Sashe 42
Tubali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Amatuk’ar fusace Daddyn ya juyo, cikin tafasan zuciya ya dann wani tsawan daya saka hanjin cikin Momn kad’awa yace.
“Waya baki izinin shigomin falo kai tsaye? Kifita daga harkata fa Maryam, da kike tambayan Jannart kinfini sonta ne? Ba’ayata bace, Ina ruwanki da inda aka kaita? Ko kece kika haifa min ita? Fice min daga falo, tunkafun na aikata abunda zai bata miki rai!!!”
Daddy’n ya fad’a fuskarsa babu alaman annuri asamanta.
Hakan kuwa shiya sanya, gaba d’aya jikin Mom yayi sanyi, kamar kuma yanda ya buk’ata cikin sauri ta juya ta fice daga cikin falon.
Abdull dake tsaye awaje kuwa ganin Mom nasu tafi to jiki asanyaye ne yasashi rufa mata baya.
Bayan sun isa nasu falonne ya kalli mahaifiyar tasa cikin sharce hawaye yace cewa.
“Ki kwantar da hankalinki Mom, Insha Allah Aunty Jannart ako Ina take Allah zai kula da ita, kuma naga Abba Kabir nema da kansa ya d’auketa, nasan kuma asibiti zai kaita.”
Jin abunda Abdull din ya fad’ane kuwa yasa Mom sauke ajiyar zuciya, lokaci guda kuma taji hankalinta ya d’an kwanta.
Wayarta ta dauka tare da lalub’o lamban Barrister Kabir din, saidai kuma amma kwata kwata wayartasa bata shiga, hakanne kuma yasa ta hakura tare da ajiyewa akan anjima zata sake kira.
*Mainasara hospital*
Cikin yanayin tashin hankali Barrister Kabir ya zauna bisa kujerar dake gaban babban table ɗin dake gaba Dr Sulaiman.
Gyara zama Dr Sulaiman yayi tare da d’an sauk’e numfashi, kana ya fuskanci Barrister Kabir, murya a tausashe yace.
“Babanta ne kai?”.
Cikin sauri Barrister Kabir ya gyaɗa mishi kai alamun eh kawai.
Shi kuwa Dr Sulaiman, kai ya jinjina tare da ci gaba da cewa.
“Kuna sane da cewa tana ɗauke da chronic Asthma, wanda yayi worst sosai ajikinta ko kunsan hakan?”
Kai Barrister Kabir ya jinjina, kana cikin bada tabbaci yace.
“K’warai Dr. munsan da hakan.”
Ajiyar zuciya Dr. Sulaiman din yayi, kamar kuma zaice wani abu saiya fasa, rubutu ya danyi ajikin wata takarda.
Bayan ya mikowa Barrister Kabir din takardar ne kuma yace.
“Way’annan sune magungunan da zata sha idan ta farka, sannan kuma Dan Allah ana kiyaye yawan bacin ranta please dan abubuwan sunyiwa zuciyarta yawa, har ta fara samun raunin harbawar jini.”
Kai Barrister Kabir din ya jinjina, tare da cewa.
“Insha Allah Dr. Nagode sosai, amma ya kake gani shin zan iya zuwa na Ganta kuwa.”
“K’warai kuwa saidai kada kayi wata magana mai karfi da zai disturbing nata, saboda akwai alluran da mukayi mata, wanda akwai buk’atar dole saita huta.”
Kai Barrister Kabir din ya jinjina, tare da mikewa tsaye musabaha suka sakeyi da Dr. Sulaiman din.
Bayan kuma ya gaya masa numbern dakin da Jannart din ke ciki ne ya juya yafice daga cikin office din.
_Dan girman Allah da isarsa masu fitar da littafina da masu karanta na sata da masu karanta Audio books da masu sawa a YouTube da masu posting nashi a wani wurin kuyiwa girman zatin ubangiji daya haliccemu kada ku taɓamin. Littafina sai kunmin mgn kun saya na lamunce muku ku, dan kin biya 1k ko 500 bawai kuɗin mallakarsa kika biyaba, kudin samun damar karantawa ne 09097853276, ga number' ta, in Kuma zaki sayane ga ac no dina 0661110170 GTBank AISHA GARKUWA ALIYU_
Kaitsaye dakin da aka kwantar da Jannart din ya nufa,
Koda ya shiga tura kofar dakin yayi, inda ya Sameta kwance tana bacci, an daura mata drip ajikinta.
Karasowa Cikin dakin Abba Kabir din yayi, cikin tsananin kulawa hadi da tausayawa ya sa hannu ya shafi goshin Jannart din dake bacci Cikin kwanciyar hankali.
“Insha Allah Jannart farinciki yana nan zuwa acikin rayuwarki, Domin ba zaki tabbata acikin kunci ba har abada, Tabbas watarana makiyanki sai sunji kunya, kunya irin Wanda ba zasu taba iya daga Ido su kalleki ba, Insha Allah watarana zaki zama y’antacciya nan bada jimawa ba.”
Abba Kabir din ya fad’a, cikin tabbaci da kuma sanin lokacin hakan na k’aratowa sabida yasan dole watan-wata rana gsky zatayi halinta.
Sanin da yayi kuma cewar Dr yace abarta tasamu ishashshen hutu ne yasa shi matsawa can gefe, tare da zaro wayarsa kaitsaye ya dannawa lamban Dr Sajo Kira.
Cikin sa’a kuwa bugu uku kacal Dr Sajo ya d’aga wayan.
Bayan sun gaisane kuma Abba Kabir din ya gyara zamansa tare da cewa.
“Yaya Sajo jikin d’iyarku Jannart ne ya tashi, yanzu haka muna cikin Mai-nasara Hospital an bata gado, saidai kuma ba Dr. Rayyern ne ya duba ta.”
Daga can b’angaren Dr. Sajo yace.
“Subahanallah yanzu Ina fata jikin natan da sauki.”
“Eh.” Abba ya bashi amsa.
Dr. Sajon kuwa cewa yayi.
“Karka damu Barrister Kabir Indai kuna Cikin Mai-nasara Hospital, koba Dr. Rayyern bane ya duba ta, To Ina tabbatar maka da zata samu isashshen kulawa, Domin gaba d’aya likitotin dake cikin asibitin sunsan aikinsu, kuma dukansu k’wararrune kamar yadda suke da lafiyayyun kayan aiki, sannan maganar Dr. Rayyern dinma zaku samu ganinsa Idan kukayi booking Insha Allah.
Cikin samun karfin guiwa yace.
"In Sha Allah kuwa zamuyi booking”.
“Yauwa sai munzo”.
To yace kana sukayi sallama da juna.
Yana katse kiran ne kuma ya kira Matarsa Aunty Dijat ya Sanar da ita halin da ake ciki, nanfa tace gatanan zuwa ta k’are mgnar da cewa.
“Yanzu ya jikin nata?”.
Juyowa yayi ya d’an ya kalleta.
a hankali take fesar da numfashi alamin baccinta yayi zurfi.
“Da sauki.”
Ya bata amsa, Domin kuwa harzuwa lokacin Jannart din bacci take bata farka ba.
“Allah ya ƙara sauki”.
Amin yace kana sukayi sallama.
K’arfe 5 dai-dai ne kuma yana nan zaune, kiran Yayan nasa, wato Alhaji Idi Sale Dakata ya shigo cikin wayarsa.
Bayan ya d’aga wayarne kuma Daddy da hankalinsa ke tashe yace.
“Wai Kabir ina kuka shiga ne? Wani asibiti ne ka kai Jannart, duk na karad’e asibitoci mafi kusa damu amma babuku babu alaman ku, kuna Ina sannan ya jikin Jannart din?”
Daddyn ya had’ewa Barrister Kabir duka tambayoyin awaje d’aya.
Barrister Kabir kuwa ajiyar zuciya ya sauk’e, tare da cewa.
“Kayi hakuri Yayah, gaba daya sha’anin ciwon Jannart dinne ya rudar dani, shi yasa bankira na sanar dakai komai ba, yanzu dai haka muna Cikin Mai-nasara Hospital, kuma jikin nata da sauki sosai Dan tun da doctors suka duba ta take bacci har yanzu kuma bata farka ba.”
Shima Daddyn ajiyar zuciya ya sauk’e, nan take kuwa yace.
“Okay ganinan zuwa Mai-nasara Hospital din”
Yana gama fadin hakan kuwa ya kashe wayan.
Mom dake kallonsa ne kuma tace.
“Bari na dauko mayafi na muje, Domin dama na gama abinci, Idan yaso saina tafi musu dashi.”
Kai kawai Daddyn ya jinjina mata, Domin kuwa hardai yanzu, Jin zuciyarsa yake a Jagule.
Koda Mom ta d’auko mayafin nata, kitchin ta wuce tare da daukan basket din da ta shirya food flask acikinsa.
Kaitsaye waje ta nufa, saboda tuni Daddyn ya fice.
Tana fita compound din gidan kuwa ta sameshi zaune acikin motarsa, bayan ta shiga kana driver yaja suka fice daga cikin gidan.
6:12 pm dai dai suka iso cikin asibitin, wanda kuma zuwannasu yayi dai dai da zuwan Aunty Dijat.
Domin kusan atare ma suka shiga cikin d’akin da Jannart din ke kwance bisa jagorancin Barrister Kabir.
Bayan sun gaggaisa da junansu ne kuma, Aunty Dijat ta zubawa Barrister Kabir din kunun data dama musu ya sha kasancewar itama tayi girki na musamman ta taho dashi.
A lokacin da aka soma kiraye kirayen Sallah magriba ne kuma, Daddy da Abba suka fice dan zuwa masallaci.
Yayinda su Aunty Dijat da Momy kuwa anan cikin d’akin asibitin sukayi nasu sallan.
Dawowar dasu Barrister Kabir din sukayi a masallaci kuwa, yayi dai-dai da shigowan wasu nurses guda biyu.
Ledan ruwan dake jikin Jannart din, wanda ya k’are nurses din suka cire, tare kuma da sake yi mata wasu y’an gwaje gwaje.
Bayan sun kammala duba lafiyar Jannart d’inne kuma, suka juyo inda d’aya daga cikin nurses din tace.
“Kuyi hakuri patient din batason hayaniya sosai, kuma ak’a’idar aikinmu Idan dare yayi, bama barin kowa acikin Hospital din sai masu kula da majinyata, saboda haka dole duk zaku tafi, saidai za a bar mutum guda d’aya kawai da zaina kulawa da ita, ma’ana wanda zai kwana da ita.”
Kai Duk suka jinjina, cikin gamsuwa da bayanan Nurse din Aunty Dijat tace.
“Shikenan To Abban Hafeez kuje, Idan yaso ni zan kwana da ita”
Saurin girgiza Kai Mom tayi tare da cewa.
“A’a Dijat baza’ayi haka ba, duk kuje ni zan kwana da ita, Domin ba wani d’awainiya ne akaina sosai ba, ke kuwa nasan dole su Hafeeza zasu nemeki.”
Murmushi Aunty Dijat din tayi kawai, saboda tasan maganan da Mom'n ta fad’a gaskiya ne.
Hakan kuwa akayi kamar yanda Momy tace, ita dince ta zauna awajen Jannart din , yayinda Barrister Kabir, Daddy, da kuma Aunty Dijat suka koma gida.
Mom na zaune kuwa har wajajen k’arfe 11 zuwa 12 amma Jannart bata farka daga nannauyan baccin da takeyi ba, wanda kuma hakan ya samo asaline saboda, k’arfin alluran dasu Dr. Sulaiman sukayi mata.
*Littafin TUBALI na kuɗine ki biya kafin ki karanta cikin salama special Group 1k ne karamin group 500 kacal kuɗin karantawa ne bawai kuɗin mallakan littafin bane, 0661110170 GTBank AISHA GARKUWA ALIYU sai ki turo min shaidar biyanki ta whatsApp number na 09097853276 in ba halin turawa ta ac no kuwa ki sayi katin MTN ki copy number's din ki turo min ta WhatsApp*
Acan gidansu Rayyern kuwa, gaba d’aya babu wani wanda zaka kalla kace yana cikin farinciki, musamman ma da ayanzun suka ga, Rayyern din ya kwashe sama da awanni bakwai bai farka daga baccin daya daukeshi ba.
*11:30 pm*
Dai-dai ahankali ya soma bud’e idanunsa da sukayi masa nauyi.
Inda yana gama waresu kuwa ya sauk’esu, tarwal akan Abbansa dake zaune agefe, ya k’ura masa ido, da dukkan alama kuma jiran farkawan nasa yake.
Idanun nasa ya sake bud’ewa da kyau, cikin kuma dan kuzarin da ya saura masa, ya soma yunkurin tashi zaune.
Ganin hakanne kuwa yasa Abba sakin numfashi, tare da cewa.
“Alhamdulillah Rayyern ka tashi ko, sannu ya jikin naka? Ya kakeji yanzu?”
Idanunsa ya d’an lumshe tare da k’ak’alo murmushin karfin hali, kana murya asanyaye yace.
“Alhamdulillah Abba, yanzu banajin komai naji sauki.”
“Waya baki izinin shigomin falo kai tsaye? Kifita daga harkata fa Maryam, da kike tambayan Jannart kinfini sonta ne? Ba’ayata bace, Ina ruwanki da inda aka kaita? Ko kece kika haifa min ita? Fice min daga falo, tunkafun na aikata abunda zai bata miki rai!!!”
Daddy’n ya fad’a fuskarsa babu alaman annuri asamanta.
Hakan kuwa shiya sanya, gaba d’aya jikin Mom yayi sanyi, kamar kuma yanda ya buk’ata cikin sauri ta juya ta fice daga cikin falon.
Abdull dake tsaye awaje kuwa ganin Mom nasu tafi to jiki asanyaye ne yasashi rufa mata baya.
Bayan sun isa nasu falonne ya kalli mahaifiyar tasa cikin sharce hawaye yace cewa.
“Ki kwantar da hankalinki Mom, Insha Allah Aunty Jannart ako Ina take Allah zai kula da ita, kuma naga Abba Kabir nema da kansa ya d’auketa, nasan kuma asibiti zai kaita.”
Jin abunda Abdull din ya fad’ane kuwa yasa Mom sauke ajiyar zuciya, lokaci guda kuma taji hankalinta ya d’an kwanta.
Wayarta ta dauka tare da lalub’o lamban Barrister Kabir din, saidai kuma amma kwata kwata wayartasa bata shiga, hakanne kuma yasa ta hakura tare da ajiyewa akan anjima zata sake kira.
*Mainasara hospital*
Cikin yanayin tashin hankali Barrister Kabir ya zauna bisa kujerar dake gaban babban table ɗin dake gaba Dr Sulaiman.
Gyara zama Dr Sulaiman yayi tare da d’an sauk’e numfashi, kana ya fuskanci Barrister Kabir, murya a tausashe yace.
“Babanta ne kai?”.
Cikin sauri Barrister Kabir ya gyaɗa mishi kai alamun eh kawai.
Shi kuwa Dr Sulaiman, kai ya jinjina tare da ci gaba da cewa.
“Kuna sane da cewa tana ɗauke da chronic Asthma, wanda yayi worst sosai ajikinta ko kunsan hakan?”
Kai Barrister Kabir ya jinjina, kana cikin bada tabbaci yace.
“K’warai Dr. munsan da hakan.”
Ajiyar zuciya Dr. Sulaiman din yayi, kamar kuma zaice wani abu saiya fasa, rubutu ya danyi ajikin wata takarda.
Bayan ya mikowa Barrister Kabir din takardar ne kuma yace.
“Way’annan sune magungunan da zata sha idan ta farka, sannan kuma Dan Allah ana kiyaye yawan bacin ranta please dan abubuwan sunyiwa zuciyarta yawa, har ta fara samun raunin harbawar jini.”
Kai Barrister Kabir din ya jinjina, tare da cewa.
“Insha Allah Dr. Nagode sosai, amma ya kake gani shin zan iya zuwa na Ganta kuwa.”
“K’warai kuwa saidai kada kayi wata magana mai karfi da zai disturbing nata, saboda akwai alluran da mukayi mata, wanda akwai buk’atar dole saita huta.”
Kai Barrister Kabir din ya jinjina, tare da mikewa tsaye musabaha suka sakeyi da Dr. Sulaiman din.
Bayan kuma ya gaya masa numbern dakin da Jannart din ke ciki ne ya juya yafice daga cikin office din.
_Dan girman Allah da isarsa masu fitar da littafina da masu karanta na sata da masu karanta Audio books da masu sawa a YouTube da masu posting nashi a wani wurin kuyiwa girman zatin ubangiji daya haliccemu kada ku taɓamin. Littafina sai kunmin mgn kun saya na lamunce muku ku, dan kin biya 1k ko 500 bawai kuɗin mallakarsa kika biyaba, kudin samun damar karantawa ne 09097853276, ga number' ta, in Kuma zaki sayane ga ac no dina 0661110170 GTBank AISHA GARKUWA ALIYU_
Kaitsaye dakin da aka kwantar da Jannart din ya nufa,
Koda ya shiga tura kofar dakin yayi, inda ya Sameta kwance tana bacci, an daura mata drip ajikinta.
Karasowa Cikin dakin Abba Kabir din yayi, cikin tsananin kulawa hadi da tausayawa ya sa hannu ya shafi goshin Jannart din dake bacci Cikin kwanciyar hankali.
“Insha Allah Jannart farinciki yana nan zuwa acikin rayuwarki, Domin ba zaki tabbata acikin kunci ba har abada, Tabbas watarana makiyanki sai sunji kunya, kunya irin Wanda ba zasu taba iya daga Ido su kalleki ba, Insha Allah watarana zaki zama y’antacciya nan bada jimawa ba.”
Abba Kabir din ya fad’a, cikin tabbaci da kuma sanin lokacin hakan na k’aratowa sabida yasan dole watan-wata rana gsky zatayi halinta.
Sanin da yayi kuma cewar Dr yace abarta tasamu ishashshen hutu ne yasa shi matsawa can gefe, tare da zaro wayarsa kaitsaye ya dannawa lamban Dr Sajo Kira.
Cikin sa’a kuwa bugu uku kacal Dr Sajo ya d’aga wayan.
Bayan sun gaisane kuma Abba Kabir din ya gyara zamansa tare da cewa.
“Yaya Sajo jikin d’iyarku Jannart ne ya tashi, yanzu haka muna cikin Mai-nasara Hospital an bata gado, saidai kuma ba Dr. Rayyern ne ya duba ta.”
Daga can b’angaren Dr. Sajo yace.
“Subahanallah yanzu Ina fata jikin natan da sauki.”
“Eh.” Abba ya bashi amsa.
Dr. Sajon kuwa cewa yayi.
“Karka damu Barrister Kabir Indai kuna Cikin Mai-nasara Hospital, koba Dr. Rayyern bane ya duba ta, To Ina tabbatar maka da zata samu isashshen kulawa, Domin gaba d’aya likitotin dake cikin asibitin sunsan aikinsu, kuma dukansu k’wararrune kamar yadda suke da lafiyayyun kayan aiki, sannan maganar Dr. Rayyern dinma zaku samu ganinsa Idan kukayi booking Insha Allah.
Cikin samun karfin guiwa yace.
"In Sha Allah kuwa zamuyi booking”.
“Yauwa sai munzo”.
To yace kana sukayi sallama da juna.
Yana katse kiran ne kuma ya kira Matarsa Aunty Dijat ya Sanar da ita halin da ake ciki, nanfa tace gatanan zuwa ta k’are mgnar da cewa.
“Yanzu ya jikin nata?”.
Juyowa yayi ya d’an ya kalleta.
a hankali take fesar da numfashi alamin baccinta yayi zurfi.
“Da sauki.”
Ya bata amsa, Domin kuwa harzuwa lokacin Jannart din bacci take bata farka ba.
“Allah ya ƙara sauki”.
Amin yace kana sukayi sallama.
K’arfe 5 dai-dai ne kuma yana nan zaune, kiran Yayan nasa, wato Alhaji Idi Sale Dakata ya shigo cikin wayarsa.
Bayan ya d’aga wayarne kuma Daddy da hankalinsa ke tashe yace.
“Wai Kabir ina kuka shiga ne? Wani asibiti ne ka kai Jannart, duk na karad’e asibitoci mafi kusa damu amma babuku babu alaman ku, kuna Ina sannan ya jikin Jannart din?”
Daddyn ya had’ewa Barrister Kabir duka tambayoyin awaje d’aya.
Barrister Kabir kuwa ajiyar zuciya ya sauk’e, tare da cewa.
“Kayi hakuri Yayah, gaba daya sha’anin ciwon Jannart dinne ya rudar dani, shi yasa bankira na sanar dakai komai ba, yanzu dai haka muna Cikin Mai-nasara Hospital, kuma jikin nata da sauki sosai Dan tun da doctors suka duba ta take bacci har yanzu kuma bata farka ba.”
Shima Daddyn ajiyar zuciya ya sauk’e, nan take kuwa yace.
“Okay ganinan zuwa Mai-nasara Hospital din”
Yana gama fadin hakan kuwa ya kashe wayan.
Mom dake kallonsa ne kuma tace.
“Bari na dauko mayafi na muje, Domin dama na gama abinci, Idan yaso saina tafi musu dashi.”
Kai kawai Daddyn ya jinjina mata, Domin kuwa hardai yanzu, Jin zuciyarsa yake a Jagule.
Koda Mom ta d’auko mayafin nata, kitchin ta wuce tare da daukan basket din da ta shirya food flask acikinsa.
Kaitsaye waje ta nufa, saboda tuni Daddyn ya fice.
Tana fita compound din gidan kuwa ta sameshi zaune acikin motarsa, bayan ta shiga kana driver yaja suka fice daga cikin gidan.
6:12 pm dai dai suka iso cikin asibitin, wanda kuma zuwannasu yayi dai dai da zuwan Aunty Dijat.
Domin kusan atare ma suka shiga cikin d’akin da Jannart din ke kwance bisa jagorancin Barrister Kabir.
Bayan sun gaggaisa da junansu ne kuma, Aunty Dijat ta zubawa Barrister Kabir din kunun data dama musu ya sha kasancewar itama tayi girki na musamman ta taho dashi.
A lokacin da aka soma kiraye kirayen Sallah magriba ne kuma, Daddy da Abba suka fice dan zuwa masallaci.
Yayinda su Aunty Dijat da Momy kuwa anan cikin d’akin asibitin sukayi nasu sallan.
Dawowar dasu Barrister Kabir din sukayi a masallaci kuwa, yayi dai-dai da shigowan wasu nurses guda biyu.
Ledan ruwan dake jikin Jannart din, wanda ya k’are nurses din suka cire, tare kuma da sake yi mata wasu y’an gwaje gwaje.
Bayan sun kammala duba lafiyar Jannart d’inne kuma, suka juyo inda d’aya daga cikin nurses din tace.
“Kuyi hakuri patient din batason hayaniya sosai, kuma ak’a’idar aikinmu Idan dare yayi, bama barin kowa acikin Hospital din sai masu kula da majinyata, saboda haka dole duk zaku tafi, saidai za a bar mutum guda d’aya kawai da zaina kulawa da ita, ma’ana wanda zai kwana da ita.”
Kai Duk suka jinjina, cikin gamsuwa da bayanan Nurse din Aunty Dijat tace.
“Shikenan To Abban Hafeez kuje, Idan yaso ni zan kwana da ita”
Saurin girgiza Kai Mom tayi tare da cewa.
“A’a Dijat baza’ayi haka ba, duk kuje ni zan kwana da ita, Domin ba wani d’awainiya ne akaina sosai ba, ke kuwa nasan dole su Hafeeza zasu nemeki.”
Murmushi Aunty Dijat din tayi kawai, saboda tasan maganan da Mom'n ta fad’a gaskiya ne.
Hakan kuwa akayi kamar yanda Momy tace, ita dince ta zauna awajen Jannart din , yayinda Barrister Kabir, Daddy, da kuma Aunty Dijat suka koma gida.
Mom na zaune kuwa har wajajen k’arfe 11 zuwa 12 amma Jannart bata farka daga nannauyan baccin da takeyi ba, wanda kuma hakan ya samo asaline saboda, k’arfin alluran dasu Dr. Sulaiman sukayi mata.
*Littafin TUBALI na kuɗine ki biya kafin ki karanta cikin salama special Group 1k ne karamin group 500 kacal kuɗin karantawa ne bawai kuɗin mallakan littafin bane, 0661110170 GTBank AISHA GARKUWA ALIYU sai ki turo min shaidar biyanki ta whatsApp number na 09097853276 in ba halin turawa ta ac no kuwa ki sayi katin MTN ki copy number's din ki turo min ta WhatsApp*
Acan gidansu Rayyern kuwa, gaba d’aya babu wani wanda zaka kalla kace yana cikin farinciki, musamman ma da ayanzun suka ga, Rayyern din ya kwashe sama da awanni bakwai bai farka daga baccin daya daukeshi ba.
*11:30 pm*
Dai-dai ahankali ya soma bud’e idanunsa da sukayi masa nauyi.
Inda yana gama waresu kuwa ya sauk’esu, tarwal akan Abbansa dake zaune agefe, ya k’ura masa ido, da dukkan alama kuma jiran farkawan nasa yake.
Idanun nasa ya sake bud’ewa da kyau, cikin kuma dan kuzarin da ya saura masa, ya soma yunkurin tashi zaune.
Ganin hakanne kuwa yasa Abba sakin numfashi, tare da cewa.
“Alhamdulillah Rayyern ka tashi ko, sannu ya jikin naka? Ya kakeji yanzu?”
Idanunsa ya d’an lumshe tare da k’ak’alo murmushin karfin hali, kana murya asanyaye yace.
“Alhamdulillah Abba, yanzu banajin komai naji sauki.”