Sashe 65
Tubali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai kuma Ashiru dake bakin gate, yana ta faman lellek’awa tako ta Ina, gudun kada su aikata kifi na ganinka mai jarkoma.
Acan cikin gidan kuwa, Momy ce ta fito daga cikin dakinta, cikin shirin kayan bacci, kaitsaye kuma dakin Daddy ta nufa.
Jannart dake tsaye acikin dakinta kuwa, Idanunta dake zubar da hawaye ta lumshe.
Wani iri takeji, Yayinda acikin ranta kuwa take cewa.
Inama da zata iya bijirewa umarnin Abba Kabir din, da zatace itakam ta fasa, da zata zauna agidansu da dadi ko ba dadi, tayarda kaddarar ta ce tazo a haka.
To amma ya zatayi? Bata da wani zabi ako da yaushe, tasani zatayi kewar gidansu sosai, zatayi kewar dakinta da kuma yan uwanta.
“Zanyi kewarka Daddy na, zanyi kewar Momy da Abdull, nasani zanyi kewar duk wani abu daya shafeni, Daddyna baya tab’a takuramin, bayayimin komai, kawai dai baya daukan mataki akan duk wani cin zarafi da Yah Junaid zaimin.”
Ta fadi hakan hawaye na ci gaba da zubowa akan fuskar ta.
Cikin sanyi da mutuwar jiki kuma ta d’auki yar jakar da ya hade komai nata na amfani aciki.
Drawernta ta bud’e tare da zaro, wani hijab mai kyau hadi da tsananin taushi ta zura akan, Daguwar rigar, Arabian gown dake jikinta.
Juyawa tayi Ahankali ta nufi kofar fita daga dakin, Yayinda tabar wayarta da goro da kuma sweets din da Abba Kabir ya bata atsakiyar gadon dakin.
Harta Kai bakin kofar fita ne kuma ta juyo, ta sake Kallon cikin dakin nata.
Lokaci daya kuma hawaye ya cigaba da sauka akan fuskarta.
Saidai kuma babu yanda ta iya, haka ta murda handle din kofar, cikin sand’a ta fice.
Fitowar nata ne kuma yayi dai-dai da wulgawan Momy, wanda ta wuce dakin Daddy.
Saurin komawa baya tayi ta labe.
Harsaida ta tabbatar da wucewan Momyn kafun ta fito, cikin tsananin sand’a take tafiya.
Harta karaso Cikin falon da Kwata Kwata babu yalwan haske acikinsa.
Handle din kofar falon ta murda Ahankali, bayan ta fito ne kuma ta maida kofar ta rufe.
Dai-dai lokacinne kuma Abdull wanda ya fito daukar ruwa, yaji kaman karan rufe kofa, saurin maida kallonsa ga kofar yayi, saidai ko alaman motsi baiga kofar tana yiba, gashi kuma babu kowa acikin falon, hakan yasa yayi tunanin ko kunnuwansa ne basu jiye masa dai-dai ba, kasancewar yana gigin bacci, bayan ya d’auki ruwanne kuma ya juya ya koma dakinsa.
Jannart kuwa Koda ta fito compound din gidan, cikin sand’a take tafiya, wanda hakan yasa Baba Ado dake tsaye yi mata alama akan tayi sauri.
Yayinda shikuwa Ashiru ya fita ya lellak’a musu waje, ganin babu kowa a arean wajenne kuma, yasa Ashirun daga mata hannu akan tazo ta wuce.
Aikuwa cikin sauri, da kuma tarin fargaban da takeji ta zo ta fice daga cikin gidan.
Yayinda Baba Ado shima ya rufa mata baya.
Ganin ficewar nasu ne kuma yasa Baba Ashiru maida kofar ahankali ya rufe.
Jannart kuwa tafiya suke ita da Baba Ado, wanda ya riga da yayi gaba, ita take biye dashi abaya.
Tafiya kuwa sukayi mai dan tsawo.
Kamar kuma yanda Abba Kabir din ya fad’a, kwana Uku suka shiga, ata ukunne kuma suka hango motarsa.
K’arasawa sukayi da sauri, inda Baba Adon kuma da kansa, ya budewa Jannart din gidan baya ta shiga ta zauna.
Kallon Abba Kabir din yayi, kana yace.
“Barrister Allah Yatsare ya kuma, taimaka akan duk wani abu da kukasa gaba, Allah Ya tono gaskiyar da ake boyewa.”
Da Ameen Barrister Kabir din ya amsa, Yayinda shi kuwa, Baba Ado ya juya Cikin sauri ya nufi hanyar komawa gidan, yana isa gidan kuwa, Baba Ashiru ya bud’e masa kofa.
Sa d’ab sad’ab haka ya shiga cikin mayan guard dinnan ya kwanta.
Barrister Kabir kuwa tada motar tasa yayi suka bar wajen.
Kaitsaye kuma Nassarawa G.R.A suka nufa.
Ita dai Jannart tunda ta shiga motar, ta kwantar da kanta ajikin kujera, hakanan takejin kanta wani iri.
Tafiyar mintuna kadan sukayi, suka shigo Cikin unguwar.
Adai-dai gaban babban gate din gidan, kuma Abba Kabir ya tsaya tare da dan danna horn.
Ari dake zaune ne ya taso ya bude musu, kasancewar Baba Maud’o karatun Qur’ani yakeyi shiyasa, Arin bai katseshi ba kuma dama Abba da Rayyern sun hanashi ziryar buɗe gate.
Ana bud’e gate din kuwa, Barrister Kabir ya tura hancin motar tasa ciki.
Bayan ya gama dai-dai-ta parking din motar ne, kuma ya bud’e b’angaren da yake ya fito.
Karasowa wajen su Baba Maud’on da yanzu ya shafa addu'a.
Isa garesa yayi, cikin girmamawa da kuma sakin fuska, ya bawa Baba Maud’on hannu suka gaisa.
kana yace.
“Dan Allah Baba Maud’o ko zaka iya nemamin iso zuwa cikin gidan.”
Murmushi Baba Maud’o yayi, tare da mikewa tsaye yace.
“Babu komai, Barrister bari nayiwa Alhajin magana.”
Kai Barrister Kabir ya jinjina, Yayinda shikuwa Baba Maud’o kaitsaye ya nufi cikin gidan, Koda ya karasa jikin kofar, kwankwasawa yayi tare dayin sallama.
Abba dake zaune afalo kuwa, Jin muryar Baba Maud’o ne, yasashi mikewa tsaye.
Tare da tasowa yazo ya bude kofar.
“A’a Baba Maud’o kaine.”
Abban ya fada.
Inda Baba Maud’o kuwa gyara tsayuwarsa yayi, tare da cewa.
”Ni ne Alhaji dama Barrister Kabir ne yace na nemama masa iso.”
Murmushi Abban ya fadada, tare da cewa.
“Masha Allah kace masa ya shigo.”
Da To Baba Maud’o ya amsa, kafun ya juya kaitsaye ya nufi wajen da Barrister din ke tsaye.
“Yace ka isa.”
“To To masha Allah Nagode sosai.”
Barrister Kabir din ya fad’a, yana me bud’e murfin motar, nan b’angaren baya inda Jannart din take.
Wanda kuma tad’an rufe gefen fuskarta, da tattausan hijabin dake jikinta.
Hannunta Abba Kabir din ya kamo, tare da cewa.
“Jannart fito, amma ki fito da kafar dama sannan ki rike addu’a a bakinki.”
Kanta ta Dan jinjina, cikin kuma sheshshekan kukan da yaso kwace mata ta fito daga cikin motar.
Sosai takejin kirjinta na wani irin bugawa, ga kuma wani nauyi da takeji acikin zuciyarta.
Yayinda hawayen dake cikin idanunta kuwa har yanzu suka kasa tsayuwa, shin wanni irin kulline acikin rayuwarta da har yasa akayi mata irin wannan auren?
“Masha Allah mu isa To.”
Baba Maud’o ya fad’a, yana me shigewa gaba, shikuwa Abba dake rike da hannun Jannart ya rufa masa baya.
Koda suka isa bakin kofar falon kuwa, Abba da kansa ya taso ya bud’e musu.
Tare da yi musu iso, cikin tsananin farinciki da jin dadi.
Karasowa cikin falon sukayi, Inda Abba Kabir din ya Zaunar da Jannart akan lallausan carfet din dake cikin falon.
Kana ya zauna asaman kujeran dake gefenta.
Abba kuwa Kallon Ramadan yayi, kana fuska asake yace.
“Ramadan jeka kiramin Rayyern.”
To Ramadan ya amsa, tare kuma da mikewa cikin sauri ya haura sama dan kiran Rayyern.
Rayyern dake kwance yana latsa system d’insa, jin muryar Ramadan dake knocking yasashi bada izinin shigowa.
Bud’e kofar Ramadan yayi ya shigo.
Cikin girmamawa, yace.
“Hamma Rayyern Abba na kiranka.”
Kai Rayyern din ya jinjina, Yayinda Ramadan kuwa ya juya ya tafi.
Koda ya dawo falon, cewa Abban yayi Rayyern din yana zuwa.
Kai Abba Ya jinjina, tare da cewa.
“Masha Allah to kaida Riyyam kudan bamu waje.”
Babu musu kuwa, duk suka Mike suka nufi steps din sama.
Suna haurawa kan steps din kuma Rayyern yana sauk’owa.
Kallonsa Ramadan yayi, tare da d’an gumtse dariyar farin cikin dake cinsa na sanin yanzu shine a layi.
Shikuwa Rayyern wani irin masifeffen kallon ya watsawa Ramadan, musamman alokacin daya sauke idanunsa akan Barrister Kabir da yake Zaune acikin falon.
Hakan yaji wani irin takaici ya cika masa zuciya sabida anfa dameshi matuka an hanashi salama.
Su kuwa Ramadan da Riyyam-nsra neman waje sukayi suka tsaya, Acan saman stairs din.
Yayinda shikuwa Rayyern jiki asanyaye ya karasa saukowa cikin falon.
Inda Barrister Kabir ke zaune agaban Abba, still kuma har yanzu yana rik’e da hannun Jannart wanda ta sunkuyar da kanta k’asa.
Abba kuwa Kallon Barrister Kabir din yayi, cikin tausasa Murya yace.
“Barrister daka koma sama ka zauna, Domin aduk sanda kazo gabana ka zauna akasa sai naji abun yamin nauyi.”
Murmushi Barrister Kabir din yayi, kana cikin mutum tawa yace.
“Babu komai Alhaji, zamana a k’asan bawai gazawa bace, kuma hakan yana da dalili.”
Kai Abban ya jinjina.
Tare kuma da kai dubansa ga Rayyern wanda ya karasa shigowa cikin falon.
“Zoka zauna anan Rayyern.”
Abban ya fada yana me nunawa Rayyern gefensa, kuma kusa da Mamy dake zaune.
Yayinda Jannart kuwa hawayen Idanunta, kwata-kwata sun kasa tsayawa, saboda yanda kukan ke neman cin karfinta ne kuma yasa har shashshekan kukan nata ya Dan soma fitowa.
Idanu duk suka zubawa Jannart din da kanta ke k’asa, Yayinda tsananin tausayin yarinyar ke sake lullub’e zuciyarsu, musamman ma Mamy da taji son yarinyar acikin zuciyarta, duk da cewar bata ga fuskar yarinyar ba, amma taji ta kwanta mata.
Rayyern kuwa yanda ya dauke kansa gefe, tamkar ma baisan da wata mai sakin sheshshekan kuka acikin falon ba.
Abba Kabir kuwa gyara zamansa yayi, tare da sake rike hannun Jannart kam, cikin muryarsa da tayi rauni sosai yace.
“Alhamdulillahi.
Yau gani na agabanka Alhaji Bashir, ga y’ata nan Jannart na kawota gareku”.
Sai kuma ya ɗan numfasa kana a hankali yaci gaba da cewa.
“Bansanku ba baku sanni ba, amma musulumci ya had’a mu kamar yanda manzon Allah yace, Almuslimu ak’ul muslim, musulmi d’an uwan musulmi ne, na nemi taimako kunyi mini, har lau kuma Ina sake neman taimakonku, akan kulawa da y’ata Jannart, da kuma rik’emin amanarta, Jannart amanace awajena numa kuma nima yau zan baku amana, arikemin Jannart Amana marainiya ce, Dan Allah ku rikemin amanarta, Jannart bata da laifi, jarrabawar rayuwace tazo mata ahaka.
Kana bata da tashin hankali, Jannart yarinyace mai tsananin biyayya, haka kuma mai tausasshiyar zuciya, Jannart yarinyace mai rauni, yarinyar da maraici ya cika gaba daya rayuwarta, Ina da tabbaci akan biyayyar Jannart.
Domin yarinya ce da take gudun bacin ran wanda ke kusa da ita, Idan tayi muku ba dai-dai ba ku hukuntata kamar yanda zaku hukunta y’ay’an cikinku.”
Dan tsagaitawa da maganan nasa yayi, saboda yanda Hawaye ke sauka akan fuskarsa.
Juyowa da kallonsa yayi ya kalli Mamy, cikin sanyin jiki yace.
Acan cikin gidan kuwa, Momy ce ta fito daga cikin dakinta, cikin shirin kayan bacci, kaitsaye kuma dakin Daddy ta nufa.
Jannart dake tsaye acikin dakinta kuwa, Idanunta dake zubar da hawaye ta lumshe.
Wani iri takeji, Yayinda acikin ranta kuwa take cewa.
Inama da zata iya bijirewa umarnin Abba Kabir din, da zatace itakam ta fasa, da zata zauna agidansu da dadi ko ba dadi, tayarda kaddarar ta ce tazo a haka.
To amma ya zatayi? Bata da wani zabi ako da yaushe, tasani zatayi kewar gidansu sosai, zatayi kewar dakinta da kuma yan uwanta.
“Zanyi kewarka Daddy na, zanyi kewar Momy da Abdull, nasani zanyi kewar duk wani abu daya shafeni, Daddyna baya tab’a takuramin, bayayimin komai, kawai dai baya daukan mataki akan duk wani cin zarafi da Yah Junaid zaimin.”
Ta fadi hakan hawaye na ci gaba da zubowa akan fuskar ta.
Cikin sanyi da mutuwar jiki kuma ta d’auki yar jakar da ya hade komai nata na amfani aciki.
Drawernta ta bud’e tare da zaro, wani hijab mai kyau hadi da tsananin taushi ta zura akan, Daguwar rigar, Arabian gown dake jikinta.
Juyawa tayi Ahankali ta nufi kofar fita daga dakin, Yayinda tabar wayarta da goro da kuma sweets din da Abba Kabir ya bata atsakiyar gadon dakin.
Harta Kai bakin kofar fita ne kuma ta juyo, ta sake Kallon cikin dakin nata.
Lokaci daya kuma hawaye ya cigaba da sauka akan fuskarta.
Saidai kuma babu yanda ta iya, haka ta murda handle din kofar, cikin sand’a ta fice.
Fitowar nata ne kuma yayi dai-dai da wulgawan Momy, wanda ta wuce dakin Daddy.
Saurin komawa baya tayi ta labe.
Harsaida ta tabbatar da wucewan Momyn kafun ta fito, cikin tsananin sand’a take tafiya.
Harta karaso Cikin falon da Kwata Kwata babu yalwan haske acikinsa.
Handle din kofar falon ta murda Ahankali, bayan ta fito ne kuma ta maida kofar ta rufe.
Dai-dai lokacinne kuma Abdull wanda ya fito daukar ruwa, yaji kaman karan rufe kofa, saurin maida kallonsa ga kofar yayi, saidai ko alaman motsi baiga kofar tana yiba, gashi kuma babu kowa acikin falon, hakan yasa yayi tunanin ko kunnuwansa ne basu jiye masa dai-dai ba, kasancewar yana gigin bacci, bayan ya d’auki ruwanne kuma ya juya ya koma dakinsa.
Jannart kuwa Koda ta fito compound din gidan, cikin sand’a take tafiya, wanda hakan yasa Baba Ado dake tsaye yi mata alama akan tayi sauri.
Yayinda shikuwa Ashiru ya fita ya lellak’a musu waje, ganin babu kowa a arean wajenne kuma, yasa Ashirun daga mata hannu akan tazo ta wuce.
Aikuwa cikin sauri, da kuma tarin fargaban da takeji ta zo ta fice daga cikin gidan.
Yayinda Baba Ado shima ya rufa mata baya.
Ganin ficewar nasu ne kuma yasa Baba Ashiru maida kofar ahankali ya rufe.
Jannart kuwa tafiya suke ita da Baba Ado, wanda ya riga da yayi gaba, ita take biye dashi abaya.
Tafiya kuwa sukayi mai dan tsawo.
Kamar kuma yanda Abba Kabir din ya fad’a, kwana Uku suka shiga, ata ukunne kuma suka hango motarsa.
K’arasawa sukayi da sauri, inda Baba Adon kuma da kansa, ya budewa Jannart din gidan baya ta shiga ta zauna.
Kallon Abba Kabir din yayi, kana yace.
“Barrister Allah Yatsare ya kuma, taimaka akan duk wani abu da kukasa gaba, Allah Ya tono gaskiyar da ake boyewa.”
Da Ameen Barrister Kabir din ya amsa, Yayinda shi kuwa, Baba Ado ya juya Cikin sauri ya nufi hanyar komawa gidan, yana isa gidan kuwa, Baba Ashiru ya bud’e masa kofa.
Sa d’ab sad’ab haka ya shiga cikin mayan guard dinnan ya kwanta.
Barrister Kabir kuwa tada motar tasa yayi suka bar wajen.
Kaitsaye kuma Nassarawa G.R.A suka nufa.
Ita dai Jannart tunda ta shiga motar, ta kwantar da kanta ajikin kujera, hakanan takejin kanta wani iri.
Tafiyar mintuna kadan sukayi, suka shigo Cikin unguwar.
Adai-dai gaban babban gate din gidan, kuma Abba Kabir ya tsaya tare da dan danna horn.
Ari dake zaune ne ya taso ya bude musu, kasancewar Baba Maud’o karatun Qur’ani yakeyi shiyasa, Arin bai katseshi ba kuma dama Abba da Rayyern sun hanashi ziryar buɗe gate.
Ana bud’e gate din kuwa, Barrister Kabir ya tura hancin motar tasa ciki.
Bayan ya gama dai-dai-ta parking din motar ne, kuma ya bud’e b’angaren da yake ya fito.
Karasowa wajen su Baba Maud’on da yanzu ya shafa addu'a.
Isa garesa yayi, cikin girmamawa da kuma sakin fuska, ya bawa Baba Maud’on hannu suka gaisa.
kana yace.
“Dan Allah Baba Maud’o ko zaka iya nemamin iso zuwa cikin gidan.”
Murmushi Baba Maud’o yayi, tare da mikewa tsaye yace.
“Babu komai, Barrister bari nayiwa Alhajin magana.”
Kai Barrister Kabir ya jinjina, Yayinda shikuwa Baba Maud’o kaitsaye ya nufi cikin gidan, Koda ya karasa jikin kofar, kwankwasawa yayi tare dayin sallama.
Abba dake zaune afalo kuwa, Jin muryar Baba Maud’o ne, yasashi mikewa tsaye.
Tare da tasowa yazo ya bude kofar.
“A’a Baba Maud’o kaine.”
Abban ya fada.
Inda Baba Maud’o kuwa gyara tsayuwarsa yayi, tare da cewa.
”Ni ne Alhaji dama Barrister Kabir ne yace na nemama masa iso.”
Murmushi Abban ya fadada, tare da cewa.
“Masha Allah kace masa ya shigo.”
Da To Baba Maud’o ya amsa, kafun ya juya kaitsaye ya nufi wajen da Barrister din ke tsaye.
“Yace ka isa.”
“To To masha Allah Nagode sosai.”
Barrister Kabir din ya fad’a, yana me bud’e murfin motar, nan b’angaren baya inda Jannart din take.
Wanda kuma tad’an rufe gefen fuskarta, da tattausan hijabin dake jikinta.
Hannunta Abba Kabir din ya kamo, tare da cewa.
“Jannart fito, amma ki fito da kafar dama sannan ki rike addu’a a bakinki.”
Kanta ta Dan jinjina, cikin kuma sheshshekan kukan da yaso kwace mata ta fito daga cikin motar.
Sosai takejin kirjinta na wani irin bugawa, ga kuma wani nauyi da takeji acikin zuciyarta.
Yayinda hawayen dake cikin idanunta kuwa har yanzu suka kasa tsayuwa, shin wanni irin kulline acikin rayuwarta da har yasa akayi mata irin wannan auren?
“Masha Allah mu isa To.”
Baba Maud’o ya fad’a, yana me shigewa gaba, shikuwa Abba dake rike da hannun Jannart ya rufa masa baya.
Koda suka isa bakin kofar falon kuwa, Abba da kansa ya taso ya bud’e musu.
Tare da yi musu iso, cikin tsananin farinciki da jin dadi.
Karasowa cikin falon sukayi, Inda Abba Kabir din ya Zaunar da Jannart akan lallausan carfet din dake cikin falon.
Kana ya zauna asaman kujeran dake gefenta.
Abba kuwa Kallon Ramadan yayi, kana fuska asake yace.
“Ramadan jeka kiramin Rayyern.”
To Ramadan ya amsa, tare kuma da mikewa cikin sauri ya haura sama dan kiran Rayyern.
Rayyern dake kwance yana latsa system d’insa, jin muryar Ramadan dake knocking yasashi bada izinin shigowa.
Bud’e kofar Ramadan yayi ya shigo.
Cikin girmamawa, yace.
“Hamma Rayyern Abba na kiranka.”
Kai Rayyern din ya jinjina, Yayinda Ramadan kuwa ya juya ya tafi.
Koda ya dawo falon, cewa Abban yayi Rayyern din yana zuwa.
Kai Abba Ya jinjina, tare da cewa.
“Masha Allah to kaida Riyyam kudan bamu waje.”
Babu musu kuwa, duk suka Mike suka nufi steps din sama.
Suna haurawa kan steps din kuma Rayyern yana sauk’owa.
Kallonsa Ramadan yayi, tare da d’an gumtse dariyar farin cikin dake cinsa na sanin yanzu shine a layi.
Shikuwa Rayyern wani irin masifeffen kallon ya watsawa Ramadan, musamman alokacin daya sauke idanunsa akan Barrister Kabir da yake Zaune acikin falon.
Hakan yaji wani irin takaici ya cika masa zuciya sabida anfa dameshi matuka an hanashi salama.
Su kuwa Ramadan da Riyyam-nsra neman waje sukayi suka tsaya, Acan saman stairs din.
Yayinda shikuwa Rayyern jiki asanyaye ya karasa saukowa cikin falon.
Inda Barrister Kabir ke zaune agaban Abba, still kuma har yanzu yana rik’e da hannun Jannart wanda ta sunkuyar da kanta k’asa.
Abba kuwa Kallon Barrister Kabir din yayi, cikin tausasa Murya yace.
“Barrister daka koma sama ka zauna, Domin aduk sanda kazo gabana ka zauna akasa sai naji abun yamin nauyi.”
Murmushi Barrister Kabir din yayi, kana cikin mutum tawa yace.
“Babu komai Alhaji, zamana a k’asan bawai gazawa bace, kuma hakan yana da dalili.”
Kai Abban ya jinjina.
Tare kuma da kai dubansa ga Rayyern wanda ya karasa shigowa cikin falon.
“Zoka zauna anan Rayyern.”
Abban ya fada yana me nunawa Rayyern gefensa, kuma kusa da Mamy dake zaune.
Yayinda Jannart kuwa hawayen Idanunta, kwata-kwata sun kasa tsayawa, saboda yanda kukan ke neman cin karfinta ne kuma yasa har shashshekan kukan nata ya Dan soma fitowa.
Idanu duk suka zubawa Jannart din da kanta ke k’asa, Yayinda tsananin tausayin yarinyar ke sake lullub’e zuciyarsu, musamman ma Mamy da taji son yarinyar acikin zuciyarta, duk da cewar bata ga fuskar yarinyar ba, amma taji ta kwanta mata.
Rayyern kuwa yanda ya dauke kansa gefe, tamkar ma baisan da wata mai sakin sheshshekan kuka acikin falon ba.
Abba Kabir kuwa gyara zamansa yayi, tare da sake rike hannun Jannart kam, cikin muryarsa da tayi rauni sosai yace.
“Alhamdulillahi.
Yau gani na agabanka Alhaji Bashir, ga y’ata nan Jannart na kawota gareku”.
Sai kuma ya ɗan numfasa kana a hankali yaci gaba da cewa.
“Bansanku ba baku sanni ba, amma musulumci ya had’a mu kamar yanda manzon Allah yace, Almuslimu ak’ul muslim, musulmi d’an uwan musulmi ne, na nemi taimako kunyi mini, har lau kuma Ina sake neman taimakonku, akan kulawa da y’ata Jannart, da kuma rik’emin amanarta, Jannart amanace awajena numa kuma nima yau zan baku amana, arikemin Jannart Amana marainiya ce, Dan Allah ku rikemin amanarta, Jannart bata da laifi, jarrabawar rayuwace tazo mata ahaka.
Kana bata da tashin hankali, Jannart yarinyace mai tsananin biyayya, haka kuma mai tausasshiyar zuciya, Jannart yarinyace mai rauni, yarinyar da maraici ya cika gaba daya rayuwarta, Ina da tabbaci akan biyayyar Jannart.
Domin yarinya ce da take gudun bacin ran wanda ke kusa da ita, Idan tayi muku ba dai-dai ba ku hukuntata kamar yanda zaku hukunta y’ay’an cikinku.”
Dan tsagaitawa da maganan nasa yayi, saboda yanda Hawaye ke sauka akan fuskarsa.
Juyowa da kallonsa yayi ya kalli Mamy, cikin sanyin jiki yace.