Sashe 26
Tubali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Zaku iya samun kayyakina a duk garin da kike, zakiyi min mgn ta whatsApp number na 09097853276 domin yin zaɓinki, ko karin bayani, zaki tura kuɗin ta account na 0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU in mun gama mgna zan sa miki kaya a mota yazo duk garin da kike, in baki shirya saya yanzuba Please kada mu wahal da juna ki bari sai kin shirya kafin kiyi min mgn.
🤝🏻🥰😘 Daga taku AYSHA ALIYU GARKUWA
*(GARKUWAR MA'AURATA)*
Sautin takun takalminsa dasu Ramadan sukaji ne kuma yasa su maida hankali zuwa gareshi.
Idanunsu gaba daya suka zuba mishi, tare da had’a baki gaba dayansu suka ce.
“Masha Allah! Tsarki ya tabbata ga sarkin daya halicce mu ya kuma halicci Hamman Rayyern dinmu.”
“Innalillahi kai Hamma Rayyern kayi kyau sosai, wallahi kamar daga Saudiya kazo.”
Cewar Riyyam-nsra daya hangame baki da hanci yana Kallon Rayyern d’in.
Shikuwa Rayyern karasa saukowa cikin falon, yayi ganin Abba da Mamy zaune ne kuma yasashi, d’an rusunawa ahankali yace.
“Mammy a bani Bootle water mai sanyi.”
Mamy da ita kanta ta yaba da tsananin kyawun da al'kyabban jikin nasa tayi masa ne ta saki murmushi, tare da fadin.
“Masha Allah Rayyern kayi kyau, wannan suturar tayi maka kyau, Lallai kuwa ashe Rayyern din nawa ya kerewa sa’a.”
Ɗan guntun Murmushin yayi, Cikin kuma alaman jin kunyar yabonsa da Mamyn nasa tayi yace.
“Nagode sosae Mamyna.”
Abba daya kafe Rayyern din da ido kuwa baya ko k’yaftawa, fuskarsa cike da mamaki yace.
“Rayyern wannan shigar fa yaushe ka fara ta? sannan a ina ka samo alkyabba mai tsananin kyau haka?”
D’an sunkuyar da kansa k’asa yayi, tare da kama y’an yatsun hannunsa ya soma murzawa.
Sam arayuwarsa shi bai iya k’arya ba, impact ma arayuwarsa babu abunda yafi tsana kamar k’arya, bayayin k’arya bakuma yaso ayi masa.
Duk da kuwa yasan Abban nasu bazai so abunba so gskyar da zai fada ba, amma ya zama dole ya gaya masa gaskiya, saboda karya ba d’abi’arsa bace.
“Kayi hakuri Abba Malam Mai-nasara ne ya bani kyautan Alkyabbu guda bakwai.”
Idanu Abba ya kankance cikin kuma nuna rashin jin dadin hakan ya kawar da kansa gefe.
Ganin hakanne kuma yasa Rayyern d’in, ya d’an rank’wafar da kansa.
Kana cikin sigar ban baki yace.
“Kayi hakuri Abba, idan bakason shigartawa sainaje na cire.”
Ajiyar zuciya Abban ya sauk’e kana ahankali yace.
“A’a ni Bance Banason shigarka ba, kayi kyau Tabbas kuma shigar alkyabba shigace da take da matuk’ar mutumci, gashi kuma ta bayyana tsananin haiba da kwarjininka, saidai amma ka kiyaye nan gaba bafa na son wata alaƙa a tsakaninku.”
Kai Rayyern din ya jinjina kana cikin girmama zancen Abban nasu yace.
“Nagode Abba kuma Insha Allah zan kiyaye.”
“Shikenan.” Abban ya fad’a atakaice.
Riyyam-nsra kuwa cikin kasa kosawa da Kallon yanda Hamadan nasu yayi kyau yace.
“Please Hamma Rayyern Ina zakaje.”
“Polo.”
Ya bawa Riyyam din amsa a taƙaice kuma dai-dai lokacin da yake kokarin fita daga falon.
Da sauri Riyyam din ya tashi yabi bayansa, yana me fad’in.
“To Hamma Rayyern tsaya muyi video dan Allah.”
Ramadan dake zaune ma mik’ewa tsaye yayi yabi bayansu.
A compound din gidan suka tsaya, inda Riyyam sarkin tiktok ya saita wayarsa ya soma yi musu video dukansu uku.
Harda sa musu wata y’ar wak’a, shidai Rayyern Kallon Yaron kawai yakeyi, domin a wuni biyu kawai da sukayi da yaron, ya fahimci wani abu, da kuma irin d’abi’a da yaron yayi shura akai.
Saidai kuma baisan Meyasa ba yakejin yaron acikin zuciyarsa hakan yasa yake kasa yakiceshi.
Gama k’arasowarsu compound din gidan kuwa, yayi dai-dai da fitowan Baba Maud’o daga cikin d’an madaidacin Part ɗinsa dake gefen gate.
Yana fitowa dinne kuma ya sauk’e idanunsa akan Rayyern, dake sanye cikin al-kyabba.
Wani irin tsayuwa Baba Maud’on yaji zuciyarsa tayi, take kuma wasu irin abubuwa suka shiga dawowa cikin tunaninsa.
Saidai kuma Ina ayanzu kwakwalwarsa bata da wani buk’atar amsar kowani irin sak’o, wannan dalilin yasa zuciyarsa ke cigaba da bugawa da harbawa a hankali.
D’an matsowa kusa dasu Baba Maud’on yayi, tare kuma da sauk’e idanunsa akan Riyyam wanda keta faman bin wak’ar Justin Bieber me suna (Peaches) dake tashi awayarsa.
Idanu Baba Maud’o ya tsurawa yaron baya ko k’iftawa, Yayinda zuciyarsa ke cike da zallan mamakin, kamannin Rayyern dake kwance akan fuskar yaron.
“Baba Maud’o barka da yammaci.”
Cewar Rayyern.
Wanda maganan nasa ne kuma yasa Baba Maud’o dawowa cikin tunaninsa.
Murmushi ne ya bayyana akan fuskarsa, duk da kuwa cewar rabin fuskartasa arufe take, amma hakan bai hana Rayyern din gane cewar Baba Maud’on murmushi yayi ba.
“Yauwa Barka dai Rayyern, yau kuma inazaka je haka naga kayi shigar da ta bayyana kyau da cikar haibarka.”
Murmushi Rayyern din yayi, tare da dan matsowa kusa da Baba Maud’on kana yace.
“Wurin wasan polo zanje Baba Maud’o".
Kai ya jinjina alamun gamsuwa.
"Shin ko akwai wasu abubuwan buk’ata naka da suka k’are, idan nazo dawowa saina sayo maka.”
Rayyern ya tambayeshi cikin mutunta ma'aikatan gidan nasu.
Again Murmushi Baba Maud’o yayi, cikin kuma Jin dadin kulawan da su Rayyern din sukeyi dashi yace.
“A’a Alhamdulillah ayanzu kam bana buk’atar komai, saidai nace kayi kyau sosai cikin wannan shigar, amma baka daura hiramin naka dai-dai ba, Bari na gyarama irin yanda samarin makka suke saka nasu.”
Murmushi Rayyern din yayi, kana ya matso Baba Maud’o d’in ya gyara masa sakun hiramin.
Riyyam-nsra kuwa da d’an mamaki ya kalli Hamma Rayyern dinnasu, tare da cewa.
“Hamma Rayyern waye wannan mutumin, naga jiya da nazo banganshi ba.”
“Sunansa Baba Maud’o.”
Ramadam ya bashi amsa.
Saurin jinjina Kai Riyyam yayi, kana ahankali ya matso kusa da Baba Maud’o din.
Fuskarsa dauke da murmushi yace.
“Rawanin da kasa akanka zuwa fuskarka yayi kyau sosai Baba Maud’o, Dan Allah Hamma Rayyern kuzo mu d’auki hoton selfie tare dashi, saboda Idan na koma Ethiopia zan nunawa Mammyna, na kuma bata labarin yanda wasu daga cikin yan Nigeria sukeyin shigarsu.”
Ya fad’i hakan saboda baisan cewa Baba Maud’o’n shigar buzayen Niger 🇳🇪 yayi ba.
Kamar yanda ya buk’ata kuwa matsowa Rayyern da Ramadan sukayi, inda suka saka Baba Maud’o da Riyyam din atsakiya.
Hakanne kuwa yasa Baba Maud’o da Riyyam din ke iya jiyo sautin bugun zuciyar kowannensu, saboda yanayin yanda sukayi kusan ci sosai da juna, domin Riyyam dan sarkin son jiki, har rungume Baba Maud’on yayi ajikinsa.
Yayinda Ramadan ya karb’i wayar Riyyam d’in, yayi musu hoton selfie har kala biyu.
Bayan ya mikawa Riyyam din wayarsa ne kuma,
Rayyern ya juya ya shiga motarsa, driver’nsa yaja suka fice daga cikin gidan.
Ramadan da Riyyam kuwa zama sukayi dab’as Akan wani dan dogon Bencin da Baba Maud’o ke zama, haka kuwa suka sa Baba Maud’on agaba sunata hira, musamman Riyyam daya bud’e baki ya dinga shararawa Baba Maud’on labarai kala-kala, wanda duk rabinsu na abun dariya ne.
*Arewa 24 TV*
Jannart ne da Salman ke tafe acikin babban corridor din, da zai sadasu da compound din gidan tv'n nasu.
Anutse Jannart take takunta, Yayinda time to time take Kallon fuskar wayarta dake rike ahannunta.
Salman dake biye da ita kuwa, idan hankalinsa yakai dubu to duk akanta yake.
Baisan meyasaba hardai idan Jannart tana waje, baya tab’a iya dauke kansa daga gareta, koda kuwa yaya baya iya gajiya da Kallon tafiyarta mai kama data hawainiya.
Yayi Imani azuciyarsa cewa Jannart macece ta gasken gaske, ko acikin mata irinta basu da yawa.
Isowarsu jikin motarsa ne kuma yasa Jannart fakon idanun guard dinta ta shige cikin motar, kana cikin sauri tace.
“Please Salman kayi sauri mubar nan, Domin idan wayannan kattin suka ganni dakai ina mai tabbatar maka cewar akwai matsala.”
“Nikuwa nasan da cewar akwai matsala ai Jannart, abu mai sauki ne ma su samin bindiga akaina su harbeni, tsoron da ake baki agidanku ko Gwamna iyakaci.”
Salman din ya fada adaidai lokacin da yake ta da motar suka bar wajen.
Suna hawa titi kuwa Jannart ta sauk’e ajiyar zuciya tare da fad’in.
“Allah Yasa dai mudace mu samu ganinsa yau, amma mutum dan ya zama richest man shikenan kuma ganinsa saiya zama wahala.”
Shidai Salman murmushi kawai yayi kaman zaice wani abu kuma saiya fasa.
Kaitsaye suka nufi Mai-nasara Hospital.
Tafiyar mintuna kad’anne ya kawosu bakin kofar katafaren asibitin.
Kasancewar kuma ba ashiga can Cikin hospital din da mota, matuk’ar ba emergency bane, yasa Salman parking motar anan babban parking lot na asibitin, wanda shi kansa ya kusan kwatan wata karamar unguwa.
Bud’e murfin motar Jannart tayi ta fito, tana me k’arewa kyau da had’uwar asibitin kallo.
Lallai privet Hospital ne daya amsa sunansa, saboda daga ginin asibitin ma kasan ba kananan billions aka kashe masa ba.
“Mai-nasara Hospital! Lallai asibitin ya had’u.”
Jannart din ta fad’a tana me Kallon Salman.
Shima Salman din kallonta yayi, tare da cewa.
“To Kema da bakinki kin fad’a, yanzu kiyi imagine tayaya za ace kinsamu ganin mamallakin wannan wajen acikin sauki? karki manta kuma bawai iya Hospital dinnan ya mallaka ba, yana da companies, bama a iya Nigeria ba, wallahi Jannart wannan mutumin *Richest Man* ne na k’arshe.”
Kai Jannart d’in ta jinjina, domin ita kanta ayanzu ta yarda da hakan.
Kaitsaye kuma suka kutsa cikin asibitin.
Acan b’angaren Rayyern kuwa kaitsaye Wajen buga wasan polo suka nufa.
Koda suka isa wajen da haduwarsa da kuma kyawunsa ya darawa kwatance.
A parking lot driver’nsa yayi parking.
Bayan ya fito daga motar nasa ne kuma kaitsaye ya nufi cikin wajen.
Da kwata-kwata babu mutane acikinsa.
Duk da tsananin girman wajen kuwa, amma bakajin motsin komai saina tarin dawakai da kuma tsirarun masu kula dasu.
Wanda kuma hakan ya faru ne saboda zuwan Dr.Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara, kasancewar idan har zaizo wajen To yakan biya mak’udan kud’ad’e ne, ta yanda ranar baza'a amshi kuɗin wasuba, harsai yayi wasansa ya gama ak’alla na tsawon awa 2, bayan ya tafi ne kuma sauran jama’a zasu dawo su cigaba da harkokinsu bawai kuma yana haka dan isa bane, sai dan sosai hayani kan iya sa mishi ciwon kai, yana kuma jin daɗi wasan polo a jikinsa.
Shigarsa cikin babban wajen wasan buga Polo dinne kuma yasashi, zare alkyabban dake jikinsa ya ajiye, tare da wayoyinsa harma da y’ar bag din da yasaka bottle water mai sanyi aciki.
🤝🏻🥰😘 Daga taku AYSHA ALIYU GARKUWA
*(GARKUWAR MA'AURATA)*
Sautin takun takalminsa dasu Ramadan sukaji ne kuma yasa su maida hankali zuwa gareshi.
Idanunsu gaba daya suka zuba mishi, tare da had’a baki gaba dayansu suka ce.
“Masha Allah! Tsarki ya tabbata ga sarkin daya halicce mu ya kuma halicci Hamman Rayyern dinmu.”
“Innalillahi kai Hamma Rayyern kayi kyau sosai, wallahi kamar daga Saudiya kazo.”
Cewar Riyyam-nsra daya hangame baki da hanci yana Kallon Rayyern d’in.
Shikuwa Rayyern karasa saukowa cikin falon, yayi ganin Abba da Mamy zaune ne kuma yasashi, d’an rusunawa ahankali yace.
“Mammy a bani Bootle water mai sanyi.”
Mamy da ita kanta ta yaba da tsananin kyawun da al'kyabban jikin nasa tayi masa ne ta saki murmushi, tare da fadin.
“Masha Allah Rayyern kayi kyau, wannan suturar tayi maka kyau, Lallai kuwa ashe Rayyern din nawa ya kerewa sa’a.”
Ɗan guntun Murmushin yayi, Cikin kuma alaman jin kunyar yabonsa da Mamyn nasa tayi yace.
“Nagode sosae Mamyna.”
Abba daya kafe Rayyern din da ido kuwa baya ko k’yaftawa, fuskarsa cike da mamaki yace.
“Rayyern wannan shigar fa yaushe ka fara ta? sannan a ina ka samo alkyabba mai tsananin kyau haka?”
D’an sunkuyar da kansa k’asa yayi, tare da kama y’an yatsun hannunsa ya soma murzawa.
Sam arayuwarsa shi bai iya k’arya ba, impact ma arayuwarsa babu abunda yafi tsana kamar k’arya, bayayin k’arya bakuma yaso ayi masa.
Duk da kuwa yasan Abban nasu bazai so abunba so gskyar da zai fada ba, amma ya zama dole ya gaya masa gaskiya, saboda karya ba d’abi’arsa bace.
“Kayi hakuri Abba Malam Mai-nasara ne ya bani kyautan Alkyabbu guda bakwai.”
Idanu Abba ya kankance cikin kuma nuna rashin jin dadin hakan ya kawar da kansa gefe.
Ganin hakanne kuma yasa Rayyern d’in, ya d’an rank’wafar da kansa.
Kana cikin sigar ban baki yace.
“Kayi hakuri Abba, idan bakason shigartawa sainaje na cire.”
Ajiyar zuciya Abban ya sauk’e kana ahankali yace.
“A’a ni Bance Banason shigarka ba, kayi kyau Tabbas kuma shigar alkyabba shigace da take da matuk’ar mutumci, gashi kuma ta bayyana tsananin haiba da kwarjininka, saidai amma ka kiyaye nan gaba bafa na son wata alaƙa a tsakaninku.”
Kai Rayyern din ya jinjina kana cikin girmama zancen Abban nasu yace.
“Nagode Abba kuma Insha Allah zan kiyaye.”
“Shikenan.” Abban ya fad’a atakaice.
Riyyam-nsra kuwa cikin kasa kosawa da Kallon yanda Hamadan nasu yayi kyau yace.
“Please Hamma Rayyern Ina zakaje.”
“Polo.”
Ya bawa Riyyam din amsa a taƙaice kuma dai-dai lokacin da yake kokarin fita daga falon.
Da sauri Riyyam din ya tashi yabi bayansa, yana me fad’in.
“To Hamma Rayyern tsaya muyi video dan Allah.”
Ramadan dake zaune ma mik’ewa tsaye yayi yabi bayansu.
A compound din gidan suka tsaya, inda Riyyam sarkin tiktok ya saita wayarsa ya soma yi musu video dukansu uku.
Harda sa musu wata y’ar wak’a, shidai Rayyern Kallon Yaron kawai yakeyi, domin a wuni biyu kawai da sukayi da yaron, ya fahimci wani abu, da kuma irin d’abi’a da yaron yayi shura akai.
Saidai kuma baisan Meyasa ba yakejin yaron acikin zuciyarsa hakan yasa yake kasa yakiceshi.
Gama k’arasowarsu compound din gidan kuwa, yayi dai-dai da fitowan Baba Maud’o daga cikin d’an madaidacin Part ɗinsa dake gefen gate.
Yana fitowa dinne kuma ya sauk’e idanunsa akan Rayyern, dake sanye cikin al-kyabba.
Wani irin tsayuwa Baba Maud’on yaji zuciyarsa tayi, take kuma wasu irin abubuwa suka shiga dawowa cikin tunaninsa.
Saidai kuma Ina ayanzu kwakwalwarsa bata da wani buk’atar amsar kowani irin sak’o, wannan dalilin yasa zuciyarsa ke cigaba da bugawa da harbawa a hankali.
D’an matsowa kusa dasu Baba Maud’on yayi, tare kuma da sauk’e idanunsa akan Riyyam wanda keta faman bin wak’ar Justin Bieber me suna (Peaches) dake tashi awayarsa.
Idanu Baba Maud’o ya tsurawa yaron baya ko k’iftawa, Yayinda zuciyarsa ke cike da zallan mamakin, kamannin Rayyern dake kwance akan fuskar yaron.
“Baba Maud’o barka da yammaci.”
Cewar Rayyern.
Wanda maganan nasa ne kuma yasa Baba Maud’o dawowa cikin tunaninsa.
Murmushi ne ya bayyana akan fuskarsa, duk da kuwa cewar rabin fuskartasa arufe take, amma hakan bai hana Rayyern din gane cewar Baba Maud’on murmushi yayi ba.
“Yauwa Barka dai Rayyern, yau kuma inazaka je haka naga kayi shigar da ta bayyana kyau da cikar haibarka.”
Murmushi Rayyern din yayi, tare da dan matsowa kusa da Baba Maud’on kana yace.
“Wurin wasan polo zanje Baba Maud’o".
Kai ya jinjina alamun gamsuwa.
"Shin ko akwai wasu abubuwan buk’ata naka da suka k’are, idan nazo dawowa saina sayo maka.”
Rayyern ya tambayeshi cikin mutunta ma'aikatan gidan nasu.
Again Murmushi Baba Maud’o yayi, cikin kuma Jin dadin kulawan da su Rayyern din sukeyi dashi yace.
“A’a Alhamdulillah ayanzu kam bana buk’atar komai, saidai nace kayi kyau sosai cikin wannan shigar, amma baka daura hiramin naka dai-dai ba, Bari na gyarama irin yanda samarin makka suke saka nasu.”
Murmushi Rayyern din yayi, kana ya matso Baba Maud’o d’in ya gyara masa sakun hiramin.
Riyyam-nsra kuwa da d’an mamaki ya kalli Hamma Rayyern dinnasu, tare da cewa.
“Hamma Rayyern waye wannan mutumin, naga jiya da nazo banganshi ba.”
“Sunansa Baba Maud’o.”
Ramadam ya bashi amsa.
Saurin jinjina Kai Riyyam yayi, kana ahankali ya matso kusa da Baba Maud’o din.
Fuskarsa dauke da murmushi yace.
“Rawanin da kasa akanka zuwa fuskarka yayi kyau sosai Baba Maud’o, Dan Allah Hamma Rayyern kuzo mu d’auki hoton selfie tare dashi, saboda Idan na koma Ethiopia zan nunawa Mammyna, na kuma bata labarin yanda wasu daga cikin yan Nigeria sukeyin shigarsu.”
Ya fad’i hakan saboda baisan cewa Baba Maud’o’n shigar buzayen Niger 🇳🇪 yayi ba.
Kamar yanda ya buk’ata kuwa matsowa Rayyern da Ramadan sukayi, inda suka saka Baba Maud’o da Riyyam din atsakiya.
Hakanne kuwa yasa Baba Maud’o da Riyyam din ke iya jiyo sautin bugun zuciyar kowannensu, saboda yanayin yanda sukayi kusan ci sosai da juna, domin Riyyam dan sarkin son jiki, har rungume Baba Maud’on yayi ajikinsa.
Yayinda Ramadan ya karb’i wayar Riyyam d’in, yayi musu hoton selfie har kala biyu.
Bayan ya mikawa Riyyam din wayarsa ne kuma,
Rayyern ya juya ya shiga motarsa, driver’nsa yaja suka fice daga cikin gidan.
Ramadan da Riyyam kuwa zama sukayi dab’as Akan wani dan dogon Bencin da Baba Maud’o ke zama, haka kuwa suka sa Baba Maud’on agaba sunata hira, musamman Riyyam daya bud’e baki ya dinga shararawa Baba Maud’on labarai kala-kala, wanda duk rabinsu na abun dariya ne.
*Arewa 24 TV*
Jannart ne da Salman ke tafe acikin babban corridor din, da zai sadasu da compound din gidan tv'n nasu.
Anutse Jannart take takunta, Yayinda time to time take Kallon fuskar wayarta dake rike ahannunta.
Salman dake biye da ita kuwa, idan hankalinsa yakai dubu to duk akanta yake.
Baisan meyasaba hardai idan Jannart tana waje, baya tab’a iya dauke kansa daga gareta, koda kuwa yaya baya iya gajiya da Kallon tafiyarta mai kama data hawainiya.
Yayi Imani azuciyarsa cewa Jannart macece ta gasken gaske, ko acikin mata irinta basu da yawa.
Isowarsu jikin motarsa ne kuma yasa Jannart fakon idanun guard dinta ta shige cikin motar, kana cikin sauri tace.
“Please Salman kayi sauri mubar nan, Domin idan wayannan kattin suka ganni dakai ina mai tabbatar maka cewar akwai matsala.”
“Nikuwa nasan da cewar akwai matsala ai Jannart, abu mai sauki ne ma su samin bindiga akaina su harbeni, tsoron da ake baki agidanku ko Gwamna iyakaci.”
Salman din ya fada adaidai lokacin da yake ta da motar suka bar wajen.
Suna hawa titi kuwa Jannart ta sauk’e ajiyar zuciya tare da fad’in.
“Allah Yasa dai mudace mu samu ganinsa yau, amma mutum dan ya zama richest man shikenan kuma ganinsa saiya zama wahala.”
Shidai Salman murmushi kawai yayi kaman zaice wani abu kuma saiya fasa.
Kaitsaye suka nufi Mai-nasara Hospital.
Tafiyar mintuna kad’anne ya kawosu bakin kofar katafaren asibitin.
Kasancewar kuma ba ashiga can Cikin hospital din da mota, matuk’ar ba emergency bane, yasa Salman parking motar anan babban parking lot na asibitin, wanda shi kansa ya kusan kwatan wata karamar unguwa.
Bud’e murfin motar Jannart tayi ta fito, tana me k’arewa kyau da had’uwar asibitin kallo.
Lallai privet Hospital ne daya amsa sunansa, saboda daga ginin asibitin ma kasan ba kananan billions aka kashe masa ba.
“Mai-nasara Hospital! Lallai asibitin ya had’u.”
Jannart din ta fad’a tana me Kallon Salman.
Shima Salman din kallonta yayi, tare da cewa.
“To Kema da bakinki kin fad’a, yanzu kiyi imagine tayaya za ace kinsamu ganin mamallakin wannan wajen acikin sauki? karki manta kuma bawai iya Hospital dinnan ya mallaka ba, yana da companies, bama a iya Nigeria ba, wallahi Jannart wannan mutumin *Richest Man* ne na k’arshe.”
Kai Jannart d’in ta jinjina, domin ita kanta ayanzu ta yarda da hakan.
Kaitsaye kuma suka kutsa cikin asibitin.
Acan b’angaren Rayyern kuwa kaitsaye Wajen buga wasan polo suka nufa.
Koda suka isa wajen da haduwarsa da kuma kyawunsa ya darawa kwatance.
A parking lot driver’nsa yayi parking.
Bayan ya fito daga motar nasa ne kuma kaitsaye ya nufi cikin wajen.
Da kwata-kwata babu mutane acikinsa.
Duk da tsananin girman wajen kuwa, amma bakajin motsin komai saina tarin dawakai da kuma tsirarun masu kula dasu.
Wanda kuma hakan ya faru ne saboda zuwan Dr.Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara, kasancewar idan har zaizo wajen To yakan biya mak’udan kud’ad’e ne, ta yanda ranar baza'a amshi kuɗin wasuba, harsai yayi wasansa ya gama ak’alla na tsawon awa 2, bayan ya tafi ne kuma sauran jama’a zasu dawo su cigaba da harkokinsu bawai kuma yana haka dan isa bane, sai dan sosai hayani kan iya sa mishi ciwon kai, yana kuma jin daɗi wasan polo a jikinsa.
Shigarsa cikin babban wajen wasan buga Polo dinne kuma yasashi, zare alkyabban dake jikinsa ya ajiye, tare da wayoyinsa harma da y’ar bag din da yasaka bottle water mai sanyi aciki.