Sashe 28
Tubali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yana zuwa kuwa ya zauna akan wata kujerar silver mai daukar mutun uku,
Sunkuyowa yayi tare da bud’e jakan daya shigo da ita ya zaro bottle water, b’alle murfin goran yayi, kana ya soma zubawa akan tarin sumar dake kansa wanda yake jin zufa na tsastsafo mishi.
Jin da yayi baisamu gamsuwa bane kuma yasashi karkad’a gashin kannasa dan yadda ruwan zai taɓa fatar kansa, wanda hakan yasa har ruwan dake kan nasa ya watsu akan fuskar Jannart.
Salman dake tsaye kuwa dan matsowa yayi, tare da gaishe da Rayyern d’in.
Batare kuma daya dago ba ya amsawa Salman d’in atakaice.
Idanu Salman yayiwa Rayyern dake tsaye, alaman ta gaishe shi.
D’an k’aramin bakinta ta turo gaba tare dasa hannunta ta goge ruwan daya watsa mata, kana asanyaye tace.
“Ina wuni.”
Shiru yayi bai amsa taba, tare dayin kamar ma baijita ba.
“Ina wuni.”
Jannart d’in ta sake fad’a akaro na biyu.
still shiru yasakeyi kamar baijita ba.
“Kibashi hakuri.”
Salman dake tsaye ya fada kasa-kasa.
Karamin bakinta ta sake turowa, cikin kuma wata irin murya mai kama da shagwab’a, sakalci, sanyi da kuma tsoro tace.
“Kayi hakuri please, ranan nayi maka b’arna amma bada sanina nayi hakan ba, Dan Allah da Manzonsa kayi hakuri.”
Idanunsa yadan lumshe saboda jin ta had’asa da sunan Allah da Manzonsa ne kuma, yasashi gyaɗa mata kai alaman yayi.
“Nagode.” Ta fad’a asanyaye.
Shikuwa Salman ganin hakanne ya sashi dan matsowa, cikin neman alfarma yace.
“Dan Allah ranka ya dad’e tambaya mukeyi.”
D’ago Kai Rayyern din yayi ya kalli Salman din afakaice.
Batare kuma dayace komai ba ya maida kansa k’asa tare da ɗaukan ɗan karamin towel ɗin dake gefe ya fara goge suman kanshi zuwa wuyanshi da fuskarshi da sajenshi da ruwan ya jiƙa.
Salman kuwa ganin hakanne yasashi Kallon Jannart, wanda gaba d’aya mood dinta ya sanja,tun lokaci da taga kamar dokin zai takesu ta soma sakin wani irin numfashi sama-sama a hankali.
Wanda da dukkan alama kuma tsoritan da tayi dazunne yakeson tayar mata da ciwon ta.
Sanin yanda ciwon keyi mata idan ya tashi ne kuma yasa, Salman din cewa.
“Subahanallah Jannart ciwonki ko?.”
Kai ta gyaɗa mishi cikin jawo ajiyan zuciya da take son yi.
Cikin kula ya nuna mata gefen Rayyern dan babu wata kujerar a nan kusa dasu.
"Maza ga waje ki zauna.”
Ya kare maganan yana meyi mata
Nuni da d’an gefen Rayyern, wanda kuma dama wajen zaman daya rage din bai wuce na zaman mutum daya ba sabida ya ajiye tarkacensa a wajan zaman mutun ɗaya gashi kuma a ɗaya wojen.
Jannart kuwa kasancewar dama ta gaji da tsayuwa kuma ga numfashin ta dake fizga ne yasa, batare da ta musa ba ta zauna awajen sanin in ta zauna zai iya dai-dai-ta.
Shikuwa Salman ƙara matsosu yayi.
Tare da sake maimaita maganarsa ta dazu.
“Dan Allah ranka ya dad’e tambaya mukeyi.”
“Inaji.”
Rayyern din ya fada agajarce, nan ma saboda yaji Salman din ya hadashi da Allah ne.
"Dan Allah wani mutum muke nema".
Uhum ya kuma cewa a taƙaice.
Gyara tsayuwa Salman yayi tare da cewa.
" Sunan shi Dr. Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara.
Shi muke nema, munje Hospital d’insa ne aka tabbatar mana da cewa Lallai-Lallai yana nan, shine muke tambaya dan Allah koka sanshi?”
Ad’an fakaice Rayyern din ya kalli Salman, saidai kuma cikin halin nuna ko inkula yace.
“Meyasa kuke nemanshi me zai muku? Wa yace muku yana nan?.”
Jannart dake dan haki ne taja ajiyan zuciya ta fizogishi da ɗan ƙarfi kana tace.
“Mitssss mutun sai rashin gsky, gaba ɗaya ya wahal damu."
Ta wutsiyar idonshi ya ɗan kalleta a fizge.
Ita kuwa ci ga da cewa tayi.
"Nemansa kawai mukeyi, wallahi daga yanzu kuma ni nagaji,
Dan bazan zauna inyi ta neman wani can ƙato baƙi mummuna mai ƙaton tumbi ba dan yayi kuɗi yana jin kansa waya masan TUBALI kuɗin nashi ko na haram ne shiyasa yake tsoron yin ido huɗu damu ƴan jaridu.
Kada ya gaza amsa mana tambayoyinmu."
Numfashin ta fesar a hankali jin ya dai-dai ta.
Salman nata jujjuya mata kai ina bata ganiba bare tasawa bakinta linzamin.
Tsaki ta ɗan ja tare da ci gaba da cewa.
"Mutumin nan ya wahalar damu sosai, na farko dai shiba kudi ba, amma na lura kudi yafi saukin samu akanshi.”
Alama Salman ya mata akan tayi shiru, da yin gyaran murya.
hakanne kuwa yasa tayi shirun.
Shikuwa Rayyern tunda ta fara maganan yake kallonta ta wutsiyar idanunsa baki cai-cai.
Salman kuwa gyara tsayuwarsa yayi, tare da fadin.
“Mu yan jarida ne kuma ma’aikatan tashar Arewa24, munzo nanne domin samun daman yin hira dashi, Lallai kuma muna da buk’atar ganinsa.
Domin rashin samun tattaunawa dashi ɗin, dai-dai yake da rasa aikin mu.”
Fuska Rayyern din yadan tab’e tare da cewa.
“Uhummm.” Atakaice.
Jin hakanne kuma yasa jikin Salman yin sanyi, still cikin yanayin dake bayyana damuwarsa yace.
“Dan Allah In dai kasan hanyar da zanbi wajen ganinsa ka taimaka min, Banason rasa aikina, inason aikina sosai, Dan Allah Idan ka sanshi, ko kuma kasan inda zan sameshi ka fad’amin, domin da wannan aikin kad’ai na dogara, dashi ne kuma nake ciyar da iyalaina da iyayena, dan Allah ka taimaka kada in rasa aikina.”
Tabbas Salman ya karyo lagonsa tunda ya hadashi da Allah da kuma nuna masa aikin shine mafogararsa, Idanunsa yadan lumshe ahankali, batare kuma daya kalli daya daga cikinsu ba yace.
“Naji badamuwa amma dai yanzu kam bayanan, Zan gaya masa idan ya amince shikenan, zan kawoshi har cikin tashan Arewa24 din kuyi mishi duk tambayar da kukeso.”
Farinciki da tsananin jindadi ne ya lullub’e cikin zuciyar Jannart da Salman.
Cikin bayyana zallan jin dadi Salman yace.
“Mungode sosai ranka ya dad’e, mungode kwarai, saidai amma dama ka sanshi ne?”
Kansa ya jinjina tare da cewa.
“Eh nasanshi uban gidanane zan gaya masa Insha Allah kuma zaizo zan roƙeshi in gaya masa uzurinka bisa tausayawarsa kan kada ka rasa aikinka da kake kula da ilanka zaizo in Sha Allah.”
Murmushi Jannart dake gefe tayi, tare da lumshe idanunta saboda wani irin sanyi da taji acikin zuciyarta sai kuma ta ɗan gyara zamanta.
Shikuwa Salman cikin tsananin jin daɗi yace.
“Sir! Nagode! Nagode!! sosai!!! Dan Allah kayi mishi magana, ni kuma zan tsumayeka har zuwa nan da y’an wasu kwanaki, wallahi Banason rasa aikina yau kuma saura kwana takwas za'ayi hirar dashi ranar Alhamis na sama.”
Kai Rayyern din ya jinjina, tare da sake cewa.
“Insha Allah zaizo.”
“Ka tabbatar zaizo?”
Jannart da nutsuwa ya dan fara sauka azuciyarta ta fad’a.
Dan juyawa yayi ya watsa mata harara, cikin zuciyarsa kuwa cewa yayi.
“Oho bansani ba shegen baki.”
Salman da farinciki ya cika zuciyarsa kuwa, cewa yayi.
“Mungode sosai amma dan Allah in ba matsala ka bamu numbern ka saboda idan zaizo din musani.”
Kansa yadan girgiza, cikin kuma rashin sabonsa da yawan magana yace.
“No kai dai ka bani taka numbern.”
To Salman yace Cikin gaggawa kuma ya bashi numbernsa.
Mikewa tsaye yayi fuskarsa cike da farinciki yace.
“Alhamdulillah Jannart taso mutafi Insha Allah yanzu kam na samu full confidence.”
Yayi maganar yana me soma tafiya, saboda tsananin farincikin da yake ciki kuwa bai majira Jananrt dinba.
Jannart kuwa ganin Salman din ya soma tafiya ne yasa ta mik’ewa tsaye itama.
Tashin nata kuwa yayi dai-dai da juyowan Rayyern inda ya sauke idanunsa Akan bayanta.
Da sauri ya rumtse idanunshi da ƙarfi tare da kame jikinsa sabida yadda yaji tsikar jikinshi na mimmiƙewa yana tashi tsaye.
Sabida a bunda ya gani ajikinta.
Yadda yaji tsikar jikinshi na tashi ne ya kuma sashi buɗe idanunsa.
Damatsan hannunsa ya kalla gaba ɗaya tattausan gargasar jikinsa ta miƙe tsaye.
Ita kuwa Jannart taku ta farayi da nufin bin bayan Salman wanda haka yasa ta ƙara matsowa gabanshi tana takun dake juya kyawawan mazaunanta.
Fuskarshi ya kuma yamutsawa.
Tare da saurin kawar da kansa gefe.
“Meye haka?”
Ya fad’a azuciyarsa yana mai jin kamar ana tsikarinsa
Jannart kuwa da batasan komai ba, ahankali ta soma dan takawa.
"Ta yaya mace zata kasa sanin ranakun al'adar ta? Ko ta kasa kimtsa kanta har ya fito ya ɓata mata sutura?".
Yayiwa kansa tambayoyin a jere.
"Miteeeew". Ya kuma jan gajeren tsaki.
"Daga nan zuwa parking lot mutun nawa zata sa suga jininta, maza nawa zasu ganta a haka, yanzu ita in an barta wai mai hankali ce ko? Waɗanne irin iyayene gareta da zasu barta kara zube da irin wannan shigar, na tabbatar da suturarmu ta hausa fulani tasa baza'a gane lalacewar kayan jikinta da wuriba kamar wannan tsukekken farin wondon pallozo ɗin ko ya ɓata mata jiki hijabinta zai kareta."
Yayi kalaman a saman harshensa.
A hankali ya ɗan juyo ya kalleta tana mai ci gaba da tafiya.
"Ko ba komai musulmace yana da kyau ta suturce kanta".
Ya faɗa yana kallon yadda take jujjuyawa tamkar Wahainiya.
Sai-dai bai wuce taku goma tayi ba zuwa sha biyu.
Taji muryarsa ta ratsa dodon kunnenta.
Inda yace “Stop.” Cikin wata irin kakkauran murya.
Aikuwa cak ta tsaya saidai kuma Sam ta kasa juyawa ta kalleshi.
Shikuwa Rayyern fuskarsa ya sake had’ewa, tare da yamutsaawa dan ji yake tamkar zaiyi amai kana ahankali ya juyo ya kalli alkyabbar shi dayake gefenshi.
A hankali yasa hannunshin ya d’auki alkyabban.
Ya tashi tsaye kana ya fara taku a nitse.
Har lau bata juyoba kuma bataci gaba da tafiya ba.
Salman kuwa juyowa yayi ya zuba musu ido.
Kauda kansa gefe yayi lokacin daya kara taku ɗaya ya iso kusa da Jannart ɗin.
Ƙara matsowa yayi kusa da ita yana mai ware alkyabbar.
Kanshi ya ɗan ronkofar cikin yamutsa fuska yace.
“Duk wata Macen da tasan ciwon kanta, bata yawo a haka kamar yanda ke kike yi, sannan mata da yawa suna sirranta kansu, amma ke kina bayyana kazantarki in kika sani nayi amai bazan yafeba.”
Cike da mamaki ta ɗan juyo yana kallonshi.
Hakan ya zama kamar irin hirar masoyane irin ana kallon juna nan.
Wani saurayi ne dake can ta bayane yana kallonsu ta cikin raga,
Ya zaro wayarsa da sauri ya fara ɗaukar su hoto, domin ya gano ƙanwar Junaidu ce.
Sunkuyowa yayi tare da bud’e jakan daya shigo da ita ya zaro bottle water, b’alle murfin goran yayi, kana ya soma zubawa akan tarin sumar dake kansa wanda yake jin zufa na tsastsafo mishi.
Jin da yayi baisamu gamsuwa bane kuma yasashi karkad’a gashin kannasa dan yadda ruwan zai taɓa fatar kansa, wanda hakan yasa har ruwan dake kan nasa ya watsu akan fuskar Jannart.
Salman dake tsaye kuwa dan matsowa yayi, tare da gaishe da Rayyern d’in.
Batare kuma daya dago ba ya amsawa Salman d’in atakaice.
Idanu Salman yayiwa Rayyern dake tsaye, alaman ta gaishe shi.
D’an k’aramin bakinta ta turo gaba tare dasa hannunta ta goge ruwan daya watsa mata, kana asanyaye tace.
“Ina wuni.”
Shiru yayi bai amsa taba, tare dayin kamar ma baijita ba.
“Ina wuni.”
Jannart d’in ta sake fad’a akaro na biyu.
still shiru yasakeyi kamar baijita ba.
“Kibashi hakuri.”
Salman dake tsaye ya fada kasa-kasa.
Karamin bakinta ta sake turowa, cikin kuma wata irin murya mai kama da shagwab’a, sakalci, sanyi da kuma tsoro tace.
“Kayi hakuri please, ranan nayi maka b’arna amma bada sanina nayi hakan ba, Dan Allah da Manzonsa kayi hakuri.”
Idanunsa yadan lumshe saboda jin ta had’asa da sunan Allah da Manzonsa ne kuma, yasashi gyaɗa mata kai alaman yayi.
“Nagode.” Ta fad’a asanyaye.
Shikuwa Salman ganin hakanne ya sashi dan matsowa, cikin neman alfarma yace.
“Dan Allah ranka ya dad’e tambaya mukeyi.”
D’ago Kai Rayyern din yayi ya kalli Salman din afakaice.
Batare kuma dayace komai ba ya maida kansa k’asa tare da ɗaukan ɗan karamin towel ɗin dake gefe ya fara goge suman kanshi zuwa wuyanshi da fuskarshi da sajenshi da ruwan ya jiƙa.
Salman kuwa ganin hakanne yasashi Kallon Jannart, wanda gaba d’aya mood dinta ya sanja,tun lokaci da taga kamar dokin zai takesu ta soma sakin wani irin numfashi sama-sama a hankali.
Wanda da dukkan alama kuma tsoritan da tayi dazunne yakeson tayar mata da ciwon ta.
Sanin yanda ciwon keyi mata idan ya tashi ne kuma yasa, Salman din cewa.
“Subahanallah Jannart ciwonki ko?.”
Kai ta gyaɗa mishi cikin jawo ajiyan zuciya da take son yi.
Cikin kula ya nuna mata gefen Rayyern dan babu wata kujerar a nan kusa dasu.
"Maza ga waje ki zauna.”
Ya kare maganan yana meyi mata
Nuni da d’an gefen Rayyern, wanda kuma dama wajen zaman daya rage din bai wuce na zaman mutum daya ba sabida ya ajiye tarkacensa a wajan zaman mutun ɗaya gashi kuma a ɗaya wojen.
Jannart kuwa kasancewar dama ta gaji da tsayuwa kuma ga numfashin ta dake fizga ne yasa, batare da ta musa ba ta zauna awajen sanin in ta zauna zai iya dai-dai-ta.
Shikuwa Salman ƙara matsosu yayi.
Tare da sake maimaita maganarsa ta dazu.
“Dan Allah ranka ya dad’e tambaya mukeyi.”
“Inaji.”
Rayyern din ya fada agajarce, nan ma saboda yaji Salman din ya hadashi da Allah ne.
"Dan Allah wani mutum muke nema".
Uhum ya kuma cewa a taƙaice.
Gyara tsayuwa Salman yayi tare da cewa.
" Sunan shi Dr. Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara.
Shi muke nema, munje Hospital d’insa ne aka tabbatar mana da cewa Lallai-Lallai yana nan, shine muke tambaya dan Allah koka sanshi?”
Ad’an fakaice Rayyern din ya kalli Salman, saidai kuma cikin halin nuna ko inkula yace.
“Meyasa kuke nemanshi me zai muku? Wa yace muku yana nan?.”
Jannart dake dan haki ne taja ajiyan zuciya ta fizogishi da ɗan ƙarfi kana tace.
“Mitssss mutun sai rashin gsky, gaba ɗaya ya wahal damu."
Ta wutsiyar idonshi ya ɗan kalleta a fizge.
Ita kuwa ci ga da cewa tayi.
"Nemansa kawai mukeyi, wallahi daga yanzu kuma ni nagaji,
Dan bazan zauna inyi ta neman wani can ƙato baƙi mummuna mai ƙaton tumbi ba dan yayi kuɗi yana jin kansa waya masan TUBALI kuɗin nashi ko na haram ne shiyasa yake tsoron yin ido huɗu damu ƴan jaridu.
Kada ya gaza amsa mana tambayoyinmu."
Numfashin ta fesar a hankali jin ya dai-dai ta.
Salman nata jujjuya mata kai ina bata ganiba bare tasawa bakinta linzamin.
Tsaki ta ɗan ja tare da ci gaba da cewa.
"Mutumin nan ya wahalar damu sosai, na farko dai shiba kudi ba, amma na lura kudi yafi saukin samu akanshi.”
Alama Salman ya mata akan tayi shiru, da yin gyaran murya.
hakanne kuwa yasa tayi shirun.
Shikuwa Rayyern tunda ta fara maganan yake kallonta ta wutsiyar idanunsa baki cai-cai.
Salman kuwa gyara tsayuwarsa yayi, tare da fadin.
“Mu yan jarida ne kuma ma’aikatan tashar Arewa24, munzo nanne domin samun daman yin hira dashi, Lallai kuma muna da buk’atar ganinsa.
Domin rashin samun tattaunawa dashi ɗin, dai-dai yake da rasa aikin mu.”
Fuska Rayyern din yadan tab’e tare da cewa.
“Uhummm.” Atakaice.
Jin hakanne kuma yasa jikin Salman yin sanyi, still cikin yanayin dake bayyana damuwarsa yace.
“Dan Allah In dai kasan hanyar da zanbi wajen ganinsa ka taimaka min, Banason rasa aikina, inason aikina sosai, Dan Allah Idan ka sanshi, ko kuma kasan inda zan sameshi ka fad’amin, domin da wannan aikin kad’ai na dogara, dashi ne kuma nake ciyar da iyalaina da iyayena, dan Allah ka taimaka kada in rasa aikina.”
Tabbas Salman ya karyo lagonsa tunda ya hadashi da Allah da kuma nuna masa aikin shine mafogararsa, Idanunsa yadan lumshe ahankali, batare kuma daya kalli daya daga cikinsu ba yace.
“Naji badamuwa amma dai yanzu kam bayanan, Zan gaya masa idan ya amince shikenan, zan kawoshi har cikin tashan Arewa24 din kuyi mishi duk tambayar da kukeso.”
Farinciki da tsananin jindadi ne ya lullub’e cikin zuciyar Jannart da Salman.
Cikin bayyana zallan jin dadi Salman yace.
“Mungode sosai ranka ya dad’e, mungode kwarai, saidai amma dama ka sanshi ne?”
Kansa ya jinjina tare da cewa.
“Eh nasanshi uban gidanane zan gaya masa Insha Allah kuma zaizo zan roƙeshi in gaya masa uzurinka bisa tausayawarsa kan kada ka rasa aikinka da kake kula da ilanka zaizo in Sha Allah.”
Murmushi Jannart dake gefe tayi, tare da lumshe idanunta saboda wani irin sanyi da taji acikin zuciyarta sai kuma ta ɗan gyara zamanta.
Shikuwa Salman cikin tsananin jin daɗi yace.
“Sir! Nagode! Nagode!! sosai!!! Dan Allah kayi mishi magana, ni kuma zan tsumayeka har zuwa nan da y’an wasu kwanaki, wallahi Banason rasa aikina yau kuma saura kwana takwas za'ayi hirar dashi ranar Alhamis na sama.”
Kai Rayyern din ya jinjina, tare da sake cewa.
“Insha Allah zaizo.”
“Ka tabbatar zaizo?”
Jannart da nutsuwa ya dan fara sauka azuciyarta ta fad’a.
Dan juyawa yayi ya watsa mata harara, cikin zuciyarsa kuwa cewa yayi.
“Oho bansani ba shegen baki.”
Salman da farinciki ya cika zuciyarsa kuwa, cewa yayi.
“Mungode sosai amma dan Allah in ba matsala ka bamu numbern ka saboda idan zaizo din musani.”
Kansa yadan girgiza, cikin kuma rashin sabonsa da yawan magana yace.
“No kai dai ka bani taka numbern.”
To Salman yace Cikin gaggawa kuma ya bashi numbernsa.
Mikewa tsaye yayi fuskarsa cike da farinciki yace.
“Alhamdulillah Jannart taso mutafi Insha Allah yanzu kam na samu full confidence.”
Yayi maganar yana me soma tafiya, saboda tsananin farincikin da yake ciki kuwa bai majira Jananrt dinba.
Jannart kuwa ganin Salman din ya soma tafiya ne yasa ta mik’ewa tsaye itama.
Tashin nata kuwa yayi dai-dai da juyowan Rayyern inda ya sauke idanunsa Akan bayanta.
Da sauri ya rumtse idanunshi da ƙarfi tare da kame jikinsa sabida yadda yaji tsikar jikinshi na mimmiƙewa yana tashi tsaye.
Sabida a bunda ya gani ajikinta.
Yadda yaji tsikar jikinshi na tashi ne ya kuma sashi buɗe idanunsa.
Damatsan hannunsa ya kalla gaba ɗaya tattausan gargasar jikinsa ta miƙe tsaye.
Ita kuwa Jannart taku ta farayi da nufin bin bayan Salman wanda haka yasa ta ƙara matsowa gabanshi tana takun dake juya kyawawan mazaunanta.
Fuskarshi ya kuma yamutsawa.
Tare da saurin kawar da kansa gefe.
“Meye haka?”
Ya fad’a azuciyarsa yana mai jin kamar ana tsikarinsa
Jannart kuwa da batasan komai ba, ahankali ta soma dan takawa.
"Ta yaya mace zata kasa sanin ranakun al'adar ta? Ko ta kasa kimtsa kanta har ya fito ya ɓata mata sutura?".
Yayiwa kansa tambayoyin a jere.
"Miteeeew". Ya kuma jan gajeren tsaki.
"Daga nan zuwa parking lot mutun nawa zata sa suga jininta, maza nawa zasu ganta a haka, yanzu ita in an barta wai mai hankali ce ko? Waɗanne irin iyayene gareta da zasu barta kara zube da irin wannan shigar, na tabbatar da suturarmu ta hausa fulani tasa baza'a gane lalacewar kayan jikinta da wuriba kamar wannan tsukekken farin wondon pallozo ɗin ko ya ɓata mata jiki hijabinta zai kareta."
Yayi kalaman a saman harshensa.
A hankali ya ɗan juyo ya kalleta tana mai ci gaba da tafiya.
"Ko ba komai musulmace yana da kyau ta suturce kanta".
Ya faɗa yana kallon yadda take jujjuyawa tamkar Wahainiya.
Sai-dai bai wuce taku goma tayi ba zuwa sha biyu.
Taji muryarsa ta ratsa dodon kunnenta.
Inda yace “Stop.” Cikin wata irin kakkauran murya.
Aikuwa cak ta tsaya saidai kuma Sam ta kasa juyawa ta kalleshi.
Shikuwa Rayyern fuskarsa ya sake had’ewa, tare da yamutsaawa dan ji yake tamkar zaiyi amai kana ahankali ya juyo ya kalli alkyabbar shi dayake gefenshi.
A hankali yasa hannunshin ya d’auki alkyabban.
Ya tashi tsaye kana ya fara taku a nitse.
Har lau bata juyoba kuma bataci gaba da tafiya ba.
Salman kuwa juyowa yayi ya zuba musu ido.
Kauda kansa gefe yayi lokacin daya kara taku ɗaya ya iso kusa da Jannart ɗin.
Ƙara matsowa yayi kusa da ita yana mai ware alkyabbar.
Kanshi ya ɗan ronkofar cikin yamutsa fuska yace.
“Duk wata Macen da tasan ciwon kanta, bata yawo a haka kamar yanda ke kike yi, sannan mata da yawa suna sirranta kansu, amma ke kina bayyana kazantarki in kika sani nayi amai bazan yafeba.”
Cike da mamaki ta ɗan juyo yana kallonshi.
Hakan ya zama kamar irin hirar masoyane irin ana kallon juna nan.
Wani saurayi ne dake can ta bayane yana kallonsu ta cikin raga,
Ya zaro wayarsa da sauri ya fara ɗaukar su hoto, domin ya gano ƙanwar Junaidu ce.