← Book details Tubali Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 6 OF 81

Sashe 6

Tubali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

“Hello Deen ya Gida".
Cewar Mahmoud.
Deen dake zaune gaban mamansu wanda yanzu ya gama magana da Usman ne yace.
"Lfy lau Alhamdulillah Mahmoud".

"Yah jikin Mama".

"Alhamdulillah jiki da sauƙi".
Ya bashi amsa yana miƙa mata maganin.

Gyara zamanshi yayi tare da cewa.
"Yah Usman ɗin yana dawowa ko?".
Ɗan gajeren tsaki yaja tare da cewa.
"Eh to, zasu dawo, amman sai jibi fa kuma nan ma wata ƙil in sun iso su kwana a Abuja wata ƙil suda nan sai ranar jumma'a".
ya ƙare mgnar da sanyi.

"Ayyah ba komai ai in dai jikin da sauƙi, jumma'a kamar yaune Allah dai ya dawo dashi lfy. Ka gaida min Mama da jiki Allah ƙara ƙarfin jiki".

“Amin Amin". yace kana sukayi sallama.

Katse kiran yayi tare da juyowa ya kalleta.
Numfashi suka sauƙe ita da Hajia Rabi'ah.
Sai kuma tace.
"Alhamdulillah, toh Mahmoud ko zaka bani number Deen".
Da sauri yace.
"A a in fa yasan me kike bincika bazai saurareki ba".
Hajia Rabi'ah ne ta amshi zancen da cewa.
"Kada ki damu Jannart in sha Allah komai zai tafi dai-dai.
Shi Mahmoud ɗin shi zai rinƙa samo mana bayani.
Tunda kuna da number’n juna zaike miki bayani, ba sai kin fito kinzo nan ba, tunda fitar naki aikine mai zaman kanshi."
Cikin gamsuwa da hakan tace.
"Toh shike nan My Aunty, Ngd Matuƙa Allah ya saka da al'khairi".

“Amin Amin.” tace
Tana mai gudun kada aikin ya bar hannun yarinyar tunda kowa ya ganta dai yasan bawai tana yin aikin dan neman kuɗi ko suna bane, tana yine dan ra'ayin tane gashi du-du watanni huɗu tayi da fara aikin kuma suna jin daɗin mu'amala da ita, so dama sanyin da shirin yayi shiyasa aka canza wanda ke yinsa a baya.
Kuma da alamun tana matuƙar jin daɗin aikin.

Kiran Salman ne ya shigo wayarta.
Da sauri ta amsa tare da karawa a kunne.
"Assalamu alaikum".
Tace cikin sassayan sautin ta.

Daga b’angarensa kuwa murmushi yayi tare da cewa.
"Wa alaikissalam, Jannart kinbi diddigin Rayyern d’in? Kuma wane lbri kika samo mana a kanshi? "

Cikin yarda da kai tace.
"Duk motsinshi na cikin tafin hannuna!".
Dariya mai sauti Salman yayi.
Hakama Hajia Rabi'ah da Mahmoud.
"Karsashi’nki da ƙarfin guiwarki akan aiki yana burgeni Jannart”.
Cewar Salman.
Cikin sauƙe numfashi tace.
"Toh ba doleba Salman, tunda naji ana shirin korata, ai sai inda ƙarfina da hikimata suka ƙare".

Cikin wasa yace.
"Ke har wani ƙarfi a garreki da dai kin tsaya a hikimar na yarda".

Murmushin daya sanya beauty point ɗin ta lotsawa tayi.
Haka dai suka ɗan tattauna batun bayan ta mishi bayanin abinda ta ji kan dawowarshi.

Saida tayi sallan azahar ne kuma ta fito suka nufi gida.

A kan hanyarsu ta komawa ne, Baba Ado driver'nta ya ɗan juyo ya kalleta cikin kulawa yace.
"Jannart yanzu dai ciwonki da sauƙi ko?".
Numfashin ta ɗan fidda kana a hankali tace.
"Alhamdulillah da sauƙi dai zance, amman yana yawan motsa min a kwanan nan kamar yana son tashi."
Cikin tausayawa yace.
"Toh amman har yanzu babu wani maganin da ake baki sai allurar da akeyi duk watan ne?".
Kai ta gyaɗa mishi tare da cewa.
"Eh".
Numfashi ya ɗan fesar kana yace.
"Allah ya sauƙaƙa yasa zakkan jikine al'farmar Annabi da al'ƙur'ani".
Cikin jin daɗi tace.

“Amin Baba Ado nagode!".

A can Ethiopia birnin Addis Ababa, kuwa.
Riyyam-nsra ne tsaye gaban wayarsa daya tsaida.
Rawa yakeyi da murmushi a fuskarsa.
Sai kuma ya kalli gefensa.
Wata kyakkyawar budurwa wacce a ƙalla suyi sa'anni.
Murmushi yakeyi cikin harshen Hausa yake cewa.
"Jibi iwar haka ina hanyar Nigeria, su Zayton kuma sai dai ayi ta aikin zumbura baki.
Fan's ku gani, wai kishi takeyi dani".
Da sauri ta kai mushi bugu tare da matso ƙwallar idanunta, tana faɗin
"Mammy! Mammy!!".
Wata kyakkyawar matace mai Kekkyawar sura da jiki da shiga ta kamala, wacce kyan surarta ya iya boye ainihin shekarunta, ta fito daga cikin wata ƙofar da fuskantar inda ya kafa wayar tashi.
Ɗan gudu-gudu da tsalle-tsalle yake yana zagaya parlon Zayton na biye dashi a baya.
Da sauri yayi tsalle tare da ɗan sakin ƙara yace.
"Ohh Mommy".
Jin ta ɗan sa hannu ta bugi ƙeyarshi.
Tura baki yayi tare dasa hannunshi ya shafa ƙeyar yana mai zazzarewa Zayton ido.
Abin gwanin ban dariya da ka gani kasan akwai Kekkyawar shaƙuwa, ƙauna, tausayi, da son juna.
Ɗauke wayar tashi yayi ya sake video a shafinsa na TIKTOK.
Kun san matsalar su kenan ƴan TIKTOK duk abinda zasuyi ko sukeyi sai sun nunawa duniya, More Especially irin Riyyam-nsra da yayi shuhura yayi zarra da dubban dubatan masoya mabiya, musamman a cikin kwanakin nan da yai mgn da Hausa ya janye mana hankalin matasan Nigeria, domin kuwa ayanzu followers d’insa harsun d’arawa two million.
Gane abin da yayi dinne kuma yasa. Mammy matsoshi da kyau ta kama kunnenshi ta ɗan matse.
Ƙara ya kuma ɗan saki, wanda yasa Zayton tuntsirewa da dariyar jin daɗi tana ɗaga mishi gira.
Ita kuma Mammy cikin ɗan faɗa tace.

“Wato kai Riyyam baza ka taɓa canzawa bako, duk motsinmu sai ka bazamu a duniya? Kai kam inaga kana gab da nuna duniya yadda kake kashi ma ko".
Hannunshi yake ɗan yayyarfawa tare da cewa.
"Afwan Yaah Mammy na tuba, wayyo Hamma Mammy zata tsinke min kunne".
Dariya Zayton tayi tare da cewa.
"Zai aikata fiye da hakama Mammy ja kunnen da kyau".
Hannunshi ya kai ya bugi hannunta tare da cewa.
"Yarinyar nan ki shiga hankalinki fa".
Fuska ta haɗe tare da cewa.
"Waye yarinyar yaro in ka manta in tuna maka nice babba 15 minute nake baka, kaga kuwa dole ace da mijin iya baba, dan 15 minute ba 15 second bane".
Sosai Mammy ta saki murmushi suna matuƙar sata nishaɗi da ɗebe mata kewa, da danne mata duk wani ƙuncin rayuwa, Especially in suna faɗa kan girma.
Zayton son girma kamar gyambo, 15 minute da take bashin nan ji takeyi kamar shekaru goma sha biyar take bashi.
Gefe ta zauna kana suka zo suka sata a tsakiya.
Cikin sakin fuska ta shafa kan Riyyam-nsra tare da cewa.
"Zoh nan autana".
Gwalo yayiwa Zayton tare da ɗaura kanshi bisa cinyarta tuni kuma ya sake haɗa video.
Murmushi yakeyi yana yiwa Zaiton signal tare da cewa.
"Mammy asamin al'barka".
Da sauri itama ta sako kanta tare da cewa.
"Mammy ai nice mace, dan haka ya riƙe girman ya matsa ni in kwanta".
Cikin yin ƙasa da murya Mammy tace.
"Ya isa haka ku bari, Dida na bacci kada ku tada min ita".
Toh sukace dan yadda tayi mgnar ba wasa.
Bayan ya saki wannan video ɗin ne kuma.
Ya gyara zamanshi ya fuskanci Mammy da kyau jin tana cewa.

“Riyyam sam hankali na. baya kwanciya da wannan rawan kan naka! Ina jin tsoron kayi nesa dani, gaba ɗaya ka juye ka zama ɗan nanaye, ka zama tamkar mazari duk inda kake sai rawa, sai waƙa, sai haɗa comedy duk inda kake waya na hannu, kai kaɗai a ganka kana dariya ko kana kuka ko kana haɗa fuska ko layi, kai gasu nan dai barkatai, ka zama ɗan Film a fili ka rubuta lbri ka tsara ka bawa kanka umarni kayi shirin.
Ga ɗan karen yawo yau kace zaka tafi waccar ƙasar, gobe kace zakaje waccar gashi ka zama babu sirri duk inda kake an sani, shiyasa nake jin tsoron zuwanka Nigeria duk inda kaga mata sai ka bisu da ido".

Da sauri ya gyara zamanshi cikin nitsuwa kamar ba shiba yace.
"Mammy babu komai sai al'khairi, ki yarda dani bana wani mugun abu, in ke bakya gani na ai Ubangijin talikai daya busan numfashin yana ganina".

Uhum tsakanin uwa da ɗa kenan ya gane cewa tana zargin shi ne ko tana tsoron taɓarɓarewar tarbiyarshi.
Cikin sauƙe nannauyan numfashin tace.
"Wlh badon dole ba, bazaka jeba, amman ba komai Allah ya kaika lfy ya dawo da kai lfy.
Sai dai dole ka nitsu ka dena wannan rawan kan".

Hannunshi yasa ya kame kanshi kana yace.
"Toh Mammy na dena".
Murmushi tayi hakama zaitun.

Washe gari ranar Laraba, Kano Nigeria.

Cikin bacci taji numfashin ta, na fita a cushe, kana tana shaƙan zazzafan ƙamshin turaren sa mai masifar ƙarfi da tafiya da numfashin ta.
Idonta ta buɗe cikin wahalar numfashi.
Da sauri ta ida buɗe su duka tare da fisgo numfashin ta a wahalce.
Sabida ganin Yah Junaid da tayi sunkuye a kanta hannunshi na kan ƙirjinta.
Wani irin tsuma da karkarwa jikinta ya farayi, da azaban ƙarfi.
Cikin tsananin tsoro da razanin ta yunƙuro zata tashi, tare da furta "innalillahi wa innalillahi raji'un."
Wani irin azabebben tsoro firgita kaɗuwa da gigitane suka dirar mata lokacin ɗaya jin yadda yasa hannunshi ya matse ta tare da murtuƙe fuskarshi.
Cikin tsananin rawan jiki take zaro ido murya da baki na rawa tace.
"Innalillahi Wa’inna Ilaihirraju’un Y... Ya... Yah... Juna..Junaid, me haka!!”

Wani irin masifeffen kallo ya watsa mata, tare da kai hannunshi duka biyu kan breast ɗinta, yayi musu wani irin masifeffen kamu wanda yasa ta saki wani irin gigitaccen ƙara, lokaci ɗaya kuma numfashin ta ya fara off and Dawn, ciwonta na gab da tashi.
Shi kuwa Junaid wani irin sanyi yakeji a ransa tare da rumtse tafin hannunsa.
Mom kuwa dake ɗakinta, ita da Abdul cikin razanin jin sautin muryar Jannart ta miƙe tsaye jiki na rawa, ta fito falo.
Dai-dai lokacin kuma Jannart ɗin ta fara wani irin fiffizgewa sabida numfashin ta dake shirin barin gangan jikinta.
Wata iriyar fitinenneyar zufa mai cike da zafi, ta fara tsastsafo mata tako wani hudan gashin jikinta.

“Hahhhh! Uhhhhhhhh!! Fuhhhhhhhheeeeyyyy!!! M...Mom!"
Ta fuzgo maganar da ƙarfi lokaci daya kuma numfashin ta ya dena shiga sai fifita.
Jiki na rawa Mom ta kutsa kanta cikin ɗakin nata.
Shi kuwa Junaid wani irin fitinenne abu yakeji yana tsirgar masa.
Hannunshi ya kirjinta. Tare da yiwa breast ɗin ta wani azabebben riƙon da saida yaji.
Gamsuwa shaiɗan cinsa.
Kana ya juya ya nufi ƙofar fita.
A bakin ƙofar sukayi kiciɓis da Mom.
Chapter 6 · 0% Book details