Sashe 64
Tubali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Abba kayi hakuri kawai dai inajin ba dadi ne, Ina son gidanmu sosai, inajin banason barinsa, matsalata kawai.
Yah Junaid ne, shine wanda ako da yaushe baya son farinciki na, asanadinsa ne kuma yau gashi, zan bar gidan zantafi wajen way’anda, basu sanni ba.”
Hannayenta Abban ya kama, tare da girgiza mata Kai.
“Kada kiyi kuka Jannart, gidan da zan kaiki zai samar miki da ingantaccen farinciki, mutanen cikinsa masu karamci ne kuma zasu zame miki yan uwa da yardar Allah, kinsani Jannart bazan tab’a cutar dake ko na kaiki inda za’a cutar dake ba.”
Kai Jannart din ta jinjina, alaman gamsuwa da kalamansa.
“Yauwa Jannart, Allah ya sanyawa rayuwar aurenki al'barka, sannan idan zaki fita, ki tattare duk wani abu naki mai amfani, kama daga kan laptop da kuma certificates, and duk wasu takardunki masu amfani, ki sasu ajaka ki kuma taho dasu, wayoyinki kuma ki barsu a nan a tsakiyar gadonki. Maganan kaya kuma banda kayan jikinki kada ki d’auki kaya ko kala d’aya, ni da kaina zanje na saya miki kayayyakin da zakina sawa.”
Kanta ta jinjina tana mai son tsaida hawayenta, Yayinda shi kuwa Abba Kabir din, ya mik’e ya fice daga cikin dakin.
Yana fita kuwa Jannart din ta mik’e, jiki asanyaye ta soma harhad’a takardun ta dama yan kananan abubuwan ta masu amfani.
Ab’angaren Abba Kabir kuwa yana fita daga cikin gidan, kaitsaye gidansa ya nufa.
Koda yaje ya samu Aunty Dijat zaune afalo, anan yake shaida mata cewar yau an daura Auren Jannart.
Farinciki ne ya lullub’e zuciyar Aunty Dijat, cikin jin dadi tace.
“Masha Allah, gaskiya naji dadi Allah Ya basu zaman lafiya, yaushe za’a kaita gidan Mijin?”
“Adaren yau zan kaita, amma Dijat karki manta, wannan maganan sirrine atsakaninmu, muddin ta fita daga bakinki, kada kiyi tunanin soyayyar dake tsakaninmu, da kuma irin zaman lafiyar da mukeyi, hadi da al’amarin yaya, zan watsar da ita, zan gurfanar dake agaban hukuma, ke kanki zan iya daura ayar zargi akanki.”
Kai Aunty Dijat din ta jinjina, cikin yin imani da abunda zata fad’a tace.
“Insha Allah Abban Hafeez, zaka sameni me matuk’ar sirrinta sirrinka, da izinin Ubangiji, wannan magana ba zata tab’a fita daga bakina ba.”
Kansa ya jinjina, alaman gamsuwa da bayanan nata.
By
*GARKUWAR FULANI*
https://chat.whatsapp.com/K6m92SSD10n24Jc3FDLxMp
Samun zafafan saukakan kayayyakin zamani na mata tun daga kan leshi, shadda, atamfa, material, jaka da takalmi, hijab..... da dai sauransu akan farashi mai sauki da rahusa sai a kamfanin Garkuwa collection. Bama wannan kadai ba akwai kayan order da muke yi shi ma duk a cikin rahusan da saukin kudi. Ba mu tsaya nan ba ina kuke yan kasar *NIGER* albishirinku kuma kuna iya siyan kayanmu ya isa gareku cikin aminci ba tare da bata lokaci ba. maza yan’uwa ku garzayo ku gane wa kanku wannan rahusar da kuke jin labari. Kayanmu ko a kasuwa ba zaka samu farashinsu ba. gidanmu gidan duniyar leshi, atamfa shadda, material da sauransu. Sai kun zo. Muna maraba da kai a kowanne gari kake.
GARKUWA COLLECTION! Siyan nagari mayar da kudi gida!
Acan B’angaren Daddy kuwa, shida Dr Lukman, da kuma Alhaji Abdu Tababa ne ke zaune, ad’aya daga cikin hall, na Tababa Company.
Wanda kuma gama meeting dinsu kenan, bayan kowa ya watse ne kuma suka d’auko zance akan Rayyern.
K’wafa Alhaji Idi Sale Dakata’n. Yayi, tare da d’agowa ya kalli abokanan makircin nasa.
“Yaron nan Dr. Rayyern ya tsayamin aka, kullum da zancen kawar dashi nake kwana nake tashi, amma Dan iskan yaro har yau ko gidansu na kasa ganewa, yaron yana nan kamar Maye, duk wani motsin da kayi yakan zama tamkar a tsakiyar tafin hannunsa yake, narasa wanni irin yaro ne, nasa abibiyeshi amma ya gane, binciken da yayi akaina kuma saida ya ninka wanda nayi akansa, yanzu shi babu abunda bai sani ha akaina, yasan gidana yasan komai akan al’amurana, ni kuma har yau bansan inane, gidansu ba, nadaisan acikin Nassarawa G.R.A suke, amma bansan Ina ne taka maimai gidansu ba acikin unguwar, duk iya bincikena na gaza ganewa, karfi da yaji.
D’an karamin tsako yana nema ya zamarmin ciwon ido, ya kuma zama dole na kawar dashi dole na b’atar dashi adoron kasa, dole yabar numfasawa nan bada jimawa ba, Domin Idan ba haka ba zai jawo babban b’arakar da dinketa zaiyi mana matuk’ar wahala.”
Gyara zama Alhaji Abdu Tababa yayi, cikin son kwantarwa da Alhaji Idi’n hankali yace.
“Karka damu Insha Allah, duk yanda zamuyi sai munyi.
Dan sanin duk wani abu daya shafesa, dole zamu kashe sa.
Domin barinsa araye hadari ne.”
“K’warai kuwa ai dole ne ma sai ya mutu, batun nemo gidansu kuwa, ku barshi a hannuna da kaina zanyi wannan, Domin ni na mafi bukatar mutuwarsa ayanzu fiye da komai, gaba daya duk ya tottosheni, acikin kaso 100 na daga mutanen da suke zuwa hospital dina, yanzu kaso 80 sun koma masa, kullum da bakin cikin abun nan nake kwana.”
Cewar Dr Lukman.
Dukansu kwafa sukayi, Yayinda kowannensu ya soma tsara irin bak’ar nufin dake cikin zuciyarsa.
Acan gidan su Rayyern kuwa, da matsanancin farinciki, Mamy take Kallon Abba wanda ya gaya mata batun d’aurin auren Rayyern din.
“Alhamdulillah, Alhamdulillah Allah mungode ma, Lallai Tabbas komai nada lokaci, Yau RAYYERN dina ya zama ango, Allah ya basu zaman lafiya, ya kuma saka al'khairi da al'barka acikin auren, ya kade musu duk wata fitina.”
Da.
“Ameen.” Abba ya amsa.
Batare kuma daya jima awajen Mamyn ba, ya tashi kaitsaye ya tafi wajen Baba Maud’o.
Mamy kuwa cikin tsananin farinciki ta fito falo ta zauna, dai-dai lokacinne kuma Ramadan da Riyyam-nsra suma suka sauk’o k’asa.
Riyyam-nsra ne ya karaso wajen Mamyn da sauri, cikin farincikin da yake ciki ne kuma yace.
“Mamy yaufa Auren Hamma Rayyern, gaskiya ya kamata ace mun d’an shashe, duk da ma auren sirrine amma ai dai mukam ya kamata, mu Dan shana ko Mamy.”
Murmushi Mamyn tayi, tare da dan jinjina masa Kai alaman eh.
Saboda tana cikin farin ciki itama yau din.
Riyyam kuwa waka ya kunna awayarsa, tare dayi musu connecting da tv, nan take kuwa sautin wakan Davido Maisuna Jowo ya soma tashi.
Nanfa Yayi starting video awayartasa, tare da soma rawa wayar na shooting d’insa, Mamy kuwa dake zaune gudun kada ya shooting da ita ne yasa ta tashi ta koma daki.
Tana tafiya kuwa Ramadan shima ya mik’e yana taya Riyyam-nsra din dancewa dan shi farin cikinsa biyu ne auren Hammansa da kuma samun damar nasa.
Adai-dai lokacinne kuma Rayyern ya bud’e murfin kofar dakinsa ya fito, jikinsa dauke da danshin ruwan alwala, kasancewar adai-dai lokacin ana ta kiraye kirayen sallan la’asar.
Tun kafun ya gama saukowa akan steps din falon, kuwa yake jin kida na tashi.
Da sauri ya dan karaso cikin falon.
Abunda ya ganine kuma ya sashi tsayawa, tare da dakawa su Riyyam din tsawa, fuska a murtuke yace.
“Mekukeyi haka, wannan wanni irin haukan banzane, ya zaku mayar mana da gida kaman filin gala ko club? Akan meye zaku cika mana gida da kide-kide, saboda meye akan wani dalili??”
Cikin fada sosai ya kare maganar.
Wanda hakan yasa Zakariyya Dan langwabar da kansa.
“Eyyah Hamma Rayyern Dan Allah ka barmu, yau fa ranar farinciki ne ranar auren babban yaya.”
Harara Rayyern din ya watsa masa, kana cikin takaici yace.
“Nabaku nanda 1mn ku tsaida kidannan, sannan lokacin sallah yayi, kuje kuyi alwala ku wuce masallaci.”
Baki Riyyam-nsra din ya dan turo gaba, dai-dai lokacin kuma Mamy ta fito daga cikin dakinta.
Kallon Mamyn Rayyern yayi, tare da d’an narkar da fuska yace.
“Mamy yaran nan basa ji, wai kida suke kunna mana acikin gida, kuma Mamy kinajinsu amma kika kyalesu.”
Murmushi Mamyn tayi tare da cewa.
“To Rayyern me kakeso nayi musu, na hanasu nishadi? Bayan ni kaina yau din farin cikin dake zuciyata bazai misaltu ba, yaufa aka daura maka aure, kaga Aikuwa ya zama dole muyi farinciki.”
Fuskarsa yadan narke, kaman zaice wani abu kuma saiya fasa kaitsaye ya fita tare da wucewa zuwa masallaci.
Yayinda su Riyyam-nsra da Ramadan kuwa suka haura sama dan gabatar da nasu alwalan.
Rayyern kuwa Koda yaje masallacin, bayan an idar da sallah, kaitsaye company d’insa ya sake komawa, yayi hakanne kuma saboda kwata kwata bayason zama haka har wani tunani ya dameshi.
Yayinda su Ramadan kuwa bayan sun idar da nasu sallan, suka shiga gari, musamman kuma suka yada zango a Green park, nanfa Riyyam-nsra ya shiga aikin yi musu Video, yana sending direct to Tiktok, daga karshe ma live ya fara yi.
Daga nan masaukinsa Ramadan ya wuce dole yasa Riyyam-nsra kwatso kwamutsansa suka taho gida.
Basu ne suka dawo gidan ba kuma, saida akayi sallan magriba.
Bayan sun dawo dinne kuma suka shirya kayan Riyyam-nsra sukayi al'wala kana suka wuce masallaci.
Rayyern kuwa har saida aka idar da sallan Isha kafun yake dawowa gida.
Anan falo ya samesu dukansu suna dinner.
Shigowarsa ne kuma yasa Mamy sakin murmushi, cike da kulawa tace.
“Yauwa Babana ka dawo ko, yanzu nake zancenka araina, zo kaci abinci.”
Kansa ya dan langwabar tare da Karasowa dining table din,
“Na nakoshi.”
Ya fad’a akasalance.
Wanda hakan yasa duk suka tsura masa ido, musamman Abba.
Shikuwa Rayyern still sake kwab’e Fuskarsa yayi, tare da dubansu yace.
“Ni baccima nakeji saida safe.”
Yana gama fadin hakan kuwa, baijirayi me waninsu zaice ba kaitsaye ya haura Sama.
Da Kallo Abba ya bisa, Yayinda acikin ransa yake mamakin halin Rayyern din, daga daura masa aure kawai lokaci daya harya sanja, sai kace wani mai aljanu.
Da haka dai suka ci gaba da cin abincinsu, bayan sun kammala ne kuma Abba ya koma dakinsa, Yayinda Ramadan Riyyam da Mamy kuwa suka zauna afalo, suna yar tab’a hira.
11:30 pm.
Gaba d’aya ko ina dake Cikin gidan, yayi shiru babu wani alaman kwakkwaran motsi dake tashi, wanda kuma hakan alamace dake nuna cewar duk wasu mutannen dake zirga-zirga acikin gidan sunyi bacci.
Haka ma compound din gidan babu kowa, ko ina shiru.
Daga can gefe kuwa, gaba daya guards din da suke gadin Jannart ne kwance, kowannesu ya sake katon baki da ciki, suna bacci kamar matattu.
Ind daga gefensu kuwa Baba Ado ne zaune, yana rik’e dayar radion sa.
Yah Junaid ne, shine wanda ako da yaushe baya son farinciki na, asanadinsa ne kuma yau gashi, zan bar gidan zantafi wajen way’anda, basu sanni ba.”
Hannayenta Abban ya kama, tare da girgiza mata Kai.
“Kada kiyi kuka Jannart, gidan da zan kaiki zai samar miki da ingantaccen farinciki, mutanen cikinsa masu karamci ne kuma zasu zame miki yan uwa da yardar Allah, kinsani Jannart bazan tab’a cutar dake ko na kaiki inda za’a cutar dake ba.”
Kai Jannart din ta jinjina, alaman gamsuwa da kalamansa.
“Yauwa Jannart, Allah ya sanyawa rayuwar aurenki al'barka, sannan idan zaki fita, ki tattare duk wani abu naki mai amfani, kama daga kan laptop da kuma certificates, and duk wasu takardunki masu amfani, ki sasu ajaka ki kuma taho dasu, wayoyinki kuma ki barsu a nan a tsakiyar gadonki. Maganan kaya kuma banda kayan jikinki kada ki d’auki kaya ko kala d’aya, ni da kaina zanje na saya miki kayayyakin da zakina sawa.”
Kanta ta jinjina tana mai son tsaida hawayenta, Yayinda shi kuwa Abba Kabir din, ya mik’e ya fice daga cikin dakin.
Yana fita kuwa Jannart din ta mik’e, jiki asanyaye ta soma harhad’a takardun ta dama yan kananan abubuwan ta masu amfani.
Ab’angaren Abba Kabir kuwa yana fita daga cikin gidan, kaitsaye gidansa ya nufa.
Koda yaje ya samu Aunty Dijat zaune afalo, anan yake shaida mata cewar yau an daura Auren Jannart.
Farinciki ne ya lullub’e zuciyar Aunty Dijat, cikin jin dadi tace.
“Masha Allah, gaskiya naji dadi Allah Ya basu zaman lafiya, yaushe za’a kaita gidan Mijin?”
“Adaren yau zan kaita, amma Dijat karki manta, wannan maganan sirrine atsakaninmu, muddin ta fita daga bakinki, kada kiyi tunanin soyayyar dake tsakaninmu, da kuma irin zaman lafiyar da mukeyi, hadi da al’amarin yaya, zan watsar da ita, zan gurfanar dake agaban hukuma, ke kanki zan iya daura ayar zargi akanki.”
Kai Aunty Dijat din ta jinjina, cikin yin imani da abunda zata fad’a tace.
“Insha Allah Abban Hafeez, zaka sameni me matuk’ar sirrinta sirrinka, da izinin Ubangiji, wannan magana ba zata tab’a fita daga bakina ba.”
Kansa ya jinjina, alaman gamsuwa da bayanan nata.
By
*GARKUWAR FULANI*
https://chat.whatsapp.com/K6m92SSD10n24Jc3FDLxMp
Samun zafafan saukakan kayayyakin zamani na mata tun daga kan leshi, shadda, atamfa, material, jaka da takalmi, hijab..... da dai sauransu akan farashi mai sauki da rahusa sai a kamfanin Garkuwa collection. Bama wannan kadai ba akwai kayan order da muke yi shi ma duk a cikin rahusan da saukin kudi. Ba mu tsaya nan ba ina kuke yan kasar *NIGER* albishirinku kuma kuna iya siyan kayanmu ya isa gareku cikin aminci ba tare da bata lokaci ba. maza yan’uwa ku garzayo ku gane wa kanku wannan rahusar da kuke jin labari. Kayanmu ko a kasuwa ba zaka samu farashinsu ba. gidanmu gidan duniyar leshi, atamfa shadda, material da sauransu. Sai kun zo. Muna maraba da kai a kowanne gari kake.
GARKUWA COLLECTION! Siyan nagari mayar da kudi gida!
Acan B’angaren Daddy kuwa, shida Dr Lukman, da kuma Alhaji Abdu Tababa ne ke zaune, ad’aya daga cikin hall, na Tababa Company.
Wanda kuma gama meeting dinsu kenan, bayan kowa ya watse ne kuma suka d’auko zance akan Rayyern.
K’wafa Alhaji Idi Sale Dakata’n. Yayi, tare da d’agowa ya kalli abokanan makircin nasa.
“Yaron nan Dr. Rayyern ya tsayamin aka, kullum da zancen kawar dashi nake kwana nake tashi, amma Dan iskan yaro har yau ko gidansu na kasa ganewa, yaron yana nan kamar Maye, duk wani motsin da kayi yakan zama tamkar a tsakiyar tafin hannunsa yake, narasa wanni irin yaro ne, nasa abibiyeshi amma ya gane, binciken da yayi akaina kuma saida ya ninka wanda nayi akansa, yanzu shi babu abunda bai sani ha akaina, yasan gidana yasan komai akan al’amurana, ni kuma har yau bansan inane, gidansu ba, nadaisan acikin Nassarawa G.R.A suke, amma bansan Ina ne taka maimai gidansu ba acikin unguwar, duk iya bincikena na gaza ganewa, karfi da yaji.
D’an karamin tsako yana nema ya zamarmin ciwon ido, ya kuma zama dole na kawar dashi dole na b’atar dashi adoron kasa, dole yabar numfasawa nan bada jimawa ba, Domin Idan ba haka ba zai jawo babban b’arakar da dinketa zaiyi mana matuk’ar wahala.”
Gyara zama Alhaji Abdu Tababa yayi, cikin son kwantarwa da Alhaji Idi’n hankali yace.
“Karka damu Insha Allah, duk yanda zamuyi sai munyi.
Dan sanin duk wani abu daya shafesa, dole zamu kashe sa.
Domin barinsa araye hadari ne.”
“K’warai kuwa ai dole ne ma sai ya mutu, batun nemo gidansu kuwa, ku barshi a hannuna da kaina zanyi wannan, Domin ni na mafi bukatar mutuwarsa ayanzu fiye da komai, gaba daya duk ya tottosheni, acikin kaso 100 na daga mutanen da suke zuwa hospital dina, yanzu kaso 80 sun koma masa, kullum da bakin cikin abun nan nake kwana.”
Cewar Dr Lukman.
Dukansu kwafa sukayi, Yayinda kowannensu ya soma tsara irin bak’ar nufin dake cikin zuciyarsa.
Acan gidan su Rayyern kuwa, da matsanancin farinciki, Mamy take Kallon Abba wanda ya gaya mata batun d’aurin auren Rayyern din.
“Alhamdulillah, Alhamdulillah Allah mungode ma, Lallai Tabbas komai nada lokaci, Yau RAYYERN dina ya zama ango, Allah ya basu zaman lafiya, ya kuma saka al'khairi da al'barka acikin auren, ya kade musu duk wata fitina.”
Da.
“Ameen.” Abba ya amsa.
Batare kuma daya jima awajen Mamyn ba, ya tashi kaitsaye ya tafi wajen Baba Maud’o.
Mamy kuwa cikin tsananin farinciki ta fito falo ta zauna, dai-dai lokacinne kuma Ramadan da Riyyam-nsra suma suka sauk’o k’asa.
Riyyam-nsra ne ya karaso wajen Mamyn da sauri, cikin farincikin da yake ciki ne kuma yace.
“Mamy yaufa Auren Hamma Rayyern, gaskiya ya kamata ace mun d’an shashe, duk da ma auren sirrine amma ai dai mukam ya kamata, mu Dan shana ko Mamy.”
Murmushi Mamyn tayi, tare da dan jinjina masa Kai alaman eh.
Saboda tana cikin farin ciki itama yau din.
Riyyam kuwa waka ya kunna awayarsa, tare dayi musu connecting da tv, nan take kuwa sautin wakan Davido Maisuna Jowo ya soma tashi.
Nanfa Yayi starting video awayartasa, tare da soma rawa wayar na shooting d’insa, Mamy kuwa dake zaune gudun kada ya shooting da ita ne yasa ta tashi ta koma daki.
Tana tafiya kuwa Ramadan shima ya mik’e yana taya Riyyam-nsra din dancewa dan shi farin cikinsa biyu ne auren Hammansa da kuma samun damar nasa.
Adai-dai lokacinne kuma Rayyern ya bud’e murfin kofar dakinsa ya fito, jikinsa dauke da danshin ruwan alwala, kasancewar adai-dai lokacin ana ta kiraye kirayen sallan la’asar.
Tun kafun ya gama saukowa akan steps din falon, kuwa yake jin kida na tashi.
Da sauri ya dan karaso cikin falon.
Abunda ya ganine kuma ya sashi tsayawa, tare da dakawa su Riyyam din tsawa, fuska a murtuke yace.
“Mekukeyi haka, wannan wanni irin haukan banzane, ya zaku mayar mana da gida kaman filin gala ko club? Akan meye zaku cika mana gida da kide-kide, saboda meye akan wani dalili??”
Cikin fada sosai ya kare maganar.
Wanda hakan yasa Zakariyya Dan langwabar da kansa.
“Eyyah Hamma Rayyern Dan Allah ka barmu, yau fa ranar farinciki ne ranar auren babban yaya.”
Harara Rayyern din ya watsa masa, kana cikin takaici yace.
“Nabaku nanda 1mn ku tsaida kidannan, sannan lokacin sallah yayi, kuje kuyi alwala ku wuce masallaci.”
Baki Riyyam-nsra din ya dan turo gaba, dai-dai lokacin kuma Mamy ta fito daga cikin dakinta.
Kallon Mamyn Rayyern yayi, tare da d’an narkar da fuska yace.
“Mamy yaran nan basa ji, wai kida suke kunna mana acikin gida, kuma Mamy kinajinsu amma kika kyalesu.”
Murmushi Mamyn tayi tare da cewa.
“To Rayyern me kakeso nayi musu, na hanasu nishadi? Bayan ni kaina yau din farin cikin dake zuciyata bazai misaltu ba, yaufa aka daura maka aure, kaga Aikuwa ya zama dole muyi farinciki.”
Fuskarsa yadan narke, kaman zaice wani abu kuma saiya fasa kaitsaye ya fita tare da wucewa zuwa masallaci.
Yayinda su Riyyam-nsra da Ramadan kuwa suka haura sama dan gabatar da nasu alwalan.
Rayyern kuwa Koda yaje masallacin, bayan an idar da sallah, kaitsaye company d’insa ya sake komawa, yayi hakanne kuma saboda kwata kwata bayason zama haka har wani tunani ya dameshi.
Yayinda su Ramadan kuwa bayan sun idar da nasu sallan, suka shiga gari, musamman kuma suka yada zango a Green park, nanfa Riyyam-nsra ya shiga aikin yi musu Video, yana sending direct to Tiktok, daga karshe ma live ya fara yi.
Daga nan masaukinsa Ramadan ya wuce dole yasa Riyyam-nsra kwatso kwamutsansa suka taho gida.
Basu ne suka dawo gidan ba kuma, saida akayi sallan magriba.
Bayan sun dawo dinne kuma suka shirya kayan Riyyam-nsra sukayi al'wala kana suka wuce masallaci.
Rayyern kuwa har saida aka idar da sallan Isha kafun yake dawowa gida.
Anan falo ya samesu dukansu suna dinner.
Shigowarsa ne kuma yasa Mamy sakin murmushi, cike da kulawa tace.
“Yauwa Babana ka dawo ko, yanzu nake zancenka araina, zo kaci abinci.”
Kansa ya dan langwabar tare da Karasowa dining table din,
“Na nakoshi.”
Ya fad’a akasalance.
Wanda hakan yasa duk suka tsura masa ido, musamman Abba.
Shikuwa Rayyern still sake kwab’e Fuskarsa yayi, tare da dubansu yace.
“Ni baccima nakeji saida safe.”
Yana gama fadin hakan kuwa, baijirayi me waninsu zaice ba kaitsaye ya haura Sama.
Da Kallo Abba ya bisa, Yayinda acikin ransa yake mamakin halin Rayyern din, daga daura masa aure kawai lokaci daya harya sanja, sai kace wani mai aljanu.
Da haka dai suka ci gaba da cin abincinsu, bayan sun kammala ne kuma Abba ya koma dakinsa, Yayinda Ramadan Riyyam da Mamy kuwa suka zauna afalo, suna yar tab’a hira.
11:30 pm.
Gaba d’aya ko ina dake Cikin gidan, yayi shiru babu wani alaman kwakkwaran motsi dake tashi, wanda kuma hakan alamace dake nuna cewar duk wasu mutannen dake zirga-zirga acikin gidan sunyi bacci.
Haka ma compound din gidan babu kowa, ko ina shiru.
Daga can gefe kuwa, gaba daya guards din da suke gadin Jannart ne kwance, kowannesu ya sake katon baki da ciki, suna bacci kamar matattu.
Ind daga gefensu kuwa Baba Ado ne zaune, yana rik’e dayar radion sa.