Sashe 71
Tubali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yana shiga cikin falon ya durk’usa guiwowinsa ak’asa, tare da kai goshinsa k’asa, yayiwa Allah Sujjada, wani irin farinciki yakeji acikin zuciyarsa, bayan ya d’ago daga sujjadan ne kuma ya kalli Dr. Sajo dake kallonsa yana murmushi, cikin matukar farinciki yace.
“Alhamdulillah Allah abun godiya, doctor shawararmu tayi, komai da muka tsara ya tafi yanda ya kamata, Insha Allahu yanzu kwata-kwata ma hankalinsu bazai tab’a zuwa kaina ba.”
Murmushi Dr Sajon ya faɗada lokaci daya kuma farinciki ya bayyana akan fuskarsa.
Barrister Kabir kuwa ci gaba yayi da cewa.
“Junaid ya daure kansa da kansa, da zaluncin da yakeyi wa Jannart tsawon shekaru.
yanzu shikansa Yaya Idi bai isa yayi wani tunani akan abunda ya shafeni ba, Alhamdulillah Allah.”
Still murmushi mai kama da dariya Dr Sajon yayi, cikin kuma jin dadin labarin da Barrister Kabir din yazo masa dashi yace.
“Masha Allah Barrister Kabir, wannan abu yayi dadi, haka mukeso yanzu kaga mun dauke hankalinsu daga kan komai, zasu tsaya wa abu daya ne kawai, inda kaikuma zaka ci gaba da bincike, da kuma kara Adana hujjojinka, sannan Jannart kuma tana killace a gidan mijinta, Alhamdulillah Wannan shine matakin nasara na farko da muka fara hawa.”
Kai Barrister Kabir din ya jinjina, kana cikin gamsuwa yace.
“Insha Allah, da sannu duk wani kulli zai warware, gaskiya kuma zatayi halinta, yanzu sunacan hankalinsu duk atashe, musamman shi Yaya.”
Dariya Dr Sajo yayi, tare da gyara zamansa, cikin ya bawa shirin nasu yace.
“Aikinmu yayi kyau gaskiya, Allah kuma ya dafa mana.”
“Ameen summa Ameen.”
Barrister Kabir din ya amsa, zuciyarsa wasai babu wani alaman damuwa.
Hira suka d’an tab’a kad’n da Dr Sajon, kafun daga bisani Barrister Kabir din ya tashi ya tafi.
Acan gidansu Rayyern kuwa, kusan atare suka jero wajen shigowa cikin gidan.
Wanda kuma dawowarsu kenan daga sallan asuba.
Abba, da kuma Dr. Rayyern ne agaba, sai Ramadan da Riyyam-nsra dake take musu baya.
Ahaka suka k’araso cikin babban falon dake k’asa, tare da neman waje kowannensu ya zauna.
Mamy kuwa sanin zaman shan coffee al’adar mazan gidanne, yasa tun kafun su dawo daga masallacin ta gama had’a musu coffee wanda yaji kayan k’amshi.
Ganin shigowarsu Cikin falonne kuma yasa, Mamy daukan coffee din tare da tahowa cikin falon.
Zama tayi a tsakiyarsu
Kana ta fara tsiyayawa kowannensu a mug ta mik’a musu.
Riyyam-nsra ne ya Karb’i Mug din coffee din da Mamyn ke mik’o masa, tare da tank’washe k’afafunsa, cikin yanayin jin dadi yace.
“Mamy ngd. Da wannan al'farmar, da na samu.
Wanda yake sawa nake ga kamar ina gaban Mammy na dan itama haka takeyi min
da zaran nadawo amasallaci sai ta bamu abun tab’awa.
wannan yana d’aya daga cikin abunda yasa naji zaman gidannan yafi min na hotel.”
Dariya Mamy da Ramadan sukayi, domin hatta Abba ma saida ya dan murmusa.
Shikuwa Rayyern gaba daya ma ya dauke wuta, Yayinda ya Kawar da kansa gefe, ahankali yake sipping coffee din, ko gefen dasu Riyyam din suke kuwa bai kalla ba.
Mamy kuwa bayan ta kammala had’a musu komai ne, ta mike tare da komawa kitchine, mug din coffee din da ta had’ashi musamman dan Jannart ta d’auka, Koda ta fito daga cikin kitchine din, batare da ta tankawa su Ramadan da Riyyam dake hira ba.
kaitsaye ta wuce dakin Jannart.
Ahankali ta murd’a handle din kofar falon ta shiga, kamar kuma yanda ta tsammata hakanne ya kasance, saboda babu kowa acikin falon.
Kaitsaye kofar bedroom din ta nufa, Koda taje tsayawa tayi abakin kofar tare, da d’an k’wank’wasawa kana cikin kulawa takira sunanta.
“Jannart.”
A can cikin Bedroom kuwa.
Jannart dake zaune akan sallayan jin muryar Mamyn na kiran sunanta ne yasa ta, amsawa aladabce.
Mamy kuwa dake tsaye, jin Jannart din ta amsa ne, yasa ta tura kofar dakin ahankali ta shiga, bakinta dauke da sallama.”
Ganin Jannart din da tayi akan sallayane kuma, yasa kata sakin Murmushi, cikin kulawa tace.
“Masha Allah Jannart kin tashi ashe.”
Kai Jannart din ta jinjina alaman Eh, lokaci daya kuma tayi kasa da kanta, cikin sassanyar muryarta dake bayyana zallan ladabinta tace.
“Mamy inakwana.”
Yalwataccen murmushi Mamyn tayi, tare da cewa.
“Lafiya lau Jannart, fatan kema kintashi lafiya ya jikinki?”
Cikin jin daɗi tace.
“Da sauki sosai.”
Jannart din ta bata amsa tana medan wasa da yatsun hannunta.
“Masha Allah, haka akeso Allah ya kara sauki”.
“Amin Mamy ngd”.
Jannart ta kuma faɗa.
Ita kuwa Mamy murmushin jin daɗi tayi tare da cewa.
“Ga coffee nan mai zafi maza ki shanye shi.
zakiji d’umi cikinki zai ware.”
Mamyn ta fad’a tana me ajiye mata mug din Coffee din.
“Toh Mamy Nagode.”
Still Jannart din ta fada tana mekokarin gyara zamanta.
Mamy kuwa murmushi tayi tare da cewa.
“Ba komai Jannart, ki saki jikinki, Idan kinsha coffee din kuma zaki iya komawa bacci, ki dai samu ki huta kinji ko.”
Kai Jannart din ta jinjina, inda Mamyn kuwa cike da kauna, hadi da yaba hankalin yarinyar ta juya ta fita.
Ganin fitar Mamyn ne kuma yasa, Jannart daukan coffee din ahankali ta soma sha, saboda dadin da coffee din yayi ne kuma yasa harta shanye feye da rabinshi, batare da ta farga ba cin cikinta yayi dumine kuma yasa aje sauran.
Alhamdulillah kuma ta danji karfi ajikinta.
Mamy kuwa tana fita daga dakin Jannart din, direct kitchine ta sake wucewa.
Dan soma shirin aikin breakfast.
Yayinda kuma har yanzu Ramadan da Riyyam ke zaune acikin falon suna tad’i.
Kasancewar tuntuni Rayyern ya tashi ya haura sama, Koda yaje dakin nasa ma kuma kwanciyaya yayi, saboda gaba daya Daren jiya baiwani samu isashshen bacci ba.
Cikin sa’a kuwa Yana kwanciya bacci ya d’aukesa.
7:30 pm dai-dai.
Mamyn ta kammala had’a duk wani abu da takeyi.
Ita da Riyyam ne kuma suka jere duk abincin akan dining table, Yayinda Abba da kuma Ramadan ke zaune acikin falon.
“Bismillah komai ya zama ready, Ina Rayyern bai sauk’o ba ko.”
Mamy ta fad’a adai-dai lokacin da take ajiye plate plates na cin abincin.
Jin abunda ta fad’ane kuma yasa Abba dake zaune yana karatun Alqur'ani juyowa ya kalleta, cikin tausasa harshe yace.
“Masha Allah, amma nikam daga yau na daina cin abinci acikin ku.
ana shiryamin nawa Acan dining table dina”
Murmushi Mamy tayi, cikin gamsuwa da kuma fahimta mijin nata tace.
“To shikenan Ranka ya dad’e Insha Allah, naka shirin ma na musamman zanna maka.”
Yar dariya sukayi, Yayinda Riyyam-nsra kuwa Kallon Abban yayi, cikin nishadi Yace.
“Abba Kai bazakayi irin na turawa bane.”
Murmushi Abban yayi, tare da girgiza kansa yace.
“To ni ai ba bature bane Riyyam.”
Kai Riyyam ya jinjina aransa yana mejin dadi, saboda akaron farko kenan da yaga Abban yayi masa murmushi, tabbas yaji dadin abun.
Mamy kuwa cewa tayi, Ramadan da Riyyam duk su taso suzo suci abinci.
Aikuwa dama kaman jira suke, zama sukayi akan dining table din, Yayinda Mamy da kanta tayi saving dinsu, kana Itama tayi saving din kanta.
Abba kuwa har yanzu yana nan zaune acikin falon.
Suna cikin cin abincinne kuma Mamy ta d’an d’ago Kai ta kalli Abban.
Cikin tausasa muryarta irin na mata masu ladabi ga mazajensu tace.
“Yauwa Alhaji, yarinyar nan Jannart kaga irin yanayin yanda tazo gidannan, komai anyisa ne asace a boye.
Hakan yasa batazo da suturun sawa ba, sai nake ganin maizai hana, Indai babu matsala a fita aje asamomata suturun sawa.”
Kai Abban ya jinjina cike da gamsuwar abunda Mamyn ta fad’a yace.
“Tabbas ya kamata kam asamomata kayan sawa, tun dai ayanzu kam duk wani hakkinta ci da shanta da sutura jinya yana wuyan Mijinta ne, saboda haka ku tambayesa ya bada kudi, Idan yaso sai kije kiyi mata duk wata sayayya da ta dace.”
Kai Mamy ta jinjina, cikin kuma yin kasa da murya da alaman ladabi tace.
“Mijinta kuwa?”
“K’warai kuwa shid’in dai, ai yanzu duk wani nauyinta ya rataya ne akan wuyansa ne.
Hakkinsa ne dole kuma shi zai sauke dan haka ya fara da wurima.”
Kai Mamyn ta jinjina, kana a gamsashe tace.
“To shikenan Insha Allah zanyi masa magana.”
Daga haka kuwa babu wanda ya sake cewa komai, suka ci gaba da cin abincinsu.
Bayan sun kammala ne cin abincinnasu ne kuma suka dawo cikin falon.
Mamy kuwa Ganin lokaci ya danja sosai ne, yasa ta kalli Ramadan, kana cikin kulawa tace.
“Ramadan jeka kiramin Hammanku, gashi har kusan goma ko breakfast bai sauk’o yayi ba.”
“To.” Ramadan yace tare kuma da mik’ewa ya haura sama, Koda ya k’arasa d’akin Rayyern d’in, samunsa yayi acikin blanket yana ta bacci.
Batare daya tashesa ba kuma ya juyo, tare da dawowa falon.
Tun kafun ya zauna kuma ya kalli Mamyn tare da cewa.
“Mamy Hamma Rayyern fa bacci yakeyi, ni kuma gaskiya tsoron tashinsa nake kada na tashesa kuma ya hauni da fad’a.”
D’an Jim Mamyn tayi, tare da mik’ewa tsaye tace.
“Shikenan badamuwa bari na fad’awa Abban ku.”
Kaitsaye falon Abban ta wuce.
Koda taje zaune tasa meshi, zama tayi ad’an gefensa kana cikin tausasa Murya tace.
“Natura Ramadan ya kira Rayyern, amma yace bacci yake har yanzu bai tashi ba, ka kumasan Rayyern kwata kwata baya so atashesa Idan yana bacci kasan matsalar ciwon kansa.”
Kai Abban ya girgiza bayan ya tankwashe kafafunsa ne kuma ya d’ago da kansa ya kalli Mamyn, cikin bada umarni kuma yace.
“Yau dai kam atashesa daga baccin da yakeyi, saboda yana da kyau yasan cewar yanzu bawai lokacin kansa kawai yake dashi ba.
Yana da lokaci wata, maza ki tura Ramadan ya taso sa.”
Kai Mamyn ta jinjina, cikin Dan ladabtar da murya tace.
“Ramadan yace yana jin tsoron tashin sa, kada Yayi masa fad’a”
“To ke kije ki tasosa.”
Abban ya fad’a kaitsaye.
Jin hakanne kuma yasa Mamy yin shiru, saboda tasani Sam Rayyern bayaso Idan yana bacci azo atashesa any how, musamman kuma kasancewar yana da matsalan ciwon Kai, shiyasa Mamyn ma take gudun yin duk wani abu dazai takurasa, domin tun yana karaminsa, Idan yana bacci bata cika son tashinsa, saidai idan ya gaji ya tashi dan kansa.
Fahimtar hakanne kuma yasa Abba mik’ewa tsaye, tare da cewa.
“To ni bari naje na tasosa da kaina.”
Hakan kuwa akayi inda kaitsaye ya nufi sama, nan sashin Rayyern din.
Yana zuwa kuwa ya tura kofar dakin ya shiga.
“Alhamdulillah Allah abun godiya, doctor shawararmu tayi, komai da muka tsara ya tafi yanda ya kamata, Insha Allahu yanzu kwata-kwata ma hankalinsu bazai tab’a zuwa kaina ba.”
Murmushi Dr Sajon ya faɗada lokaci daya kuma farinciki ya bayyana akan fuskarsa.
Barrister Kabir kuwa ci gaba yayi da cewa.
“Junaid ya daure kansa da kansa, da zaluncin da yakeyi wa Jannart tsawon shekaru.
yanzu shikansa Yaya Idi bai isa yayi wani tunani akan abunda ya shafeni ba, Alhamdulillah Allah.”
Still murmushi mai kama da dariya Dr Sajon yayi, cikin kuma jin dadin labarin da Barrister Kabir din yazo masa dashi yace.
“Masha Allah Barrister Kabir, wannan abu yayi dadi, haka mukeso yanzu kaga mun dauke hankalinsu daga kan komai, zasu tsaya wa abu daya ne kawai, inda kaikuma zaka ci gaba da bincike, da kuma kara Adana hujjojinka, sannan Jannart kuma tana killace a gidan mijinta, Alhamdulillah Wannan shine matakin nasara na farko da muka fara hawa.”
Kai Barrister Kabir din ya jinjina, kana cikin gamsuwa yace.
“Insha Allah, da sannu duk wani kulli zai warware, gaskiya kuma zatayi halinta, yanzu sunacan hankalinsu duk atashe, musamman shi Yaya.”
Dariya Dr Sajo yayi, tare da gyara zamansa, cikin ya bawa shirin nasu yace.
“Aikinmu yayi kyau gaskiya, Allah kuma ya dafa mana.”
“Ameen summa Ameen.”
Barrister Kabir din ya amsa, zuciyarsa wasai babu wani alaman damuwa.
Hira suka d’an tab’a kad’n da Dr Sajon, kafun daga bisani Barrister Kabir din ya tashi ya tafi.
Acan gidansu Rayyern kuwa, kusan atare suka jero wajen shigowa cikin gidan.
Wanda kuma dawowarsu kenan daga sallan asuba.
Abba, da kuma Dr. Rayyern ne agaba, sai Ramadan da Riyyam-nsra dake take musu baya.
Ahaka suka k’araso cikin babban falon dake k’asa, tare da neman waje kowannensu ya zauna.
Mamy kuwa sanin zaman shan coffee al’adar mazan gidanne, yasa tun kafun su dawo daga masallacin ta gama had’a musu coffee wanda yaji kayan k’amshi.
Ganin shigowarsu Cikin falonne kuma yasa, Mamy daukan coffee din tare da tahowa cikin falon.
Zama tayi a tsakiyarsu
Kana ta fara tsiyayawa kowannensu a mug ta mik’a musu.
Riyyam-nsra ne ya Karb’i Mug din coffee din da Mamyn ke mik’o masa, tare da tank’washe k’afafunsa, cikin yanayin jin dadi yace.
“Mamy ngd. Da wannan al'farmar, da na samu.
Wanda yake sawa nake ga kamar ina gaban Mammy na dan itama haka takeyi min
da zaran nadawo amasallaci sai ta bamu abun tab’awa.
wannan yana d’aya daga cikin abunda yasa naji zaman gidannan yafi min na hotel.”
Dariya Mamy da Ramadan sukayi, domin hatta Abba ma saida ya dan murmusa.
Shikuwa Rayyern gaba daya ma ya dauke wuta, Yayinda ya Kawar da kansa gefe, ahankali yake sipping coffee din, ko gefen dasu Riyyam din suke kuwa bai kalla ba.
Mamy kuwa bayan ta kammala had’a musu komai ne, ta mike tare da komawa kitchine, mug din coffee din da ta had’ashi musamman dan Jannart ta d’auka, Koda ta fito daga cikin kitchine din, batare da ta tankawa su Ramadan da Riyyam dake hira ba.
kaitsaye ta wuce dakin Jannart.
Ahankali ta murd’a handle din kofar falon ta shiga, kamar kuma yanda ta tsammata hakanne ya kasance, saboda babu kowa acikin falon.
Kaitsaye kofar bedroom din ta nufa, Koda taje tsayawa tayi abakin kofar tare, da d’an k’wank’wasawa kana cikin kulawa takira sunanta.
“Jannart.”
A can cikin Bedroom kuwa.
Jannart dake zaune akan sallayan jin muryar Mamyn na kiran sunanta ne yasa ta, amsawa aladabce.
Mamy kuwa dake tsaye, jin Jannart din ta amsa ne, yasa ta tura kofar dakin ahankali ta shiga, bakinta dauke da sallama.”
Ganin Jannart din da tayi akan sallayane kuma, yasa kata sakin Murmushi, cikin kulawa tace.
“Masha Allah Jannart kin tashi ashe.”
Kai Jannart din ta jinjina alaman Eh, lokaci daya kuma tayi kasa da kanta, cikin sassanyar muryarta dake bayyana zallan ladabinta tace.
“Mamy inakwana.”
Yalwataccen murmushi Mamyn tayi, tare da cewa.
“Lafiya lau Jannart, fatan kema kintashi lafiya ya jikinki?”
Cikin jin daɗi tace.
“Da sauki sosai.”
Jannart din ta bata amsa tana medan wasa da yatsun hannunta.
“Masha Allah, haka akeso Allah ya kara sauki”.
“Amin Mamy ngd”.
Jannart ta kuma faɗa.
Ita kuwa Mamy murmushin jin daɗi tayi tare da cewa.
“Ga coffee nan mai zafi maza ki shanye shi.
zakiji d’umi cikinki zai ware.”
Mamyn ta fad’a tana me ajiye mata mug din Coffee din.
“Toh Mamy Nagode.”
Still Jannart din ta fada tana mekokarin gyara zamanta.
Mamy kuwa murmushi tayi tare da cewa.
“Ba komai Jannart, ki saki jikinki, Idan kinsha coffee din kuma zaki iya komawa bacci, ki dai samu ki huta kinji ko.”
Kai Jannart din ta jinjina, inda Mamyn kuwa cike da kauna, hadi da yaba hankalin yarinyar ta juya ta fita.
Ganin fitar Mamyn ne kuma yasa, Jannart daukan coffee din ahankali ta soma sha, saboda dadin da coffee din yayi ne kuma yasa harta shanye feye da rabinshi, batare da ta farga ba cin cikinta yayi dumine kuma yasa aje sauran.
Alhamdulillah kuma ta danji karfi ajikinta.
Mamy kuwa tana fita daga dakin Jannart din, direct kitchine ta sake wucewa.
Dan soma shirin aikin breakfast.
Yayinda kuma har yanzu Ramadan da Riyyam ke zaune acikin falon suna tad’i.
Kasancewar tuntuni Rayyern ya tashi ya haura sama, Koda yaje dakin nasa ma kuma kwanciyaya yayi, saboda gaba daya Daren jiya baiwani samu isashshen bacci ba.
Cikin sa’a kuwa Yana kwanciya bacci ya d’aukesa.
7:30 pm dai-dai.
Mamyn ta kammala had’a duk wani abu da takeyi.
Ita da Riyyam ne kuma suka jere duk abincin akan dining table, Yayinda Abba da kuma Ramadan ke zaune acikin falon.
“Bismillah komai ya zama ready, Ina Rayyern bai sauk’o ba ko.”
Mamy ta fad’a adai-dai lokacin da take ajiye plate plates na cin abincin.
Jin abunda ta fad’ane kuma yasa Abba dake zaune yana karatun Alqur'ani juyowa ya kalleta, cikin tausasa harshe yace.
“Masha Allah, amma nikam daga yau na daina cin abinci acikin ku.
ana shiryamin nawa Acan dining table dina”
Murmushi Mamy tayi, cikin gamsuwa da kuma fahimta mijin nata tace.
“To shikenan Ranka ya dad’e Insha Allah, naka shirin ma na musamman zanna maka.”
Yar dariya sukayi, Yayinda Riyyam-nsra kuwa Kallon Abban yayi, cikin nishadi Yace.
“Abba Kai bazakayi irin na turawa bane.”
Murmushi Abban yayi, tare da girgiza kansa yace.
“To ni ai ba bature bane Riyyam.”
Kai Riyyam ya jinjina aransa yana mejin dadi, saboda akaron farko kenan da yaga Abban yayi masa murmushi, tabbas yaji dadin abun.
Mamy kuwa cewa tayi, Ramadan da Riyyam duk su taso suzo suci abinci.
Aikuwa dama kaman jira suke, zama sukayi akan dining table din, Yayinda Mamy da kanta tayi saving dinsu, kana Itama tayi saving din kanta.
Abba kuwa har yanzu yana nan zaune acikin falon.
Suna cikin cin abincinne kuma Mamy ta d’an d’ago Kai ta kalli Abban.
Cikin tausasa muryarta irin na mata masu ladabi ga mazajensu tace.
“Yauwa Alhaji, yarinyar nan Jannart kaga irin yanayin yanda tazo gidannan, komai anyisa ne asace a boye.
Hakan yasa batazo da suturun sawa ba, sai nake ganin maizai hana, Indai babu matsala a fita aje asamomata suturun sawa.”
Kai Abban ya jinjina cike da gamsuwar abunda Mamyn ta fad’a yace.
“Tabbas ya kamata kam asamomata kayan sawa, tun dai ayanzu kam duk wani hakkinta ci da shanta da sutura jinya yana wuyan Mijinta ne, saboda haka ku tambayesa ya bada kudi, Idan yaso sai kije kiyi mata duk wata sayayya da ta dace.”
Kai Mamy ta jinjina, cikin kuma yin kasa da murya da alaman ladabi tace.
“Mijinta kuwa?”
“K’warai kuwa shid’in dai, ai yanzu duk wani nauyinta ya rataya ne akan wuyansa ne.
Hakkinsa ne dole kuma shi zai sauke dan haka ya fara da wurima.”
Kai Mamyn ta jinjina, kana a gamsashe tace.
“To shikenan Insha Allah zanyi masa magana.”
Daga haka kuwa babu wanda ya sake cewa komai, suka ci gaba da cin abincinsu.
Bayan sun kammala ne cin abincinnasu ne kuma suka dawo cikin falon.
Mamy kuwa Ganin lokaci ya danja sosai ne, yasa ta kalli Ramadan, kana cikin kulawa tace.
“Ramadan jeka kiramin Hammanku, gashi har kusan goma ko breakfast bai sauk’o yayi ba.”
“To.” Ramadan yace tare kuma da mik’ewa ya haura sama, Koda ya k’arasa d’akin Rayyern d’in, samunsa yayi acikin blanket yana ta bacci.
Batare daya tashesa ba kuma ya juyo, tare da dawowa falon.
Tun kafun ya zauna kuma ya kalli Mamyn tare da cewa.
“Mamy Hamma Rayyern fa bacci yakeyi, ni kuma gaskiya tsoron tashinsa nake kada na tashesa kuma ya hauni da fad’a.”
D’an Jim Mamyn tayi, tare da mik’ewa tsaye tace.
“Shikenan badamuwa bari na fad’awa Abban ku.”
Kaitsaye falon Abban ta wuce.
Koda taje zaune tasa meshi, zama tayi ad’an gefensa kana cikin tausasa Murya tace.
“Natura Ramadan ya kira Rayyern, amma yace bacci yake har yanzu bai tashi ba, ka kumasan Rayyern kwata kwata baya so atashesa Idan yana bacci kasan matsalar ciwon kansa.”
Kai Abban ya girgiza bayan ya tankwashe kafafunsa ne kuma ya d’ago da kansa ya kalli Mamyn, cikin bada umarni kuma yace.
“Yau dai kam atashesa daga baccin da yakeyi, saboda yana da kyau yasan cewar yanzu bawai lokacin kansa kawai yake dashi ba.
Yana da lokaci wata, maza ki tura Ramadan ya taso sa.”
Kai Mamyn ta jinjina, cikin Dan ladabtar da murya tace.
“Ramadan yace yana jin tsoron tashin sa, kada Yayi masa fad’a”
“To ke kije ki tasosa.”
Abban ya fad’a kaitsaye.
Jin hakanne kuma yasa Mamy yin shiru, saboda tasani Sam Rayyern bayaso Idan yana bacci azo atashesa any how, musamman kuma kasancewar yana da matsalan ciwon Kai, shiyasa Mamyn ma take gudun yin duk wani abu dazai takurasa, domin tun yana karaminsa, Idan yana bacci bata cika son tashinsa, saidai idan ya gaji ya tashi dan kansa.
Fahimtar hakanne kuma yasa Abba mik’ewa tsaye, tare da cewa.
“To ni bari naje na tasosa da kaina.”
Hakan kuwa akayi inda kaitsaye ya nufi sama, nan sashin Rayyern din.
Yana zuwa kuwa ya tura kofar dakin ya shiga.