Sashe 59
Tubali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kai Jannart ta jinjina, saboda ayanzu kam amatsayinta na y’ar jarida ta gamsu da duk kalaman mutumin, musamman da ta fahimci with full confidence yake magana, ba irin na wasu mutanen ba, da mafi yawancin maganansu Kame kame da kuma k’aryane.
Domin sometimes ma suna fad’an karyane Dan su kare kawunansu daga titsen yan jarida.
Daga can gefe kuwa, Asiya ce dake tsaye take ta aikin bankawa Jannart d’in Harara.
Yayinda takejin wani irin kuna da radadi acikin zuciyarta, Lallai Tabbas taso ace itace ta samu wannan damar, taso ace yau itace akan stage din tare da mutumin da kyau, nutsuwa da kuma haibarsa suka matuk’ar tafiya da hankalin ta, kana kuma mutumin da take ganin cewa, samun daman magana dashi ma wani matakin nasara ne.
Kamar kuwa yanda Asiya ke jin tukukin bakinciki acikin zuciyarta, haka ma Dr Lukman, yakejin kamar ya shiga cikin tv’n ya shak’o wuyar Dr Rayyern.
Abunda yasan bazai taba samun daman aikatashi ba a gaske kenan.
Kallonsa ya mayar gasu Alhaji Idi Sale Dakata, cikin takaici yace.
“Lallai wannan Dr Rayyern din shege ne, ko ta Ina so yake ya tauyeni, bakinsa baya tab’a mutuwa, kowacce tambaya akwai amsarta acikin kansa.”
Murmushin daya fi kuka ciwo Alhaji Idi Sale Dakata’n yayi, cikin takaicin daya lullub’e zuciyarsa yace.
“Nan kusa wannan bakin nasa bazai sake motsawa ba, wannan alk’awari ne na daukawa kaina.”
Murmushin Jin dadi Dr Lukman da kuma Alhaji Abdu Tababa sukayi, saboda sanin hali irin na Alhaji Idi Sale Dakata da sukayi, Domin sunsan duk abunda yace zai aikata saiya aikata Tabbas.
Ab’angaren Gidansu Rayyern kuwa, Abba Mamy, Ramadan da kuma Riyyam-nsra ne zaune afalo suna kallon shirin, gaba daya sun bada hankalinsu akan shirin, musamman ma Abba, da tunaninsa ya rabu izuwa wani waje na daban.
Kallon Rayyern da kuma yarinyar da takeyiwa Rayyern din tambayoyi yake baya ko k’yaftawa, Yayinda acikin zuciyarsa yakejin wani irin abu na daban.
Su Ramadan kuwa Hamman nasu suka tsurawa ido,suna mai jinjina kawunansu saboda irin amsoshin da Hamman nasu ke bayarwa, yana matukar ratsa zuciyarsu, acikin zuciyarsu kuwa babu wanda bai yaba da irin kyawun yarinyar da takeyiwa Rayyern din tambayoyi ba.
Jannart kuwa, akaro na barkatai ta d’ago ta kalli camera’s din dake haska su, mike din dake gefenta ta gyara, tare da cewa.
“Kamar dai yanda kuka sani, ayanzu zamu bud’e layukan wayoyinmu saboda, masu kira.
Dan fadar ra’ayoyinsu da tambaya, ga numbar layin namu kamar haka...
Tana gama fad’an numbers dinne kuma ta kunna wata waya mai kaman telephone dake aje agabansu, kan wani had’add’en table.
Aikuwa kaman jira ake sukunna layin saiga kiraye-kiraye suna shigowa.
Wanda manyan mutane-ne suke kiran.
Numfashi ta ɗan fesar tare da gyara zamanta.
Kana ta ɗan kalli wayar da wani kiran ya kuma shigowa tun kan ta ajiyeta.
Picking call din Jannart tayi, tare kuma da latsawa tasa wayar a hands free.
Cikin zazzakar muryarta tace.
“Assalamu Alaekum.”
Daga can b’angaren aka amsa mata, da murya irin ta manyan mutane.
Jin hakanne kuma yasa ta cewa.
“Barka da shigowa filin bakon mako.”
“Yauwa Barka dai”.
Aka faɗa daga daya sashin cikin girma.
Ita kuwa Jannart lumshe idonta tayi tare da cewa.
“Ko zamu iya sanin waye akan layi?.”
“Sunana Alhaji Abubakar Ginsau S.A protocol na gwamna, nakira ne kuma Domin na jinjinawa babban Bak’o DR. Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara, agame da maganganu masu amfani daya fad’a, Insha Allahu kuma maganan zata isa ga kunnen way’anda ya kamata suji, sannan muna godiya k’warai matuk’a, da irin shawarwarin daya bayar.”
Kai Jannart ta jinjina, tare da dan satan Kallon Dr Rayyern din, wanda ya kauda kansa gefe, kamar baiji ana yabonsa ba.
“Girman kai rawanin tsiya.”
Tafad’a acikin zuciyarta, Yayinda afili kuwa cewa tayi.
“To S.A protocol muma godiya muke sosai, sannan bakon mu Dakta shima yana godiya.”
Daga haka kuwa kiran S.A din ya katse, wani kiran kuma ya sake shigowa.
Cikin tashin hankali Dr Lukman ya mik’e tsaye, tare dasa hannunsa ya dafe kansa, zuciyarsa cike da takaici yace.
“Lallai wannan yaron ya shallake duk wani tunani na, ba a banza ba ake kiransa da Mai-nasara ba, tunda gashi yayi sara akan gab’a, daga maganansa har S.A da kansa ya kira, ya kuma shaida cewa maganar zata tafi har wajen governor, wannan wanne irin Dan iskan yaro ne? Mai sa'a”.
Cikin tsananin takaici tsana Alhaji Idi Saleh Dakata ya fesar da numfashi tare da cewa.
“Ai yamafi Dan iska wannan yaron da kake gani Dr Lukman, shegen yaro ne kwance-kwance yake mana, da sannu Idan bamu tashi ba, duk sai yabi ya sare mana duk wani reshen mu, b’arna babba yake aikata mana, batare da ko damuwa da hakan yayi ba, Tabbas kuma ya kafu iya kafuwa, da wayannan kalaman nasa masu ratsa zuciya yake yaudarar mutane, waishi ala dole mai tausayin talakawa, yana abu tamkar Dan siyasan da yake barar neman kujerar takara, hmmmm Lallai zanyi maganin wannan yaron, zan kawar dashi kamar yanda na kawar da way’anda suka fishi tsauri a baya.”
Alhaji Idi Sale Dakata ya ƙare mgnar yana me sakin zazzafan numfashin takaici.
Yayinda Alhaji Abdu Tababa kuwa yace.
“Lallai kawar dashi daga doron k’asa shine hanya mafi a’ala, Idan ba haka ba kuwa duk sai ya fito damu waje cikin rana daga gidajenmu.”
“Hakan bazaiyi wuba kuwa.”
Alhaji Idi Sale’n ya fad’a yana me mikewa tsaye.
Yayinda acan gidan su Rayyern kuwa, har yanzu su Abba basu matsa daga gun tv’n ba.
Sunanan zaune kowannensu dauke da farincikin, irin nasaran da Rayyern din ke samu.
Haka ma agidan Barrister Kabir har yanzu shima yana zaune agaban tv’nsa.
Dai-dai lokacin da ake cigaba da haska shirinne kuma, Aunty Dijat ta fito daga daki.
Zama tayi akusa da mijinnata tare da soma kokarin had’a masa coffee.
Kallon ta Barrister Kabir din yayi, kana cikin tausasa murya yace.
“Dijat kalli tv kiga, Jannart da matashin saurayin nan dake zaune agefenta”.
Da sauri ta miƙa mishi cup ɗin tare da zubawa tv ido tare da cewa.
“Masha Allah”.
Kurban coffee'n yayi tare da cewa.
“Sundace ko?.”
Ware ido Aunty Dijat din tayi ta kalli tv’n, dai-dai lokacin kuwa aka sake matso da fuskokin Jannart dana Rayyern din kusa.
“Masha Allah, ai kuwa Abban Hafeez matukar dacewa ma sukayi, kyau da kyau kenan.”
Murmushi Barrister Kabir din yayi, tare da gyara zamansa a takaice yace.
“Shine mijin dana zab’a mata, kuma shine wanda zata aura amma batare da ta sani ba.”
Ya fad’a yana me karb’an coffee din da aka had’asa masa.
Idanu Aunty Dijat ta d’an zaro waje, cike da tsananin mamaki hadi da zallar farinciki tace.
“Allahu Akhbar, Lallai girman Allah iko da buwayarsa tana da yawa, Masha Allah Lallai Jannart ta dace da hazik’in Namiji kuma jarumi, mai dauke da nagarta, Tabbas ka cika Uba nagari, ai kuwa zamusha biki yaushe ne Auren?”
Murmushi Abban yayi, tare da girgiza mata Kai, Ahankali kuma yace.
“A’a bayanzu zan gaya miki ba, abun namu sirrine.”
*GARKUWAR taku ce dai MA'AURATA, da masu shirin aure, da masu jego, da yan gayu masu son k’amshi kece raini, da gyaran da zaike maimaita muku dararen forkon kuruciya*
Ko kunsan Jikinmu na da sinadaran hormones da suke taimakawa dan’adam akan komai musamman lokacin da mace take mu’amalar aure da mijinta. Mafi akasari wannan hormones din ne ke samun matsala ko su yi sanyi koma su daina aiki kwata-kwata shi ne dalilin da zai sa mace tace bata jin sha’awa ko bata san dadin aure ba. Albishirinku ina da kayan da ke taimakawa wannan sinadaran du dawo aiki tukuru don karkato miki da kimarki wajan mai gida sannan su taimakawa wannan sinadaran hormones dinki su dinka secreting din ni’ima wadatacciya da zata taimaka miki ki gamsu mijinki ya gamsu fiye da tunaninki. Note: Kayana ba sa tsinka ruwan ni’ima suna dai taimakawa hormones dinki ne su tsattsafo da ni’imar musamman wacca cutar sanyi ko dattin mahaifa ya dankarar da su ya hana su yin aikinsu yanda ya kamata. Haka zalika idan kina da kyau ki kara da wanka. Zaki iya amfani da magani na na gargajiya wanda zai gyara miki sex hormones din kullum ki kasance cikin humidify wato cikin damshi mai albarka kamar yanda ake son mace. Yana gyara miki mara.
Sai kamshi. Hajiyata daure ki fara amfani da turarena ki ji irin salon kamshin sa salo ne da zai daidaita ki da mijinki ya kankaro miki da kimarki a wajansa. Siyan na gari mayar da kudi gida.
Ga masu buƙata ga number' wayata wanda nake whatsApp dashi 09097853276 kimin mgn ta whatsApp in har kin tabbatar kin shirya saya mu dai-dai ta, kayana ba ƙanana bane, shiyasa bana harkan karanta, muddin kinsan baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu, ba ina nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so.
0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki kaya a mota, duk ƙasar da kike kayana zaije gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nasune🤝🏻sayan na gari meda kudi gida.
GARKUWAR MA'AURATA
By
*GARKUWAR FULANI*
Murmushin Jin dadi Aunty Dijat din tayi, kana cikin sakin fuska tace.
“Alhamdulillah nidai ko yaushene ma ina jira.”
Barrister Kabir dinma murmushi yayi, batare kuma daya sake cewa komai ba, ya cigaba da shan coffee d’insa.
Acan cikin tashar kuwa, zuwa yanzu kira na 15 kenan Jannart din ta amsa, wanda kuma daga kan kira na 15 dinne ta katse layin gaba d’aya, tare da d’agowa ta kalli cameras din dake jere agabansu.
“To masu kallonmu laifin dadi dai ance karewa, Domin naga lokaci yana daga mana hannu, saboda haka duka duka anan muka kawo k’arshen shirin namu Na Bak’on Mako, sai kuma wani sati Idan mai kowa mai komai ya kaimu, Insha Allah zamu sake zuwar muku da wani bak’on na musamman.”
Dan Juyowa tayi ta kalli Rayyern dake zaune, Cikin kuma sakin fuska kamar yanda ta sabayiwa kowa tace.
“Doctor ayiwa masu kallo da sauraronmu sallama.”
Domin sometimes ma suna fad’an karyane Dan su kare kawunansu daga titsen yan jarida.
Daga can gefe kuwa, Asiya ce dake tsaye take ta aikin bankawa Jannart d’in Harara.
Yayinda takejin wani irin kuna da radadi acikin zuciyarta, Lallai Tabbas taso ace itace ta samu wannan damar, taso ace yau itace akan stage din tare da mutumin da kyau, nutsuwa da kuma haibarsa suka matuk’ar tafiya da hankalin ta, kana kuma mutumin da take ganin cewa, samun daman magana dashi ma wani matakin nasara ne.
Kamar kuwa yanda Asiya ke jin tukukin bakinciki acikin zuciyarta, haka ma Dr Lukman, yakejin kamar ya shiga cikin tv’n ya shak’o wuyar Dr Rayyern.
Abunda yasan bazai taba samun daman aikatashi ba a gaske kenan.
Kallonsa ya mayar gasu Alhaji Idi Sale Dakata, cikin takaici yace.
“Lallai wannan Dr Rayyern din shege ne, ko ta Ina so yake ya tauyeni, bakinsa baya tab’a mutuwa, kowacce tambaya akwai amsarta acikin kansa.”
Murmushin daya fi kuka ciwo Alhaji Idi Sale Dakata’n yayi, cikin takaicin daya lullub’e zuciyarsa yace.
“Nan kusa wannan bakin nasa bazai sake motsawa ba, wannan alk’awari ne na daukawa kaina.”
Murmushin Jin dadi Dr Lukman da kuma Alhaji Abdu Tababa sukayi, saboda sanin hali irin na Alhaji Idi Sale Dakata da sukayi, Domin sunsan duk abunda yace zai aikata saiya aikata Tabbas.
Ab’angaren Gidansu Rayyern kuwa, Abba Mamy, Ramadan da kuma Riyyam-nsra ne zaune afalo suna kallon shirin, gaba daya sun bada hankalinsu akan shirin, musamman ma Abba, da tunaninsa ya rabu izuwa wani waje na daban.
Kallon Rayyern da kuma yarinyar da takeyiwa Rayyern din tambayoyi yake baya ko k’yaftawa, Yayinda acikin zuciyarsa yakejin wani irin abu na daban.
Su Ramadan kuwa Hamman nasu suka tsurawa ido,suna mai jinjina kawunansu saboda irin amsoshin da Hamman nasu ke bayarwa, yana matukar ratsa zuciyarsu, acikin zuciyarsu kuwa babu wanda bai yaba da irin kyawun yarinyar da takeyiwa Rayyern din tambayoyi ba.
Jannart kuwa, akaro na barkatai ta d’ago ta kalli camera’s din dake haska su, mike din dake gefenta ta gyara, tare da cewa.
“Kamar dai yanda kuka sani, ayanzu zamu bud’e layukan wayoyinmu saboda, masu kira.
Dan fadar ra’ayoyinsu da tambaya, ga numbar layin namu kamar haka...
Tana gama fad’an numbers dinne kuma ta kunna wata waya mai kaman telephone dake aje agabansu, kan wani had’add’en table.
Aikuwa kaman jira ake sukunna layin saiga kiraye-kiraye suna shigowa.
Wanda manyan mutane-ne suke kiran.
Numfashi ta ɗan fesar tare da gyara zamanta.
Kana ta ɗan kalli wayar da wani kiran ya kuma shigowa tun kan ta ajiyeta.
Picking call din Jannart tayi, tare kuma da latsawa tasa wayar a hands free.
Cikin zazzakar muryarta tace.
“Assalamu Alaekum.”
Daga can b’angaren aka amsa mata, da murya irin ta manyan mutane.
Jin hakanne kuma yasa ta cewa.
“Barka da shigowa filin bakon mako.”
“Yauwa Barka dai”.
Aka faɗa daga daya sashin cikin girma.
Ita kuwa Jannart lumshe idonta tayi tare da cewa.
“Ko zamu iya sanin waye akan layi?.”
“Sunana Alhaji Abubakar Ginsau S.A protocol na gwamna, nakira ne kuma Domin na jinjinawa babban Bak’o DR. Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara, agame da maganganu masu amfani daya fad’a, Insha Allahu kuma maganan zata isa ga kunnen way’anda ya kamata suji, sannan muna godiya k’warai matuk’a, da irin shawarwarin daya bayar.”
Kai Jannart ta jinjina, tare da dan satan Kallon Dr Rayyern din, wanda ya kauda kansa gefe, kamar baiji ana yabonsa ba.
“Girman kai rawanin tsiya.”
Tafad’a acikin zuciyarta, Yayinda afili kuwa cewa tayi.
“To S.A protocol muma godiya muke sosai, sannan bakon mu Dakta shima yana godiya.”
Daga haka kuwa kiran S.A din ya katse, wani kiran kuma ya sake shigowa.
Cikin tashin hankali Dr Lukman ya mik’e tsaye, tare dasa hannunsa ya dafe kansa, zuciyarsa cike da takaici yace.
“Lallai wannan yaron ya shallake duk wani tunani na, ba a banza ba ake kiransa da Mai-nasara ba, tunda gashi yayi sara akan gab’a, daga maganansa har S.A da kansa ya kira, ya kuma shaida cewa maganar zata tafi har wajen governor, wannan wanne irin Dan iskan yaro ne? Mai sa'a”.
Cikin tsananin takaici tsana Alhaji Idi Saleh Dakata ya fesar da numfashi tare da cewa.
“Ai yamafi Dan iska wannan yaron da kake gani Dr Lukman, shegen yaro ne kwance-kwance yake mana, da sannu Idan bamu tashi ba, duk sai yabi ya sare mana duk wani reshen mu, b’arna babba yake aikata mana, batare da ko damuwa da hakan yayi ba, Tabbas kuma ya kafu iya kafuwa, da wayannan kalaman nasa masu ratsa zuciya yake yaudarar mutane, waishi ala dole mai tausayin talakawa, yana abu tamkar Dan siyasan da yake barar neman kujerar takara, hmmmm Lallai zanyi maganin wannan yaron, zan kawar dashi kamar yanda na kawar da way’anda suka fishi tsauri a baya.”
Alhaji Idi Sale Dakata ya ƙare mgnar yana me sakin zazzafan numfashin takaici.
Yayinda Alhaji Abdu Tababa kuwa yace.
“Lallai kawar dashi daga doron k’asa shine hanya mafi a’ala, Idan ba haka ba kuwa duk sai ya fito damu waje cikin rana daga gidajenmu.”
“Hakan bazaiyi wuba kuwa.”
Alhaji Idi Sale’n ya fad’a yana me mikewa tsaye.
Yayinda acan gidan su Rayyern kuwa, har yanzu su Abba basu matsa daga gun tv’n ba.
Sunanan zaune kowannensu dauke da farincikin, irin nasaran da Rayyern din ke samu.
Haka ma agidan Barrister Kabir har yanzu shima yana zaune agaban tv’nsa.
Dai-dai lokacin da ake cigaba da haska shirinne kuma, Aunty Dijat ta fito daga daki.
Zama tayi akusa da mijinnata tare da soma kokarin had’a masa coffee.
Kallon ta Barrister Kabir din yayi, kana cikin tausasa murya yace.
“Dijat kalli tv kiga, Jannart da matashin saurayin nan dake zaune agefenta”.
Da sauri ta miƙa mishi cup ɗin tare da zubawa tv ido tare da cewa.
“Masha Allah”.
Kurban coffee'n yayi tare da cewa.
“Sundace ko?.”
Ware ido Aunty Dijat din tayi ta kalli tv’n, dai-dai lokacin kuwa aka sake matso da fuskokin Jannart dana Rayyern din kusa.
“Masha Allah, ai kuwa Abban Hafeez matukar dacewa ma sukayi, kyau da kyau kenan.”
Murmushi Barrister Kabir din yayi, tare da gyara zamansa a takaice yace.
“Shine mijin dana zab’a mata, kuma shine wanda zata aura amma batare da ta sani ba.”
Ya fad’a yana me karb’an coffee din da aka had’asa masa.
Idanu Aunty Dijat ta d’an zaro waje, cike da tsananin mamaki hadi da zallar farinciki tace.
“Allahu Akhbar, Lallai girman Allah iko da buwayarsa tana da yawa, Masha Allah Lallai Jannart ta dace da hazik’in Namiji kuma jarumi, mai dauke da nagarta, Tabbas ka cika Uba nagari, ai kuwa zamusha biki yaushe ne Auren?”
Murmushi Abban yayi, tare da girgiza mata Kai, Ahankali kuma yace.
“A’a bayanzu zan gaya miki ba, abun namu sirrine.”
*GARKUWAR taku ce dai MA'AURATA, da masu shirin aure, da masu jego, da yan gayu masu son k’amshi kece raini, da gyaran da zaike maimaita muku dararen forkon kuruciya*
Ko kunsan Jikinmu na da sinadaran hormones da suke taimakawa dan’adam akan komai musamman lokacin da mace take mu’amalar aure da mijinta. Mafi akasari wannan hormones din ne ke samun matsala ko su yi sanyi koma su daina aiki kwata-kwata shi ne dalilin da zai sa mace tace bata jin sha’awa ko bata san dadin aure ba. Albishirinku ina da kayan da ke taimakawa wannan sinadaran du dawo aiki tukuru don karkato miki da kimarki wajan mai gida sannan su taimakawa wannan sinadaran hormones dinki su dinka secreting din ni’ima wadatacciya da zata taimaka miki ki gamsu mijinki ya gamsu fiye da tunaninki. Note: Kayana ba sa tsinka ruwan ni’ima suna dai taimakawa hormones dinki ne su tsattsafo da ni’imar musamman wacca cutar sanyi ko dattin mahaifa ya dankarar da su ya hana su yin aikinsu yanda ya kamata. Haka zalika idan kina da kyau ki kara da wanka. Zaki iya amfani da magani na na gargajiya wanda zai gyara miki sex hormones din kullum ki kasance cikin humidify wato cikin damshi mai albarka kamar yanda ake son mace. Yana gyara miki mara.
Sai kamshi. Hajiyata daure ki fara amfani da turarena ki ji irin salon kamshin sa salo ne da zai daidaita ki da mijinki ya kankaro miki da kimarki a wajansa. Siyan na gari mayar da kudi gida.
Ga masu buƙata ga number' wayata wanda nake whatsApp dashi 09097853276 kimin mgn ta whatsApp in har kin tabbatar kin shirya saya mu dai-dai ta, kayana ba ƙanana bane, shiyasa bana harkan karanta, muddin kinsan baki shirya sayaba Please kada kiyi min mgn ki bari sai kin shirya kuɗinki a hannu, ba ina nufin kayana bana talaka bane, no akwai ƙananan set na masu karamin karfi, banson aimin mgn a ɓatamin lokacin aiyukana a shirme baki shiryaba. Shine karantan da bana so.
0005388578 Jaiz bank AISHA GARKUWA ALIYU. In kin shirya ga number ta ga kuma account number ta wanda in mun gama mgn zaki turo kudin ki, kana insa miki kaya a mota, duk ƙasar da kike kayana zaije gareki, amman fa in kinada dalilin zuwan nasune🤝🏻sayan na gari meda kudi gida.
GARKUWAR MA'AURATA
By
*GARKUWAR FULANI*
Murmushin Jin dadi Aunty Dijat din tayi, kana cikin sakin fuska tace.
“Alhamdulillah nidai ko yaushene ma ina jira.”
Barrister Kabir dinma murmushi yayi, batare kuma daya sake cewa komai ba, ya cigaba da shan coffee d’insa.
Acan cikin tashar kuwa, zuwa yanzu kira na 15 kenan Jannart din ta amsa, wanda kuma daga kan kira na 15 dinne ta katse layin gaba d’aya, tare da d’agowa ta kalli cameras din dake jere agabansu.
“To masu kallonmu laifin dadi dai ance karewa, Domin naga lokaci yana daga mana hannu, saboda haka duka duka anan muka kawo k’arshen shirin namu Na Bak’on Mako, sai kuma wani sati Idan mai kowa mai komai ya kaimu, Insha Allah zamu sake zuwar muku da wani bak’on na musamman.”
Dan Juyowa tayi ta kalli Rayyern dake zaune, Cikin kuma sakin fuska kamar yanda ta sabayiwa kowa tace.
“Doctor ayiwa masu kallo da sauraronmu sallama.”