yake, Domin tana tafiya shima ya rufe dakin.
Bayan ya bada key din a reception ne kuma, kaitsaye ya fito daga cikin hotel din.
Taxi ya tara, tare da fad’awa mai taxi din ya kaisa can cikin Nassarawa G.R.A din.
Acan b’angaren Rayyern kuwa bai baro Companyn nasu ba, har saida ya kammala duk wani abu da yakeyi.
Koda ya fito daga cikin company din kuma, kaitsaye motarsa ya shiga.
Inda suka nufo gida.
Isowarsu bakin gate din gidan kuwa, yayi dai-dai da fitowar Riyyam nsra din acikin taxi.
Ganin motar Rayyern dinne kuma yasa Riyyam sakin murmushi,
Bayan ya biya mai taxi din kudinsa ne kuma kaitsaye ya nufi cikin gidan.
Kasancewar tuni motar Rayyern din ta shige ciki.
“Baba Maud’o barka da gida.”
Riyyam din ya fad’a alokacin daya bud’e karamar kofar gate din ya shigo.
Baba Maud’o dake zaune kuwa, ganin Riyyam dinne yasa kashi sakin murmushi.
Cikin kulawa kuma yace.
“Yauwa barka dai Riyyam, tun safe yau baka zoba sai yanzu ka samu zuwa kenan.”
Kai Riyyam din ya jinjina tare da cewa.
“Eh, yau din nayi bacci sosai, kuma abokai na sun kawomin ziyara shiyasa Banzo da wuri ba.”
Kai kawai Baba Maud’on ya jinjina, Yayinda shikuwa Riyyam kaitsaye ya nufi inda motar Rayyern yake.
Yana zuwa wajen kuwa Rayyern na fitowa daga cikin motar.
K’arasowa Riyyam din yayi, cikin sauri yace. “Oyoyo Hamma Rayyern sannu da dawowa.”
Ya k’are maganan yana me rungume Rayyern din.
Rayyern kuwa zame jikinsa ya d’anyi, tare da jinjina kansa alaman yauwa.
Kamar zaice wani abu kuma sai ya fasa, kaitsaye duk suka nufi babban falon gidan.
Yayinda afakaice kuma Rayyern ke Kallon Riyyam din, Domin hakanan yaji zuciyarsa na raya masa wani abu na daban, dangane da Riyyam din musamman kamshin turaren jikinsa da yaji wanda ya tabbatar turaren matane.
Shigowarsu cikin falonne kuma yasa.
Hankalin Mamy dana Ramadan harma da Abba ya dawo kansu.
Ganin Rayyern dinne kuma yasa Abba sakin murmushi.
Yayinda Riyyam kuwa ke biye dashi abaya.
Karasowa cikin falon sukayi suka zauna.
Inda Riyyam ya durkusa har kasa ya gaishe da Abba da Mamy, fuska asake duk suka amsa masa.
Rayyern kuwa da ya Zauna akan kujeran dake gefen na Mamy.
Kallon Abban nasu yayi tare da cewa.
“Abba Mamy barka da gida.”
“yauwa Rayyern barka dai ya company’n.”
Abba ya tambaya.
“Alhamdulillah Abba komai yana tafiya dai-dai an kusa gama haɗa komai.”
Rayyern din ya fad’a yana me d’an gyara zamansa, tare kuma da sauk’e idanunsa akan, Riyyam wanda yaje ya manne da jikin Ramadan.
“Masha Allah Allah ya taimaka.”
Abba da Mamy suka hada baki wajen fad’an hakan.
“Ameen.” Ya amsa still yana mai Kallon Riyyam.
Kwarai so yake ya fahimci yaron, saboda yarda da abunda zuciyarsa ke gaya masa, yanaji ajikinsa cewar yaron kamar yana bin mata, musamman Idan akayi duba da irin rawar kan da yake dashi, ya cika rawar Kai da yawa.
Janye kansa daga Kallon Riyyam din yayi, saboda bayason yana shiga abunda bai shafesa ba.
Ramadan kuwa dake rik’e da wayarsa d’ago kansa yayi ya kalli Rayyern din.
Cikin sigar lallashi hadi da roko kuma yace.
“Yauwa Hamma Rayyern dama kai nake jira ka dawo, please Hamma Rayyern Dan Allah ka fito da mata kasamu kayi aure, kaga Abba yace bazanyi aure ba harsai kayi, ni kuma Allah yanzu aure nakeso nayi, bana son na rasa Rayhanna please Hamma na.”
ya k’are maganan yana me d’an langwab’ar da kansa gefe.
Shikuwa Rayyern d’ago kansa yayi, da kuma fuskarsa wacce ta sanja kala zuwa yanayin bacin rai.
Wani irin kallo ya watsawa Ramadan din, cikin hade fuska yace.
“Rufe min baki Ramadan kada fa ka tunzura min zuciya Kaine zaka tsaramin yanda zan tafiyar da rayuwata? Ko ka fini sanin abunda nakeyi ne, da har zaka zo kana cewa wai nayi aure! Kai ubana ne!? ko yayana!? kama fini sanin abinda ya dace kenan?.”
Rayyern din ya k’are maganan cikin fad’a.
Wanda hakan yasa Ramadan Dan sunkuyar da kansa, cikin yanayin sanyi kuma yace.
“Ayyah Hamma Rayyern kayi hakuri Insha Allah bazan sake ba kaji kayi haƙuri.”
Kai Rayyern din ya kawar, Yayinda Abba da Mamy kuwa suka kalli junansu.
Ramadan kuma mik’ewa tsaye yayi, tare da kama hannun Riyyam-nsra suka fice daga cikin falon.
Fitansu daga cikin falonne kuma yasa Abba d’ago Kai ya kalli Rayyern din.
Yayinda su Ramadan kuwa suna fita, kaitsaye wajen Baba Maud’o dake zaune abakin gate suka nufa.
Ganin su dinne kuma yasa Baba Maud’o sakin murmushi.
Bayan sun zauna akan dogon bencin da Baba Maud’on ke kaine kuma.
Baba Maud’on Ya kalli Riyyam-nsra tare cewa.
“Riyyam ya mutanen can k’asar taku, da su Mammyn ka da Zaiton.”
Murmushi Riyyam-nsra yayi, tare da gyara zamansa ya kalli Baba Maud’on cikin kuma jin dadi yace.
“Munyi waya dasu dazu kowa da kowa yana nan lafiya, sunma ce na gaishe da kai, saboda na tura musu hotonka, har Zaiton tana cewa wai itama zata zo ka nad’a mata irin abunda kake sawa afuskarka, wai zatana boye fuskarta saboda Samarin dake damunta.”
Yar dariya Baba Maud’o yayi, tare da jinjina kansa.
Cikin jin dadi yace.
“To shikenan Idan tazo zan koya mata yanda ake na dawa, ai rawani ne ba komai ba, nadashi kuma ba wahala.”
“To Baba Maud’o nima dai ai watarana zaka koya min ko, sai naje na koya mata.”
Kai Baba Maud’on ya jinjina alaman.
“Eh.” Daga haka kuma suka ci gaba da hiransu.
Ethiopian.
Adai-dai lokacin ne kuma Mammy dake zaune akan sallaya ta kurawa, hoton dake kan screen din wayar nata idanu, wanda kuma hoton Baba Maud’o ne da Riyyam ya turo mata.
Azahirin gaskia ba kuma tana Kallon hoton da wata manufa ko tunani bane.
Kawai dai tana mamamkin irin shigar da taga mutumin yayi ne, saboda su anan basu tab’a Ganin irin shigar ba.
Ajiye wayar nata tayi tare kuma da watsar da duk wani tunani dake ranta, kaitsaye ta mike daga kan sallayan ta shige kitchine.
Acan falo kuwa Abba dake Kallon Rayyern d’an gyara zamansa yayi.
Tare da fuskantar shi kana cikin yanayi masifa faɗa da kuma umarni yace.
“Uhmmm RAYYERN kenan.
Saboda kawai yace maka kayi aure shine kake daka masa irin wannan tsawan? Da ɗaga jijiyoyin wuya.
To shi meyene laifinsa, saboda kawai yace ka cika martabarka, ka kuma raya sunnar Annabi Muhammad SAW shine, yayi laifi?”.
Ya ƙare mgnar tare da tsareshi da idanun
Da dole yasa RAYYERN yayi ƙasa da kansa.
Shi kuwa Abba kwaffa yayi tare daci gaba da cewa.
“Yoh wai kai azatonka da tunaninka haka zaka ta zama babu aure ne, saboda kawai kaga na zuba maka ido tsawon shekaru, kayi tunani da hankalin ka fa Rayyern, ayanzu Kai ba yaro bane, Domin kuwa kabawa shekaru 30 baya, shin kana tunanin banason yin aurenka ne? Ko atunaninka bana da buk’atar Ganin aurenka ne? To kasani duk da cewar nasan tabbas na sakar maka ragaamar komai, na tara maka ayyukan da sukafi karfinka, bawai Ina nufin ka zauna haka babu aure bane ba wurin aiki kawai nake son ganin kamalarka ba harda aure, Tabbas banajin dadi aduk sanda ka nuna cewar babu maganar aure kwata-kwata agabanka, kaine babba akan Ramadan, ya kuma zama dole kayi aure, Domin duk wani Namiji mutumcinsa da Darajarsa bata cika ko a idanun mutane, har sai in yana da aure, komin dukiya da mulkinsa kuwa, aure shine abunda ke maida Rabi ya dawo Guda, ka d’aga mutumci da darajarka ta hanyar yin aure, Allah dakansa zai dubi al’amuranka, amma ace akoda yaushe Kai baka da zance sai na cewar bakason aure...”
*Albishirinku! Ma'aurata, GA GARKUWAR KU nan tafe muku da tsarabobi na musamman gareku ma'aurata daga cibiyar mgnin mata mai taken GARKUWAR MA'AURATA*
NI DAI AYSHA ALIYU GARKUWA.
Ina matukar mamakin wani irin lokaci da ya riske mu mai wahalallan fassara. Kullum dai magana daya ce, akan ma’aurata, fada, rashin jituwa, mutuwar aure, akan kuskure kalilan, rashin kula, rashin yi wa juna uziri. Toh wai duk me ya janyo hakan? Na zurfafa a tsananin tunani hakan ya tilasta min bincike mai tarin yawa wanda ya kai ni ga gano inda matsalar take? Shin yar’uwa ke macece amma kin san wacece mace ku? Kin san me ake kira mace kuwa? Mace ita ce matar da take zama iyali a wajan namiji ta zame masa bango, sanyin idaniyarsa, ta zame masa gata da farin cikin rayuwarsa ta zame masa ruwa abar kore ƙishinsa ta zame masa mayafi mai karesa daga gigitar kadaice, ta kuma dorar da mijinta kan turbar gaskiya, ta kashe masa jiki da salonta ta rikita shi da baiwa da ni’imar da Allah ya bata idan har ta san hanyar mayar da kanta sabuwa dal awajanta, wato kullun takasance masa tamkar amarya har ya kasa tantance daren amarcinsu da sauran dararen rakun rayuwar su.
Bayan Riyyam din ya fito awankane kuma, ya shirya kansa cikin shigar daya saba yi ta kananan kaya.
Wayarsa dake aje kan table ya d’auka tare da Kallon yarinyar da take kokarin saka kayanta.
Bandir din fararen y’an one one k dake hannunsa ya cilla mata.
Tare da d’alewa saman table din ya zauna, hakanan yakejin wani irin haushi, takaici, da kuma kunci acikin zuciyarsa, Yayinda yaji ko ganin yarinyar baya mason sake yi.
Sometimes kuma baisan Meyasa yakejin hakan ba, aduk lokacin da yayi sex da mace, bayan ya samu biyan bukatarsa sai yaji duk duniyar ma batayi masa dadi.
Itakuwa Yarinyar ganin da tayi mood d’insa ya sanja ne, yasa ta tattare kudin daya watso matan ta zuba acikin Jakarta.
Bayan ta gama kimtsa kanta ne kuma tayi masa sallama ta tafi.
Kamar kuwa dama jiran tafiyan nata yake, Domin tana tafiya shima ya rufe dakin.
Bayan ya bada key din a reception ne kuma, kaitsaye ya fito daga cikin hotel din.
Taxi ya tara, tare da fad’awa mai taxi din ya kaisa can cikin Nassarawa G.R.A din.
Acan b’angaren Rayyern kuwa bai baro Companyn nasu ba, har saida ya kammala duk wani abu da yakeyi.
Koda ya fito daga cikin company din kuma, kaitsaye motarsa ya shiga.
Inda suka nufo gida.
Isowarsu bakin gate din gidan kuwa, yayi dai-dai da fitowar Riyyam nsra din acikin taxi.
Ganin motar Rayyern dinne kuma yasa Riyyam sakin murmushi,
Bayan ya biya mai taxi din kudinsa ne kuma kaitsaye ya nufi cikin gidan.
Kasancewar tuni motar Rayyern din ta shige ciki.
“Baba Maud’o barka da gida.”
Riyyam din ya fad’a alokacin daya bud’e karamar kofar gate din ya shigo.
Baba Maud’o dake zaune kuwa, ganin Riyyam dinne yasa kashi sakin murmushi.
Cikin kulawa kuma yace.
“Yauwa barka dai Riyyam, tun safe yau baka zoba sai yanzu ka samu zuwa kenan.”
Kai Riyyam din ya jinjina tare da cewa.
“Eh, yau din nayi bacci sosai, kuma abokai na sun kawomin ziyara shiyasa Banzo da wuri ba.”
Kai kawai Baba Maud’on ya jinjina, Yayinda shikuwa Riyyam kaitsaye ya nufi inda motar Rayyern yake.
Yana zuwa wajen kuwa Rayyern na fitowa daga cikin motar.
K’arasowa Riyyam din yayi, cikin sauri yace. “Oyoyo Hamma Rayyern sannu da dawowa.”
Ya k’are maganan yana me rungume Rayyern din.
Rayyern kuwa zame jikinsa ya d’anyi, tare da jinjina kansa alaman yauwa.
Kamar zaice wani abu kuma sai ya fasa, kaitsaye duk suka nufi babban falon gidan.
Yayinda afakaice kuma Rayyern ke Kallon Riyyam din, Domin hakanan yaji zuciyarsa na raya masa wani abu na daban, dangane da Riyyam din musamman kamshin turaren jikinsa da yaji wanda ya tabbatar turaren matane.
Shigowarsu cikin falonne kuma yasa.
Hankalin Mamy dana Ramadan harma da Abba ya dawo kansu.
Ganin Rayyern dinne kuma yasa Abba sakin murmushi.
Yayinda Riyyam kuwa ke biye dashi abaya.
Karasowa cikin falon sukayi suka zauna.
Inda Riyyam ya durkusa har kasa ya gaishe da Abba da Mamy, fuska asake duk suka amsa masa.
Rayyern kuwa da ya Zauna akan kujeran dake gefen na Mamy.
Kallon Abban nasu yayi tare da cewa.
“Abba Mamy barka da gida.”
“yauwa Rayyern barka dai ya company’n.”
Abba ya tambaya.
“Alhamdulillah Abba komai yana tafiya dai-dai an kusa gama haɗa komai.”
Rayyern din ya fad’a yana me d’an gyara zamansa, tare kuma da sauk’e idanunsa akan, Riyyam wanda yaje ya manne da jikin Ramadan.
“Masha Allah Allah ya taimaka.”
Abba da Mamy suka hada baki wajen fad’an hakan.
“Ameen.” Ya amsa still yana mai Kallon Riyyam.
Kwarai so yake ya fahimci yaron, saboda yarda da abunda zuciyarsa ke gaya masa, yanaji ajikinsa cewar yaron kamar yana bin mata, musamman Idan akayi duba da irin rawar kan da yake dashi, ya cika rawar Kai da yawa.
Janye kansa daga Kallon Riyyam din yayi, saboda bayason yana shiga abunda bai shafesa ba.
Ramadan kuwa dake rik’e da wayarsa d’ago kansa yayi ya kalli Rayyern din.
Cikin sigar lallashi hadi da roko kuma yace.
“Yauwa Hamma Rayyern dama kai nake jira ka dawo, please Hamma Rayyern Dan Allah ka fito da mata kasamu kayi aure, kaga Abba yace bazanyi aure ba harsai kayi, ni kuma Allah yanzu aure nakeso nayi, bana son na rasa Rayhanna please Hamma na.”
ya k’are maganan yana me d’an langwab’ar da kansa gefe.
Shikuwa Rayyern d’ago kansa yayi, da kuma fuskarsa wacce ta sanja kala zuwa yanayin bacin rai.
Wani irin kallo ya watsawa Ramadan din, cikin hade fuska yace.
“Rufe min baki Ramadan kada fa ka tunzura min zuciya Kaine zaka tsaramin yanda zan tafiyar da rayuwata? Ko ka fini sanin abunda nakeyi ne, da har zaka zo kana cewa wai nayi aure! Kai ubana ne!? ko yayana!? kama fini sanin abinda ya dace kenan?.”
Rayyern din ya k’are maganan cikin fad’a.
Wanda hakan yasa Ramadan Dan sunkuyar da kansa, cikin yanayin sanyi kuma yace.
“Ayyah Hamma Rayyern kayi hakuri Insha Allah bazan sake ba kaji kayi haƙuri.”
Kai Rayyern din ya kawar, Yayinda Abba da Mamy kuwa suka kalli junansu.
Ramadan kuma mik’ewa tsaye yayi, tare da kama hannun Riyyam-nsra suka fice daga cikin falon.
Fitansu daga cikin falonne kuma yasa Abba d’ago Kai ya kalli Rayyern din.
Yayinda su Ramadan kuwa suna fita, kaitsaye wajen Baba Maud’o dake zaune abakin gate suka nufa.
Ganin su dinne kuma yasa Baba Maud’o sakin murmushi.
Bayan sun zauna akan dogon bencin da Baba Maud’on ke kaine kuma.
Baba Maud’on Ya kalli Riyyam-nsra tare cewa.
“Riyyam ya mutanen can k’asar taku, da su Mammyn ka da Zaiton.”
Murmushi Riyyam-nsra yayi, tare da gyara zamansa ya kalli Baba Maud’on cikin kuma jin dadi yace.
“Munyi waya dasu dazu kowa da kowa yana nan lafiya, sunma ce na gaishe da kai, saboda na tura musu hotonka, har Zaiton tana cewa wai itama zata zo ka nad’a mata irin abunda kake sawa afuskarka, wai zatana boye fuskarta saboda Samarin dake damunta.”
Yar dariya Baba Maud’o yayi, tare da jinjina kansa.
Cikin jin dadi yace.
“To shikenan Idan tazo zan koya mata yanda ake na dawa, ai rawani ne ba komai ba, nadashi kuma ba wahala.”
“To Baba Maud’o nima dai ai watarana zaka koya min ko, sai naje na koya mata.”
Kai Baba Maud’on ya jinjina alaman.
“Eh.” Daga haka kuma suka ci gaba da hiransu.
Ethiopian.
Adai-dai lokacin ne kuma Mammy dake zaune akan sallaya ta kurawa, hoton dake kan screen din wayar nata idanu, wanda kuma hoton Baba Maud’o ne da Riyyam ya turo mata.
Azahirin gaskia ba kuma tana Kallon hoton da wata manufa ko tunani bane.
Kawai dai tana mamamkin irin shigar da taga mutumin yayi ne, saboda su anan basu tab’a Ganin irin shigar ba.
Ajiye wayar nata tayi tare kuma da watsar da duk wani tunani dake ranta, kaitsaye ta mike daga kan sallayan ta shige kitchine.
Acan falo kuwa Abba dake Kallon Rayyern d’an gyara zamansa yayi.
Tare da fuskantar shi kana cikin yanayi masifa faɗa da kuma umarni yace.
“Uhmmm RAYYERN kenan.
Saboda kawai yace maka kayi aure shine kake daka masa irin wannan tsawan? Da ɗaga jijiyoyin wuya.
To shi meyene laifinsa, saboda kawai yace ka cika martabarka, ka kuma raya sunnar Annabi Muhammad SAW shine, yayi laifi?”.
Ya ƙare mgnar tare da tsareshi da idanun
Da dole yasa RAYYERN yayi ƙasa da kansa.
Shi kuwa Abba kwaffa yayi tare daci gaba da cewa.
“Yoh wai kai azatonka da tunaninka haka zaka ta zama babu aure ne, saboda kawai kaga na zuba maka ido tsawon shekaru, kayi tunani da hankalin ka fa Rayyern, ayanzu Kai ba yaro bane, Domin kuwa kabawa shekaru 30 baya, shin kana tunanin banason yin aurenka ne? Ko atunaninka bana da buk’atar Ganin aurenka ne? To kasani duk da cewar nasan tabbas na sakar maka ragaamar komai, na tara maka ayyukan da sukafi karfinka, bawai Ina nufin ka zauna haka babu aure bane ba wurin aiki kawai nake son ganin kamalarka ba harda aure, Tabbas banajin dadi aduk sanda ka nuna cewar babu maganar aure kwata-kwata agabanka, kaine babba akan Ramadan, ya kuma zama dole kayi aure, Domin duk wani Namiji mutumcinsa da Darajarsa bata cika ko a idanun mutane, har sai in yana da aure, komin dukiya da mulkinsa kuwa, aure shine abunda ke maida Rabi ya dawo Guda, ka d’aga mutumci da darajarka ta hanyar yin aure, Allah dakansa zai dubi al’amuranka, amma ace akoda yaushe Kai baka da zance sai na cewar bakason aure...”
*Albishirinku! Ma'aurata, GA GARKUWAR KU nan tafe muku da tsarabobi na musamman gareku ma'aurata daga cibiyar mgnin mata mai taken GARKUWAR MA'AURATA*
NI DAI AYSHA ALIYU GARKUWA.
Ina matukar mamakin wani irin lokaci da ya riske mu mai wahalallan fassara. Kullum dai magana daya ce, akan ma’aurata, fada, rashin jituwa, mutuwar aure, akan kuskure kalilan, rashin kula, rashin yi wa juna uziri. Toh wai duk me ya janyo hakan? Na zurfafa a tsananin tunani hakan ya tilasta min bincike mai tarin yawa wanda ya kai ni ga gano inda matsalar take? Shin yar’uwa ke macece amma kin san wacece mace ku? Kin san me ake kira mace kuwa? Mace ita ce matar da take zama iyali a wajan namiji ta zame masa bango, sanyin idaniyarsa, ta zame masa gata da farin cikin rayuwarsa ta zame masa ruwa abar kore ƙishinsa ta zame masa mayafi mai karesa daga gigitar kadaice, ta kuma dorar da mijinta kan turbar gaskiya, ta kashe masa jiki da salonta ta rikita shi da baiwa da ni’imar da Allah ya bata idan har ta san hanyar mayar da kanta sabuwa dal awajanta, wato kullun takasance masa tamkar amarya har ya kasa tantance daren amarcinsu da sauran dararen rakun rayuwar su.