← Book details Tubali Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 13 OF 81

Sashe 13

Tubali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Can gefe kuma wani kekkyawan Dinning table ne shirye cikin Dinning area mai sarƙafe da labule mai zirin-zirin igiyoyin dake sarƙafe da duwatsu masu daraja sheƙin Diamond.
Kana sai wani Fridge shima kamar show glass kana gefenshi kuma Show glass ɗinne mai shirye da cups, plates, spoons, mug's da dai sauransu.
Sai Kitchen dake gefe da store kamar na falon ƙasa.
Kana sai Bedroom guda biyu, wanda basa kusa da juna dan a tsakanin su Dinning area da kitchen da store suke.

Akwai wata baranda mai kyau ta bayan ɗaya Bedroom ɗin inda nanne ɗakin Dr.Rayyern ɗayan kuma na Ramadan.
Ƙasan benen kuma akwai wata ƙofar wanda kana shiga zaka samu wani side ne kuma irin na saman sak, koman su iri ɗaya.

Sai can gefen kitchin ɗin falon ƙasan kuma akwai wani kofa wanda room and parlour ne mai kyau da Bathroom a ciki.

Daga gefe kuma can akwai ɗaki ɗaya inda masu aiki zata iya zama, amman bbu mai aikin a gidan.

Can waje kuma akwai BQ, Boys Quaters.

Gefen BQ ɗin kuma wani part ne mai kyau matsakaici a rufe yake su kansu Dr Rayyern da Ramadan Basu san menene a cikin wannan Part ɗin ba.

Tsarin gidan dai masha ALLAH.

Bisa wannan babban baranda mai steps biyar zuwa shida suka hau. Kana suka buɗe kofar babban falon.
Ramadan na mai kiran Abba! Abba!! Yana buɗe kofar suka hango Abba da Mamy, suna sauƙowa daga steps ɗin Dinning area, Wanda ta nan zasu fito side ɗinsu.

Wani kyakkyawan mutum ne mai matsakaicin shekaru, mai jini a jiki da tarin cikar haiba da kamala.

Ganin Rayyern dinne kuma yasa shi sakin wani irin yalwataccen murmushi, tare da buɗe hannayenshi dake cikin gariyar jikinsa.
Da sauri Dr Rayyern ya ƙarasa gabansa.
Rungumeshi yayi tsam a jikinsa tare da sauƙe ajiyan zuciya.

Mamy kuwa gefe ta zauna bisa kujera ta ɗaura ƙafa ɗaya bisa ɗaya, cikin haiba da tarin son ɗan nata tace.

“Babana wato Abba kawai kayi missing ko".
Da sauri ya saki Abba yana murmushi mai cike da farin cikin ganinsu yace.
"Na isa Mamy, bakiji me bahaushe yace ba."
Da sauri tace.
"Me yace".
Ta ƙare mgnar tana yiwa Abba kallon tsokana.

Matsowa yayi kusa da ita, hannunta ya kamo ya ɗaura tsakiyar kanshi tare da yin ƙasa da murya yace.

“Uwa mafi uba koda uban sarki ne".
Dariya mai cike da so tayi mishi.
Abba kuwa gefenta ya zauna tare da tsareshi da ido.
Ƙeyarshi ya ɗan sosa cikin sanyi yace.

“Abba bani ne na faɗa bafa, Malam bahaushe ne ya faɗa".

Ramadan ne yayi murmushi yana mai jin daɗin, yaga Hamman nashi yana gaban iyayensu, dan nanne kaɗai zakaga fara'arsa ka kuma ji yayi doguwar mgn Especially in da Abba ne.

A hankali ya zauna gaban Abban nasu, tare da miƙar da ƙafarsa dake masifar mishi zogi.
Ita kuwa Mamy Dinning area ta nufa.

Plate ta ɗauƙa cikin show glass din, kana ta buɗe Fridge.
Chocolates da sweet ta cika cikin plate ɗin.
Kana ɗayan kuma tasa Apple da inibi. sai kuma goran ruwa da cup a ɗaya ta shiryasu, bisa tray'n kana ta nufo falon.

Da sauri Ramadan ya matso kusa dashi, tare da zubawa ƙafarsa ido cikin mmki yace.
"Innalillahi Hamma Rayyern meya samu ƙafarka?”

A hankali ya miƙar da ƙafar tare da motsa ta.
Da sauri Mamy ta ƙasaro, Abba kuwa sunkuyowa yayi ya kama ƙafar cikin tashin hankali, ganin yadda yatsar ta haye ta kumbura ga jini har yanzu zuba yakeyi.
"Rayyern, meya sameka? Meya faru?".
Yayi tambayar a rikice.
Kanshi ya ɗan sunkuyar ya kalli ƙafar tasa, kana a hankali yace.
"Wata mahaukaciya ce ta takani".
Yayi mgnar cikin salonsa na rashin iya ƙarya.
"Wacece ita a ina kuka haɗu?".
Abba ya kuma tambaya.
"Ban santaba, just kawai dai I know mental problem ce, kuma a Airport muka hadu.”
Ya bashi amsa, adan takai ce yana mai cije labb’ansa, wanda kuma hakan alamace dake nuna cewar kafar tanayi mishi zafi sosae.

Ramadan kuwa da sauri ya miƙe, ɗakinsa ya haura da sassarfa, dan ƙaramin akwatin taimakon gaggawa na likitoci ya ɗauko.

Yana sauƙowa ya zauna daɓas a gaban Dr.Rayyern ɗin, kamo ƙafar yayi tare da fara bashi taimakon gaggawa dan jinin ya tsaya.
Cikin mmki Ramadan yace.
"Sorry Hamma har nail dinka ya fashe, amma Mahaukaciya a airport how? then why akabarta ta shiga airport din?”

“Uhmmm” yace dan azaban zafin da yakeji.

Da sauri suka ɗago kansu baki ɗayansu.
Shi Dr.Rayyern TV dake like jikin ginin ya zubawa idanu.
Tamkar zai mannasu jikin fuskar kekyawan Dattijon nan Malam Mai-nasara da aka hasko a tashar Sunnah TV.
Ahankali ya janye ƙafarsa daga riƙon da Ramadan yayi mishi.
Tare da juyawa ya maida hankalinshi ga TV, yayinda shima Ramadan hakan yayi.
Abba da Mamy kuwa idanu suka zubawa Rayyern ɗin.

Wani irin kallo Abba yakeyi mishi mai cike da ma'anoni.
Cikin haɗe fuska yace.
"Kai Ramadan tashi ka kashe tv’n nan".
Juyawa sukayi baki ɗayansu suna kallonshi.
Fuskarshi dake haɗe ne yasa Rayyern yin ƙasa da kanshi, cikin sassayan sauti murya can ƙasa yace.

“Please Abba kayi haƙuri wa'azinshi nada daɗi".
Cikin tsawa yace.
"Ramadan kashe min TV nan".
Da sauri Ramadan ya miƙe jiki na rawa ya kashe TV’n.

Shi kuwa Rayyern cikin wani irin rauni da biyayya, ga mahaifin nashi da bin umarnin shi da neman izininshi yace.

“Abba kayi haƙuri".
Fuska a haɗe yace.
"Ramadan zokayi mishi aikin daya dace.
To yace kana yazo ya wonke mishi yatsar yayi mishi dreesing ɗin wurin da duk abinda ya kamata.
Yana gamawa magriba nayi.
Dole suka miƙe sukayi al'wala kana suka nufi masallaci.

Jannart kuwa.
A hankali ta kutsa kanta cikin falon nasu.

Tazo tsakiyar falon kekan tayi kiciɓis da...!

In sha Allah zuwa dare in na samu caji zakuga PAGE 6.

Littafin TUBALI na kuɗine .

By
*GARKUWAR FULANI*

📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*TUBALI*

PAGE 6
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

*FREE PAGE ne*

*Littafin TUBALI na kuɗine ki biya ki darinki biyar kacal in saki a ƙaramin group wanda bonus ne ga dana na, dan in na gama ya zama Complete 1k ne, saukine yanzu ga Masoyana, asalin kuɗi nai 1k ne, Special Group kuma su post nasu zaifi yawa. 0661110170 GTBank AISHA GARKUWA ALIYU, sai ki turo shaidar biyanki ta whatsApp 09097853276. Kada ki bari garabasar ta wuceki, kice sai an gama, Hajia in kuma kinada zakuwa da turo 1k a saukake cikin makonni bibbiyu zamuke gama part-part*

Fawal beauty parlor sunai muku albashir da bude gidan Mata wato kigyara da kanki👩🏻‍🦰 da cewa suna gabatar da aiki na zamani kamar su gyaran jiki, spa kenan gyaran fuska wato facial,gyaran Kai, hair style , gyaran kafa pedicure,gyaran hannaye, manicure kitso,lalle ja da bakki,ba'a barsu abayaba suna saida kayan gyaran aure, turaruka,man shafawa, suna kwalliya wato makeup,turaren wuta, humrah,kulaccham dama abunda Baku sanshiba wato maida tsohuwa yarinya akankanin lokaci😄iya kudinka iya shagalinka💃kudai ku hanzarta zuwa ga wannan gida na mata zallah (FAWaL BEAUTY PARLOR)
Address: Main gate na fire service jimeta, opp sixty plaza.
kada kubari abaku labari😍 munai muku maraba a koda yaushe Mata yan kwalisa mace sai da gyara , yar uwa bora ba sunanki kizama mowar mai🏨 da taimakon FAWAL BEAUTY PARLOR 👩🏻‍🦰da kudinki qalilan kifita sab abunki ki baza kamci mai kama jiki.
Gamai buka contact CEO FAWaL BEAUTY PARLOR kan 09033901035 or 08078809930 sai kunzo, our time services from 8:am to 7pm, Monday to Saturday/ Sunday 10am to 6pm🪞🎁🛒🛍️🤝🏻

Da Yah Junaid, wani irin masifeffen tsorone ya rufeta wanda yasa ta fara ja da baya.
"Dan ubanki sai yanzu kika dawo? Ina kikaje kika tsaya? Tukun nama ƙarfe nawa ne ƙa'idar tashi aikinki?"
Ƙara matsota yayi tare da buga mata tsawa.
"Shegiya ƴar iska badake nake mgn bane kina jina kinyi shiruba".
Cikin rawan murya tace.
"Uh uhm dama gidan Baba Kabir nake".
Ta ƙare mgnar tana komawa gefen Mom da yanzu ta iso.
Cikin haɗe fuska tace.
"Yarinyar nanfa ba isasshen lfy ne da itaba".
Juya kai yayi ya watsa mata wani irin masifeffen kallo tare da cewa.
"Toh uwar shisshigi".
A hatsale Mom tace.
"Toh ubana, anyi Shisshigin aikin banza".
Ta ƙare mgnar da kama hannun Jannart sukayi ciki.
Shi kuwa kwaffa yayi tare da bin bayan Abdul da yazo ya wuce su, bai ce musu ko ƙalaba.

Riyyam-nsra ne kwance bisa tattausan gadon ɗakin hotel ɗin daya kama.
Tuni yasa sim card ɗin sa na Mtn har ya zauna ras a wayar.
Kana yasa katin daya saya tun wurin sayan layin.

Mgn yakeyi da Mammy.
Yana mata bayanin haɗuwarsa da mutumin nan da suke kama.
Harma da haɗuwarsu da su Salman, kana ya ƙara da cewa.
"Mammy al'ummar Nigeria suna da kirki, suna da mutunci da mutunta baƙo, naga karamcinsu tun a cikin jirgi.
Mammy ina son su ina son ƙasar."
Cikin sauƙe numfashi tace.
"Yesssss! Riyyam akwai masu kirki, da amana da kawaici.
Amman kuma akwai maha'inta azzalumai macuta, ka kula da kanka kayi taka tsantsan."
Cikin gamsuwa yace.
"Toh Mammy in sha Allah zan kula".

Daga nan ta bawa Zayton sukayi ta hira yana mai gaya mata yadda ƙasar take.

Zaune suke a falon gidan Dr Lukman.
Cikin tawagarsu ta gamayyar kamfanonin jihar da kuma likitoci.
Dr Lukman keyi musu bayanin cewa.
"Dr Rayyern Mai-nasara ya dawo a yammacin yau, kuma Alhamdulillah dama akwai taron da gwamnatin jiha zatayi damu likitoci a gobe da safe, shine babban dalilin dawowarsa.
Toh muna tashi a taron zanyi ƙoƙarin tahowa dashi campany'n Alhaji Idi Sale Dakata, muyi taron jan ra'ayin nashi a can".
Cikin gamsuwa sukace eh hakan yayi.
Kana sukaci gaba da tattaunawar.

Ab’angaren Dr Rayyern Mai-nasara kuwa, kusan atare suka shigo cikin gidan shida Abba da kuma Ramadan, wanda yanzunne dawowansu daga masallaci, domin koda suka yi sallah’n magriba basu fito daga cikin masallacin ba, har saida aka sallame salla’n Isha.

Kaitsaye cikin babban falon gidan suka nufa, Yayinda zuciyar kowannensu ke cike da sanyi da kuma salama, musamman ga yanda iska mai dadi ke kad’awa tana ratsa kowani hudan gashi na jikin d’an Adam mai rai.

Haka suka shigo falon Abba na gaba, sai Rayyern dake take masa baya, wanda yayi na k’arshen shigowa kuwa shine Ramadan, wanda yake d’an shafa screen d’in wayar dake rike a hannunsa.
Chapter 13 · 0% Book details