Sashe 4
Tubali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Alhaji Yawale ne ya gyara zamanshi tare da cewa.
"Yaron nan fa yanayi mana illa ba tare da mun ankare ba.
Gaba ɗaya ya rarake tubalin da mukayi tsawon shekaru muna ginawa muna samun wuri na jawo mana wuri."
Cikin tsananin takaici Alhaji Abdu Tababa ne yace.
"Tun-tuni nake gaya muku haka.
Mu kauda yaron nan a doron ƙasa shine kawai mafi sauƙin mu.
Kunaga yadda kasuwan cinsa ke haɓaka, kamfanonin sa suna bunƙasa daga Arewacin Nigeria har ya koma kudanci ya kafu.
Uwa uba yanzu duk ƙasashen Afrika yanada rassai.
Ya maida kayan abinci da araha tamkar ruwan sama cikin damuna.
Duk inda ka shiga a kasuwannin Mai-nasara race, ke cike.
A farashi mai sauƙi ta yaya za'ayi a saurari kayan kamfanonin mu".
Ɗaya daga cikinsu ne ya miƙe tsaye tare da cewa.
"Ni tambaya ta a kullum ma shine
menene Tubalin kasuwancin yaron nan?
Yaushema aka haifeshi? Sa'an yaran cikin mune fa!
Ta ina ya samu Wannan tarin dukiyar da har ya samu damar razana mana kasuwanci ya raunata mana Company's.
Yaushe yayi ginin duk a lokacin ɗaya menene Tubalin dukiyarsa da matakan ikonsa!?."
Ya ƙare maganar yana kallon Bala Tambari wanda shine shugaban tsare-tsaren ginin masana'antu a gwamnatance, dole sai yasa hannu za'ayi gini ya za'ayi ka bashi izini da damar yin gini a duk inda yake so a ƙasar nan".
Cikin takaici Bala Tambari ya fesar da numfashi tare da cewa.
"Tsohon yarjejeniya ne, yana da dukkan abin buƙata, yanada sa hannun da suka gabaceni kuma kan tsari suke.
Naso in ƙalu balanceshi.
Tun shekaru biyar baya lokacin da ya fara gina babban campany dake Nan birnin Kano wanda yanzu yake gab da kammalashi so naga komai da hujja yakeyi.
Yaron shegen taurin kai ne dashi, gashi da ɗan banzan tsaurin ido.
Kana mgna zai tsira maka waɗannan siraran idanun nashi masu kama da soyayyan gujjiya, tsakar idon ka ya baka amsa da hujjar da baka isa kayi mgna ba".
Dr.Lukman ne ya fesar da iska a baki tare da cewa.
"Ni ta ko ina ya tosheni
A fannin likitancin gaba ɗaya yana bi yana rarake privet Hospitals.
Ɗan banzan komai na asibitinsa mai sauƙi kuma ga kula ya za'ayi aje irin namu asibitocin."
Alhaji idi Sale Dakatane ya miƙe a fusacen shina kana yace.
"Nifa gaba ɗaya ya ta'azzara min campany na na shinkafa.
Sannan kafin kace ka motsa sai ka samu ya toshe ko ina.
Hegen yaro mai jajayen kunnuwa.
Yana nan tamkar Wahainiya, samun ganinshi ma ya zamewa mutun aiki."
Dr Lukman ne ya ɗan sauƙe numfashi tare da cewa.
"Cikin satin nan zai dawo Nigeria yanzu haka yana Ethiopia yaje, shugaban kasar can da kanshi da manyan likitocin sune, suka karrama shi.
Sabida taimakon da yayiwa wasu daga cikin mutanen ƙasar Ethiopia cikin Airport kan hanyarsa ta zuwa US, dan karramashi a matsayin ɗan kasuwan da yafi ko wanne sauƙin farashin kayan masarufi.
Kaga yana tafi kuma yazo wai kuma Ethiopia zasuyi mishi wata karramawar.
Yaro kamar ɗan ruwa, komai yasa kai sai Nasara".
Bala Tambari ne, ya kalleshi tare da cewa.
Toh yanzu dole kai zaka nema mana zama dashi.
Yana dawowa muna buƙatar shi mu gwada sayan farashinsa.
Muyi mishi tayin harƙallarmu yasan irin ribar da muke shigarwa, wata ƙil zai amince mu haɗa hannu in kuma yaƙi tabbas zamu gina mishi gadar zare.".
Da sauri Alhaji Idi Sale Dakata yace.
"Uhumm ai In Kuma yaƙi amincewa mu haɗa hannu.
Toh lokacin wasan zai fara, dan in taurin kaine da gsky da samun ƙarfin iko bai kai.
Mai-gaskiya da wasu ba, da muka gama dasu shekaru ashirin da biyu baya ba, danni cinnaka ne ban bar na gida Bama, bare shi baare."
Haka dai suka tashi a taron nasu.
A nufin sai ya dawo su zauna dashi.
A cikin gidan kuwa. Jannart ce ke
Tsaye a kitchen, inda take sanye da wani half gown mai masifar kyau wanda ya d’an bayyana fararen legs d’inta, rigar irin mai kauri da kama fatar jiki dinnan ne, wanda hakanne kuma yasa had’add’iyar Surar jikinta dan bayyana, kasancewarta y’ar gayu, Tabbas Jannart macece mai matuk’ar son fashion, shiyasa hatta suturun da take sawa ya banbanta da sauran na y’an Nigeria, saboda sometimes tafi yin shiga irin na wasu daga cikin larabawa, ko kuma shigar mutanen turkey🇹🇷.
Tsaye take a kitchine din cikin kuma nutsuwa take aikinta.
Yayinda Mom ke tsaye a gefenta.
Cikin kula Mom ta kalleta tare da cewa.
"Jannart kamar Yayanki ne ke kiranki".
Cikin bugawar zuciya tace.
"Yah Junaid!?."
Da sauri tace.
"Eh shi dai".
Bugawa zuciyarta ya kumayi, tare dajin wani iri acikin jikinta, saidai kuma babu yanda ta iya, haka ta juya cikin sanyi ta nufi falon.
Can tsakar falon ta hangoshi tsaye, saurayi ne, mai murd’addiyar Surar jiki da kuma tarin gashi akansa irin busu-sun nan, duk da cewar kyawun nasa bawani na zarce hankali bane amma baza’a tab’a k’iransa da mummuna ba, wata riga
marar hannuce ajikinsa, sai kuma wondon dake jikinsa wanda ya tsaya masa iya guywa.
Bisa alamu kuma yanzu ya tashi daga bacci.
saboda yanda idanunsa sukayi jazir.
Kallonta yayi, tare kuma da d’an cije labb’ansa, still Cikin binta da wani irin mayataccen kallo yace.
"Kije ki share min ɗakina".
Fuskarta ta d’an b’ata cikin kuma tsanar shiga ɗakin nashi tace.
"Yah Junaid breakfast nake haɗa mana".
A fusace ya juyo kanta cikin takaicin abubuwan dake haɗe mishi a kanta ya yarfa mata wani irin gigitaccen mari a kan kunneta na dama, saida ya bada wani irin sauti ƙauuuuu! Da ɗan karen ƙarfi.
A gigice tasa tafin hannunta ta tallabe ƙuncin ta.
Yayinda wasu taurari suka fara gilma mata a gani.
In da sabo yaci ace fuskarta ta saba da marukan Yah Junaid Wanda tun tana yarinya take shansu gashi sanadin su, kunnuwanta sun samu matsala jinta ya raunata.
Wasu irin hawaye ne masu masifar zafine suka silalo mata.
Ba tare da tace komaiba ta juya ta nufi ɗakin shi.
Ta yaya zuciyarta zata samu sauƙin ɗan uwanta da take bata da wani sama dashi tunda shine suke uwa ɗaya uba ɗaya amman yafi kowa tsanarta a duniya.
Ba shaƙuwa ko tausayawa a tsakaninsu.
Sannan mahaifinsu babu ruwanshi ko a gabanshi Junaid zai daketa babu ruwanshi sai yayi kamar baya wurin ma.
In Mom tayi mgna ya gwatsaleta yace babu ruwanta sunfi kusa.
Wannan ne ya ƙara tsananta zubda hawayen ta.
A haka ta fara tattara mishi falon da gaba ɗaya ya birkitashi.
Shigowa yayi ya zauna yana mai Binta da ido, duk inda tayi.
Wani irin abu yakeji a kanta.
A hankali ya miƙe yabi bayanta lokacin da ta shiga Bedroom.
Da sauri ta juyo jin shigowarsa.
Gefenta ya matso fuska a murtuke hakan ne yasa bugun zuciyarta ya ƙara tsananta.
Har kana iya ganin yadda numfashin ta ke fita da yanayin tsoro.
Fuska ya kuma murtukewa.
Kana yace.
"Munafuka, sai kace da gaske haka kike tsoron maza, ji yadda kike tafiya ba bra kina wani karkakaɗa ƙirji irin ke gaki ƴar iska mai son maza ko?."
Idanunta ta rumtse da k’arfi cikin kuma ƙunan ran ƙazafin da Yah Junaid ke jifarta dashi murya na rawa tace.
"A'a".
Cikin haɗe fuska ya daka mata tsawa tare da cewa.
"Toh meya hanaki sa bra?".
Murya na rawa tace.
"Dr. Lukman ne yace in daina sa bra, sabida matsalar numfashin da Athsman ɗina ke jamin. In nasa ya matse min ƙirji sai numfashina yayi ta shaƙewa".
Wani irin dogon tsaki yaja tare da cewa.
"Ubanki zanci in baki dena raina min hankali ba, matse ƙirjin da ƙatti keyi bai shaƙe numfashin ba sai saka bra ne zai cushe miki numfashin."
Fice min da gani!!". Ya k’are maganar a tsawace.
Jin hakanne kuma yasa da sauri ta juya ta fita, hawaye na zubo mata sabida raɗaɗin marin daya yarfa mata da zafin kalaman zargi da yake binta dasu.
A falo ta samu Mom da sauri ta faɗa jikinta.
Cikin sakin sassayan kuka tace.
"Mom ki gaya musu wlh ni ba yar iska bace, Meyasa Mom Meyasa Ya Junaid ke jifana da mugayen maganganu, shifa yaya nane..”
Jawo hannunta Mom tayi suka zauna bisa kujera, a hankali tasa tafin hannunta tana share mata hawaye cikin yin ƙasa da murya tace.
"Na sani Jannart kuma Allah ya sani, ke ba ƴar iska bace. Yaushe ma kika samu sakewar rayuwar duniya kullum kina cikin takunkumi.
Ko ina zakije da masu gadinki.
Na rasa wannan masifar tsaron na menene kina girma ana ƙara killaceki kamar abun rashin gsky."
Cikin shessheƙan kuka tace.
“Mom shi Yah Junaid gani yake, su masu tsaron nawa dasu nake iskanci.
Daddy Kuma gani yake in ya cire masu tsaron da wasu zanyi iskanci.
Wlh na sani Mom bawai dan tsaron lfyata bane yasa Daddy ware min masu tsaro.
Shima zargina yakeyi ko Mom?".
Jin yadda numfashin ta ke fitane yasa mom gyara zamanta kana ta fuskanceta da kyau.
Allah ya sani tana son Jannart tamkar ƴar cikinta.
Amman duk yadda zatayi bata burge Alhaji Idi da Junaid, gani suke kamar so take Jannart ta lalace ne don ba ita ta haifeta ba.
Cikin kula da tausasawa uƙubar da suke shayar da ita tace.
"A'a Jannart Daddynku baya zarginki, shi ya bada masu tsaronkine sabida larurar ciwonki, kina buƙatar makusanci a koda yaushe, tunda abu kaɗan ke tada miki athsman ɗin wanda kinga tun da yana nimoniya, kina girma yana canzawa ya riƙa har ya zama asman shiyasa yake tsananta kulawa a kanki.
Sabida abu kaɗan ke tada miki shi.
Kuma Yah Junaid ɗinki yana sonki.
Ɗan uwa, uwa ɗaya uba ɗaya ya wuce wasa.
Sun haɗa da son da Mamanki zatayi mikine da tana raye".
Cikin zubda hawaye tace.
"Mom kin bani son da ya kamata uwa ta bawa ƴarta, ni banyi maraicin kyakkyawan tarbiyar uwa ta gari ba.
Kawai dai basa so nane".
Cikin kafeta da ido Mom tace.
"Jannart ki yarda dani, tashi muje kici abinci".
Cikin nitsuwa tasa hannunta ta share hawayenta kana ta miƙe.
Dinning area suka nufa.
Suna zama Daddy ya fito da hakama Junaid da Abdul.
Nan suka zauna sukayi breakfast.
A hankali ta sauke numfashi ganin Junaid ya miƙe ya bar wurin.
"Yaron nan fa yanayi mana illa ba tare da mun ankare ba.
Gaba ɗaya ya rarake tubalin da mukayi tsawon shekaru muna ginawa muna samun wuri na jawo mana wuri."
Cikin tsananin takaici Alhaji Abdu Tababa ne yace.
"Tun-tuni nake gaya muku haka.
Mu kauda yaron nan a doron ƙasa shine kawai mafi sauƙin mu.
Kunaga yadda kasuwan cinsa ke haɓaka, kamfanonin sa suna bunƙasa daga Arewacin Nigeria har ya koma kudanci ya kafu.
Uwa uba yanzu duk ƙasashen Afrika yanada rassai.
Ya maida kayan abinci da araha tamkar ruwan sama cikin damuna.
Duk inda ka shiga a kasuwannin Mai-nasara race, ke cike.
A farashi mai sauƙi ta yaya za'ayi a saurari kayan kamfanonin mu".
Ɗaya daga cikinsu ne ya miƙe tsaye tare da cewa.
"Ni tambaya ta a kullum ma shine
menene Tubalin kasuwancin yaron nan?
Yaushema aka haifeshi? Sa'an yaran cikin mune fa!
Ta ina ya samu Wannan tarin dukiyar da har ya samu damar razana mana kasuwanci ya raunata mana Company's.
Yaushe yayi ginin duk a lokacin ɗaya menene Tubalin dukiyarsa da matakan ikonsa!?."
Ya ƙare maganar yana kallon Bala Tambari wanda shine shugaban tsare-tsaren ginin masana'antu a gwamnatance, dole sai yasa hannu za'ayi gini ya za'ayi ka bashi izini da damar yin gini a duk inda yake so a ƙasar nan".
Cikin takaici Bala Tambari ya fesar da numfashi tare da cewa.
"Tsohon yarjejeniya ne, yana da dukkan abin buƙata, yanada sa hannun da suka gabaceni kuma kan tsari suke.
Naso in ƙalu balanceshi.
Tun shekaru biyar baya lokacin da ya fara gina babban campany dake Nan birnin Kano wanda yanzu yake gab da kammalashi so naga komai da hujja yakeyi.
Yaron shegen taurin kai ne dashi, gashi da ɗan banzan tsaurin ido.
Kana mgna zai tsira maka waɗannan siraran idanun nashi masu kama da soyayyan gujjiya, tsakar idon ka ya baka amsa da hujjar da baka isa kayi mgna ba".
Dr.Lukman ne ya fesar da iska a baki tare da cewa.
"Ni ta ko ina ya tosheni
A fannin likitancin gaba ɗaya yana bi yana rarake privet Hospitals.
Ɗan banzan komai na asibitinsa mai sauƙi kuma ga kula ya za'ayi aje irin namu asibitocin."
Alhaji idi Sale Dakatane ya miƙe a fusacen shina kana yace.
"Nifa gaba ɗaya ya ta'azzara min campany na na shinkafa.
Sannan kafin kace ka motsa sai ka samu ya toshe ko ina.
Hegen yaro mai jajayen kunnuwa.
Yana nan tamkar Wahainiya, samun ganinshi ma ya zamewa mutun aiki."
Dr Lukman ne ya ɗan sauƙe numfashi tare da cewa.
"Cikin satin nan zai dawo Nigeria yanzu haka yana Ethiopia yaje, shugaban kasar can da kanshi da manyan likitocin sune, suka karrama shi.
Sabida taimakon da yayiwa wasu daga cikin mutanen ƙasar Ethiopia cikin Airport kan hanyarsa ta zuwa US, dan karramashi a matsayin ɗan kasuwan da yafi ko wanne sauƙin farashin kayan masarufi.
Kaga yana tafi kuma yazo wai kuma Ethiopia zasuyi mishi wata karramawar.
Yaro kamar ɗan ruwa, komai yasa kai sai Nasara".
Bala Tambari ne, ya kalleshi tare da cewa.
Toh yanzu dole kai zaka nema mana zama dashi.
Yana dawowa muna buƙatar shi mu gwada sayan farashinsa.
Muyi mishi tayin harƙallarmu yasan irin ribar da muke shigarwa, wata ƙil zai amince mu haɗa hannu in kuma yaƙi tabbas zamu gina mishi gadar zare.".
Da sauri Alhaji Idi Sale Dakata yace.
"Uhumm ai In Kuma yaƙi amincewa mu haɗa hannu.
Toh lokacin wasan zai fara, dan in taurin kaine da gsky da samun ƙarfin iko bai kai.
Mai-gaskiya da wasu ba, da muka gama dasu shekaru ashirin da biyu baya ba, danni cinnaka ne ban bar na gida Bama, bare shi baare."
Haka dai suka tashi a taron nasu.
A nufin sai ya dawo su zauna dashi.
A cikin gidan kuwa. Jannart ce ke
Tsaye a kitchen, inda take sanye da wani half gown mai masifar kyau wanda ya d’an bayyana fararen legs d’inta, rigar irin mai kauri da kama fatar jiki dinnan ne, wanda hakanne kuma yasa had’add’iyar Surar jikinta dan bayyana, kasancewarta y’ar gayu, Tabbas Jannart macece mai matuk’ar son fashion, shiyasa hatta suturun da take sawa ya banbanta da sauran na y’an Nigeria, saboda sometimes tafi yin shiga irin na wasu daga cikin larabawa, ko kuma shigar mutanen turkey🇹🇷.
Tsaye take a kitchine din cikin kuma nutsuwa take aikinta.
Yayinda Mom ke tsaye a gefenta.
Cikin kula Mom ta kalleta tare da cewa.
"Jannart kamar Yayanki ne ke kiranki".
Cikin bugawar zuciya tace.
"Yah Junaid!?."
Da sauri tace.
"Eh shi dai".
Bugawa zuciyarta ya kumayi, tare dajin wani iri acikin jikinta, saidai kuma babu yanda ta iya, haka ta juya cikin sanyi ta nufi falon.
Can tsakar falon ta hangoshi tsaye, saurayi ne, mai murd’addiyar Surar jiki da kuma tarin gashi akansa irin busu-sun nan, duk da cewar kyawun nasa bawani na zarce hankali bane amma baza’a tab’a k’iransa da mummuna ba, wata riga
marar hannuce ajikinsa, sai kuma wondon dake jikinsa wanda ya tsaya masa iya guywa.
Bisa alamu kuma yanzu ya tashi daga bacci.
saboda yanda idanunsa sukayi jazir.
Kallonta yayi, tare kuma da d’an cije labb’ansa, still Cikin binta da wani irin mayataccen kallo yace.
"Kije ki share min ɗakina".
Fuskarta ta d’an b’ata cikin kuma tsanar shiga ɗakin nashi tace.
"Yah Junaid breakfast nake haɗa mana".
A fusace ya juyo kanta cikin takaicin abubuwan dake haɗe mishi a kanta ya yarfa mata wani irin gigitaccen mari a kan kunneta na dama, saida ya bada wani irin sauti ƙauuuuu! Da ɗan karen ƙarfi.
A gigice tasa tafin hannunta ta tallabe ƙuncin ta.
Yayinda wasu taurari suka fara gilma mata a gani.
In da sabo yaci ace fuskarta ta saba da marukan Yah Junaid Wanda tun tana yarinya take shansu gashi sanadin su, kunnuwanta sun samu matsala jinta ya raunata.
Wasu irin hawaye ne masu masifar zafine suka silalo mata.
Ba tare da tace komaiba ta juya ta nufi ɗakin shi.
Ta yaya zuciyarta zata samu sauƙin ɗan uwanta da take bata da wani sama dashi tunda shine suke uwa ɗaya uba ɗaya amman yafi kowa tsanarta a duniya.
Ba shaƙuwa ko tausayawa a tsakaninsu.
Sannan mahaifinsu babu ruwanshi ko a gabanshi Junaid zai daketa babu ruwanshi sai yayi kamar baya wurin ma.
In Mom tayi mgna ya gwatsaleta yace babu ruwanta sunfi kusa.
Wannan ne ya ƙara tsananta zubda hawayen ta.
A haka ta fara tattara mishi falon da gaba ɗaya ya birkitashi.
Shigowa yayi ya zauna yana mai Binta da ido, duk inda tayi.
Wani irin abu yakeji a kanta.
A hankali ya miƙe yabi bayanta lokacin da ta shiga Bedroom.
Da sauri ta juyo jin shigowarsa.
Gefenta ya matso fuska a murtuke hakan ne yasa bugun zuciyarta ya ƙara tsananta.
Har kana iya ganin yadda numfashin ta ke fita da yanayin tsoro.
Fuska ya kuma murtukewa.
Kana yace.
"Munafuka, sai kace da gaske haka kike tsoron maza, ji yadda kike tafiya ba bra kina wani karkakaɗa ƙirji irin ke gaki ƴar iska mai son maza ko?."
Idanunta ta rumtse da k’arfi cikin kuma ƙunan ran ƙazafin da Yah Junaid ke jifarta dashi murya na rawa tace.
"A'a".
Cikin haɗe fuska ya daka mata tsawa tare da cewa.
"Toh meya hanaki sa bra?".
Murya na rawa tace.
"Dr. Lukman ne yace in daina sa bra, sabida matsalar numfashin da Athsman ɗina ke jamin. In nasa ya matse min ƙirji sai numfashina yayi ta shaƙewa".
Wani irin dogon tsaki yaja tare da cewa.
"Ubanki zanci in baki dena raina min hankali ba, matse ƙirjin da ƙatti keyi bai shaƙe numfashin ba sai saka bra ne zai cushe miki numfashin."
Fice min da gani!!". Ya k’are maganar a tsawace.
Jin hakanne kuma yasa da sauri ta juya ta fita, hawaye na zubo mata sabida raɗaɗin marin daya yarfa mata da zafin kalaman zargi da yake binta dasu.
A falo ta samu Mom da sauri ta faɗa jikinta.
Cikin sakin sassayan kuka tace.
"Mom ki gaya musu wlh ni ba yar iska bace, Meyasa Mom Meyasa Ya Junaid ke jifana da mugayen maganganu, shifa yaya nane..”
Jawo hannunta Mom tayi suka zauna bisa kujera, a hankali tasa tafin hannunta tana share mata hawaye cikin yin ƙasa da murya tace.
"Na sani Jannart kuma Allah ya sani, ke ba ƴar iska bace. Yaushe ma kika samu sakewar rayuwar duniya kullum kina cikin takunkumi.
Ko ina zakije da masu gadinki.
Na rasa wannan masifar tsaron na menene kina girma ana ƙara killaceki kamar abun rashin gsky."
Cikin shessheƙan kuka tace.
“Mom shi Yah Junaid gani yake, su masu tsaron nawa dasu nake iskanci.
Daddy Kuma gani yake in ya cire masu tsaron da wasu zanyi iskanci.
Wlh na sani Mom bawai dan tsaron lfyata bane yasa Daddy ware min masu tsaro.
Shima zargina yakeyi ko Mom?".
Jin yadda numfashin ta ke fitane yasa mom gyara zamanta kana ta fuskanceta da kyau.
Allah ya sani tana son Jannart tamkar ƴar cikinta.
Amman duk yadda zatayi bata burge Alhaji Idi da Junaid, gani suke kamar so take Jannart ta lalace ne don ba ita ta haifeta ba.
Cikin kula da tausasawa uƙubar da suke shayar da ita tace.
"A'a Jannart Daddynku baya zarginki, shi ya bada masu tsaronkine sabida larurar ciwonki, kina buƙatar makusanci a koda yaushe, tunda abu kaɗan ke tada miki athsman ɗin wanda kinga tun da yana nimoniya, kina girma yana canzawa ya riƙa har ya zama asman shiyasa yake tsananta kulawa a kanki.
Sabida abu kaɗan ke tada miki shi.
Kuma Yah Junaid ɗinki yana sonki.
Ɗan uwa, uwa ɗaya uba ɗaya ya wuce wasa.
Sun haɗa da son da Mamanki zatayi mikine da tana raye".
Cikin zubda hawaye tace.
"Mom kin bani son da ya kamata uwa ta bawa ƴarta, ni banyi maraicin kyakkyawan tarbiyar uwa ta gari ba.
Kawai dai basa so nane".
Cikin kafeta da ido Mom tace.
"Jannart ki yarda dani, tashi muje kici abinci".
Cikin nitsuwa tasa hannunta ta share hawayenta kana ta miƙe.
Dinning area suka nufa.
Suna zama Daddy ya fito da hakama Junaid da Abdul.
Nan suka zauna sukayi breakfast.
A hankali ta sauke numfashi ganin Junaid ya miƙe ya bar wurin.