Sashe 39
Tubali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Y’ar k’aramar tsuka yaja, tare kuma da d’an buga kan steering motar tasa, kaitsaye ya sanja akalar tafiyar tasa, inda ya saki hanyar asibitin nasu daya kama, direct ya shari kwana tare da hawa kan titin da zai sa dashi da gidansu.
Ganin hakanne kuma yasa P.A d’agowa ya kalleshi, kamar zaice wani abu kuma saiya fasa, saboda yasan halin maigidan nasa, da yawan lokuta bayason adameshi da yawan magana.
Barrister Kabir dake bayan su Rayyern din kuwa, shima gudu yake shararawa, still kuma har yanzu yana mebin ba yansu, sai-dai duk bayan mintuna kad’an yana juyawa ya kalli Jannart dake kwance flat agidan baya, babu alaman numfashi ko d’igo ajikinta.
Wanda hakan kuwa shi yake k’ara sanya Barrister Kabir din acikin tashin hankali.
Tafiyar da bata wuce ta 30mn ba sukayi, isowarsu wajen wani jection ne kuma yasa, Usman P.A d’an d’ago kai ya kalli Rayyern din.
Sake Kallon bayansu Usman P.A din yayi, still kuma ganin motar da tun d’azu yake ankare da ita, na binsu abayane , yasa shi d’an muskutawa cikin kuma yanayin mamaki yace.
“Sir kaman fa binmu wannan motar dake bayanmu takeyi.”
Idanu Rayyern din ya d’aga, tare da maida kallonsa ga madubin motar wanda yake haska musu duk abunda ke bayansu.
Tabbas shima ya lura da motar, saidai kuma bai d’auki hakan amatsayin wani serious abuba, batare kuma daya tankawa Usman P.A ba, kaitsaye ya hau kan titin daya shigar dasu layin gidansu.
Suna isa bakin gate din tamfatsetsen gidan nasu ne kuma, barrister Kabir ya taka wani irin birki.
Wanda kuma hakan yayi dai-dai da tsayawar motar Rayyern din shima, cikin kuma zafin nama da zafin ciwon kan sa yakeji ya bud’e murfin motar ya fito, saboda duk atunaninsa Alhaji Idi Sale Dakata ne, bai daddara da gargadin daya yi masa ba, ya sake turo masa wasu mutanen dan su bibiyeshi.
Fitowarsa daga cikin tasa motar ne, kuma yasa Barrister Kabir fitowa shima cikin hanzari, kuma ya nufo Dr. Rayyern d’in.
Muryarsa na rawa yace.
“Dan Allah Dr. Rayyern ka taimakamin, kada Jannart ta rasa ranta, Dan Allah ka taimakawa rayuwarta, wlh itace kaɗai babbar *HUJJATA,* ita kad’ai ce Hujjar da zan nuna anan gaba, please ka taimaka min!!”
Barrister Kabir din ya fad’i haka cikin tsananin tashin hankali, da kuma muryarsa wacce take fitar da sautin kuka.
Dr. Rayyern din kuwa Jin amo da kuma sautin, muryar Barrister Kabir din dake fita cikin kuka ne, da kuma amo mai shiga kunne, yasa shi rumtse I danunsa, tare dasa hannunsa na dama ya dafe kansa, dake wani irin sarawa, dan lokaci daya yaji kaman ana buga masa gudu ma a tsakiyar kannasa, abu na farko da bayaso arayuwarsa shine, yi masa magana cikin sigar kuka da kuma d’aga murya, sannan kuma aduk sanda wani ya buk’aci taimako afujajan awajensa, ya kanji zuciyarsa ta karye.
Balle kuma Barrister Kabir din da yake ta had’ashi da sunan Allah.
*Inama ace makaranta zasu kasance kamar Dr Rayyern in an had’asu da Allah zasuyi abu ko zasu bari, dan Allah da Manzonsa da darajar iyayenku idan Free PAGE ya kare kada ku fitarmin da littafina, in kinsan kin sayane dan ki fitar dan Allah ki gaya min in meda miki kuɗinki Dan girman Allah da tsarki littafinmu akwai karami. Group 500 ne kacal 0661110170 GTBank AISHA GARKUWA ALIYU sai ki turo min shaidar biyanki ta whatsApp number na 09097853276 ko ki sayi katin MTN ki copy edin ki turo min ta WhatsApp*
“Usman!”
Rayyern din ya kira sunan Usman P.A da wata irin murya.
Jin amo da kuma sautin muryar Rayyern din cikin wani irin yanayi na dabanne kuma yasa, cikin sauri Usman ya fito, tare da k’arasowa yana Kallon Ogan nasa.
“Ka kaishi hospital Usman kacewa Sulaiman ya duba patient din, please kuje Usman kutafi daga nan please.....”
Rayyern din ya fad’i hakan, cikin wani irin yanayi marar dadi dayakejin kansa aciki, tare kuma dasa hannayensa duka biyu ya kama kansa.
Usman kuwa fahimtar halin da Ogan nasa ke cike ne yasa shi, saurin kallon Barrister Kabir.
Ahanzarce yace.
“Muje na rakaku hospital dinsa akwai Doctor's zasu dubata in sha Allah zata samu lfy.”
Ko jiran abunda Barrister Kabir din zaice kuwa baiyi ba, ya bud’e murfin motar barrister din, nan b’angaren mai zaman banza ya zauna.
Ganin hakanne kuma yasa Abba Kabir din shima komawa cikin motar, a 360 ya murzawa motar key tare da cillata kan titi, kaitsaye suka nufi asibitin Mai-nasara Hospital, saboda dama Barrister Kabir din yasan asibitin.
Ganin sun miki hanyar asibitinne kuma yasa Usman P.A ciro wayarsa ya dannawa Dr Sulaiman Kira.
Bugu biyu kuwa Sulaiman ya dauki wayar, bayan sun gaisa ne kuma Usman P.A ke fad’awa Sulaiman din cewa.
“Gamunan a hanyan Mai-nasara Hospital zamu kawo emergency patient, bisa umarnin Dr Rayyern.”
Da “to.”
Kawai Dr. Sulaiman ya amsa, Yayinda shi kuwa Usman P.A ya katse kiran.
Rayyern kuwa da har yanzu ke tsaye abakin, motar tasa hannayensa duka biyu yasa ya cigaba da rike kansa dake sarawa.
Jin da yayi cewar bazai iya jurewa tsayuwar bane, yasa shi nufar gate din gidannasu, koda ya isa jikin gate din, hannunsa ya daura akan y’ar karamar kofar dake jikin gate din, tare da tura ta ciki.
Baba Maud’o dake zaune abakin kofar dan Part ɗin sa, yana me sauraran radio ne ya d’ago kansa, saboda ji da yayi an tab’a kofar shigowa gate din.
Aikuwa yana d’aga kansa ya sauke idanunsa akan Rayyern, da har yanzu yake dafe da kansa da hannuwansa duka biyu.
“Rayyern!!!”
Baba Maud’o ya kira sunansa, cikin yanayi na mamaki da kuma zallar damuwa.
Batare kuma daya bari Rayyern din ya amsa masa ba, ya d’aura da cewa.
“Subahanallah Rayyern maiya sameka? Lafiya kuwa? Meke damunka? Bugewa kayi akan naka ne? Ko kuwa wani abune ya same ka?”
Baba Maud’o yayi masa duka tambayoyin cikin bayyana tsananin damuwarsa.
Shikuwa Rayyern da ayanzu, yakejin idanunsa sun fara yi masa nauyi, kai kawai ya iya girgizawa Baba Maud’on, batare kuma daya iya cewa komai ba, kaitsaye ya wuce cikin gidannasu.
Hakan da yayi dinne kuwa yasa Baba Maud’o, Jin wani iri acikin zuciyarsa, take kuma damuwa maitsananin yawa ta bayyana akan fuskarsa, saboda ya sani ba karamin abubane zai sa Rayyern din dawowa acikin irin wannan yanayin, Lallai akwai abunda yake damunshi.
“To kodai awajen aikin nasa ne aka bata masa rai? Kodai kuma ciwon kansa ne?”
Baba Maud’o yayiwa kansa tambayar da bashi da mai amsa masa ita, sai Rayyern din.
Ganin da yayi zancen zuciya bazai kaishi bane kuma, yasa shi dan bud’e kofar gidan ya lek’a waje, ganin motar Rayyern din da yayi fake akofar gate dinne kuma yasashi saurin fitowa, tare da leka cikin motar, ganin akwai key ajikin motar ne kuma yasa, da kansa ya wangale makeken gate din, tare da dawowa ya shiga cikin motar, da kansa ya shigo da motar ciki, saboda a lokacin shi kad’aine ya rage agidan, Hadi driver da kuma sauran masu bawa flowers ruwa duk basanan.
*Dan Allah da Manzonsa idan free PAGE sun kare kada ku fitar min da littafi, ina rokon nanne da yakinin duk Musulmin kirki mai cikar imani da sanin darajar Allah da Manzonsa da darajar iyayensa nasan bazai fitarmin da shi ba, ko ya karanta na watan*
Rayyern kuwa Ahankali yake tafiya, yana me d’an jujjuya kai tare kuma da rumtse idanunsa, da yakejin sunyi masa matukar nauyi.
Isowarshi jikin kofar da zata sadashi da babban falon gidanne kuma, yasa shi d’aura hannunsa akan handle din kofar.
Dai-dai lokacin kuwa Abba da Mamy ne ke zaune acikin falon da alamun tattauna abu mai mahimmanci sukeyi.
Inda Abba ya d’ago kansa ya kalli Mamy, cikin yanayin yin ƙasa da murya da alamun tsawatarwa yace.
“Kinsan abunda yake bunne, wanda kuma har yanzu bamu shirya tono shi ba. Meyasa kikeson ki bada kofa da abubuwa da yawa zasu iya wakana ba tare da mun shirya musuba.
Wannan sirrin mai karfi ne da cikar rauni, Tono shi kuma dai-dai yake da tsayawar bugun zuciyar wasu mutanen, musamman Rayye......”
Sauran maganan dake bakin Abban ne kuwa, suka mak’ale, asakamakon jin motsin bud’e kofar falon da akayi,
Wanda hakan yasa cikin sauri duk suka maida kallonsu ga bakin k’ofar.
Ganin Rayyern din da sukayi dafe da kai ne kuma, yasa duk suka mimmik’e,
“Rayyern lafiya kuwa?”
Abba ya tambaya hankalinsa atashe.
Kai Rayyern din ya d’an girgiza musu, batare daya ce komai ba, kuma ya k’arasa shigowa cikin falon, tare da nufan kan 3 seater, din leather cushion dake Cikin falon ya kwanta.
Still kuma hannayensa ya sake maidawa duka biyu ya rik’e kansa.
Al’amarin daya sanya hankalin su Abba da Mamy matukar tashi kenan.
Da sauri Abba ya k’arasa inda Rayyern din ke kwance, hannunsa ya d’aura akan Rayyern din, cikin muryar dake bayyana zallan damuwarsa da farga yace.
“Rayyern me yake damunka, kodai ciwon kanka ne ya tashi!?”
Kai Rayyern din ya jinjina alaman “Eh.” Saboda ayanzu yakai wani stage da bayajin zai iyayin wata magana.
Zazzafan numfashi Abba da Mamyn suka sauƙe, cike kuma da alhinin tashin ciwon kannasa, Abba ya zaro waya dan kiran Ramadan.
Yayinda Mamy kuwa ta matso kusa da Rayyern d’in, anutse ta zauna tare da soma shafa masa tarin sumar dake kansa.
A dai-dai wannan lokacin kuwa, Ramadan ne ke zaune acikin wani had’add’en lambu, dake cikin wani katafaren gida, yayinda ya k’urawa wata fara kyakkyawar matashiyar budurwar dake zaune agefensa idanu.
duk da cewar kuma ak’alla budurwar dake zaune agefen nashi, ba zata wuce 20 years ba, amma tana da cikar halitta mai kyau, da ganinta kuma kasan cewa yar manyan mutane ne, Rayhanna kenan kyakkyawar matashiyar budurwar mai alkunya.
Yayinda ad’an gefe da Rayhannan kuwa Riyyam-nsra ne zaune, yanata yiwa Hamman nasa tsiya.
Cikin kuma ya bawa da zab’in Ramadan d’in yace.
“Gaskiya Hamma Ramadan ka iya zab’en kyakkyawar budurwa, tamkar daga saudiya aka sassak’ota.”
Murmushin Jin dadi Ramadan yayi, tare da sanya hannunsa na dama ya dafa kafad’an Riyyam din, again kuma cikin kasa dauke idanunsa daga kan Rayhanna’n nasan yace.
“Angaya maka cewar ni na wasa ne, ai kwata kwata bana sanya, ko da ka d’auka cewar ni irin suma Hamma Rayyern ne waliyai.”
Ganin hakanne kuma yasa P.A d’agowa ya kalleshi, kamar zaice wani abu kuma saiya fasa, saboda yasan halin maigidan nasa, da yawan lokuta bayason adameshi da yawan magana.
Barrister Kabir dake bayan su Rayyern din kuwa, shima gudu yake shararawa, still kuma har yanzu yana mebin ba yansu, sai-dai duk bayan mintuna kad’an yana juyawa ya kalli Jannart dake kwance flat agidan baya, babu alaman numfashi ko d’igo ajikinta.
Wanda hakan kuwa shi yake k’ara sanya Barrister Kabir din acikin tashin hankali.
Tafiyar da bata wuce ta 30mn ba sukayi, isowarsu wajen wani jection ne kuma yasa, Usman P.A d’an d’ago kai ya kalli Rayyern din.
Sake Kallon bayansu Usman P.A din yayi, still kuma ganin motar da tun d’azu yake ankare da ita, na binsu abayane , yasa shi d’an muskutawa cikin kuma yanayin mamaki yace.
“Sir kaman fa binmu wannan motar dake bayanmu takeyi.”
Idanu Rayyern din ya d’aga, tare da maida kallonsa ga madubin motar wanda yake haska musu duk abunda ke bayansu.
Tabbas shima ya lura da motar, saidai kuma bai d’auki hakan amatsayin wani serious abuba, batare kuma daya tankawa Usman P.A ba, kaitsaye ya hau kan titin daya shigar dasu layin gidansu.
Suna isa bakin gate din tamfatsetsen gidan nasu ne kuma, barrister Kabir ya taka wani irin birki.
Wanda kuma hakan yayi dai-dai da tsayawar motar Rayyern din shima, cikin kuma zafin nama da zafin ciwon kan sa yakeji ya bud’e murfin motar ya fito, saboda duk atunaninsa Alhaji Idi Sale Dakata ne, bai daddara da gargadin daya yi masa ba, ya sake turo masa wasu mutanen dan su bibiyeshi.
Fitowarsa daga cikin tasa motar ne, kuma yasa Barrister Kabir fitowa shima cikin hanzari, kuma ya nufo Dr. Rayyern d’in.
Muryarsa na rawa yace.
“Dan Allah Dr. Rayyern ka taimakamin, kada Jannart ta rasa ranta, Dan Allah ka taimakawa rayuwarta, wlh itace kaɗai babbar *HUJJATA,* ita kad’ai ce Hujjar da zan nuna anan gaba, please ka taimaka min!!”
Barrister Kabir din ya fad’i haka cikin tsananin tashin hankali, da kuma muryarsa wacce take fitar da sautin kuka.
Dr. Rayyern din kuwa Jin amo da kuma sautin, muryar Barrister Kabir din dake fita cikin kuka ne, da kuma amo mai shiga kunne, yasa shi rumtse I danunsa, tare dasa hannunsa na dama ya dafe kansa, dake wani irin sarawa, dan lokaci daya yaji kaman ana buga masa gudu ma a tsakiyar kannasa, abu na farko da bayaso arayuwarsa shine, yi masa magana cikin sigar kuka da kuma d’aga murya, sannan kuma aduk sanda wani ya buk’aci taimako afujajan awajensa, ya kanji zuciyarsa ta karye.
Balle kuma Barrister Kabir din da yake ta had’ashi da sunan Allah.
*Inama ace makaranta zasu kasance kamar Dr Rayyern in an had’asu da Allah zasuyi abu ko zasu bari, dan Allah da Manzonsa da darajar iyayenku idan Free PAGE ya kare kada ku fitarmin da littafina, in kinsan kin sayane dan ki fitar dan Allah ki gaya min in meda miki kuɗinki Dan girman Allah da tsarki littafinmu akwai karami. Group 500 ne kacal 0661110170 GTBank AISHA GARKUWA ALIYU sai ki turo min shaidar biyanki ta whatsApp number na 09097853276 ko ki sayi katin MTN ki copy edin ki turo min ta WhatsApp*
“Usman!”
Rayyern din ya kira sunan Usman P.A da wata irin murya.
Jin amo da kuma sautin muryar Rayyern din cikin wani irin yanayi na dabanne kuma yasa, cikin sauri Usman ya fito, tare da k’arasowa yana Kallon Ogan nasa.
“Ka kaishi hospital Usman kacewa Sulaiman ya duba patient din, please kuje Usman kutafi daga nan please.....”
Rayyern din ya fad’i hakan, cikin wani irin yanayi marar dadi dayakejin kansa aciki, tare kuma dasa hannayensa duka biyu ya kama kansa.
Usman kuwa fahimtar halin da Ogan nasa ke cike ne yasa shi, saurin kallon Barrister Kabir.
Ahanzarce yace.
“Muje na rakaku hospital dinsa akwai Doctor's zasu dubata in sha Allah zata samu lfy.”
Ko jiran abunda Barrister Kabir din zaice kuwa baiyi ba, ya bud’e murfin motar barrister din, nan b’angaren mai zaman banza ya zauna.
Ganin hakanne kuma yasa Abba Kabir din shima komawa cikin motar, a 360 ya murzawa motar key tare da cillata kan titi, kaitsaye suka nufi asibitin Mai-nasara Hospital, saboda dama Barrister Kabir din yasan asibitin.
Ganin sun miki hanyar asibitinne kuma yasa Usman P.A ciro wayarsa ya dannawa Dr Sulaiman Kira.
Bugu biyu kuwa Sulaiman ya dauki wayar, bayan sun gaisa ne kuma Usman P.A ke fad’awa Sulaiman din cewa.
“Gamunan a hanyan Mai-nasara Hospital zamu kawo emergency patient, bisa umarnin Dr Rayyern.”
Da “to.”
Kawai Dr. Sulaiman ya amsa, Yayinda shi kuwa Usman P.A ya katse kiran.
Rayyern kuwa da har yanzu ke tsaye abakin, motar tasa hannayensa duka biyu yasa ya cigaba da rike kansa dake sarawa.
Jin da yayi cewar bazai iya jurewa tsayuwar bane, yasa shi nufar gate din gidannasu, koda ya isa jikin gate din, hannunsa ya daura akan y’ar karamar kofar dake jikin gate din, tare da tura ta ciki.
Baba Maud’o dake zaune abakin kofar dan Part ɗin sa, yana me sauraran radio ne ya d’ago kansa, saboda ji da yayi an tab’a kofar shigowa gate din.
Aikuwa yana d’aga kansa ya sauke idanunsa akan Rayyern, da har yanzu yake dafe da kansa da hannuwansa duka biyu.
“Rayyern!!!”
Baba Maud’o ya kira sunansa, cikin yanayi na mamaki da kuma zallar damuwa.
Batare kuma daya bari Rayyern din ya amsa masa ba, ya d’aura da cewa.
“Subahanallah Rayyern maiya sameka? Lafiya kuwa? Meke damunka? Bugewa kayi akan naka ne? Ko kuwa wani abune ya same ka?”
Baba Maud’o yayi masa duka tambayoyin cikin bayyana tsananin damuwarsa.
Shikuwa Rayyern da ayanzu, yakejin idanunsa sun fara yi masa nauyi, kai kawai ya iya girgizawa Baba Maud’on, batare kuma daya iya cewa komai ba, kaitsaye ya wuce cikin gidannasu.
Hakan da yayi dinne kuwa yasa Baba Maud’o, Jin wani iri acikin zuciyarsa, take kuma damuwa maitsananin yawa ta bayyana akan fuskarsa, saboda ya sani ba karamin abubane zai sa Rayyern din dawowa acikin irin wannan yanayin, Lallai akwai abunda yake damunshi.
“To kodai awajen aikin nasa ne aka bata masa rai? Kodai kuma ciwon kansa ne?”
Baba Maud’o yayiwa kansa tambayar da bashi da mai amsa masa ita, sai Rayyern din.
Ganin da yayi zancen zuciya bazai kaishi bane kuma, yasa shi dan bud’e kofar gidan ya lek’a waje, ganin motar Rayyern din da yayi fake akofar gate dinne kuma yasashi saurin fitowa, tare da leka cikin motar, ganin akwai key ajikin motar ne kuma yasa, da kansa ya wangale makeken gate din, tare da dawowa ya shiga cikin motar, da kansa ya shigo da motar ciki, saboda a lokacin shi kad’aine ya rage agidan, Hadi driver da kuma sauran masu bawa flowers ruwa duk basanan.
*Dan Allah da Manzonsa idan free PAGE sun kare kada ku fitar min da littafi, ina rokon nanne da yakinin duk Musulmin kirki mai cikar imani da sanin darajar Allah da Manzonsa da darajar iyayensa nasan bazai fitarmin da shi ba, ko ya karanta na watan*
Rayyern kuwa Ahankali yake tafiya, yana me d’an jujjuya kai tare kuma da rumtse idanunsa, da yakejin sunyi masa matukar nauyi.
Isowarshi jikin kofar da zata sadashi da babban falon gidanne kuma, yasa shi d’aura hannunsa akan handle din kofar.
Dai-dai lokacin kuwa Abba da Mamy ne ke zaune acikin falon da alamun tattauna abu mai mahimmanci sukeyi.
Inda Abba ya d’ago kansa ya kalli Mamy, cikin yanayin yin ƙasa da murya da alamun tsawatarwa yace.
“Kinsan abunda yake bunne, wanda kuma har yanzu bamu shirya tono shi ba. Meyasa kikeson ki bada kofa da abubuwa da yawa zasu iya wakana ba tare da mun shirya musuba.
Wannan sirrin mai karfi ne da cikar rauni, Tono shi kuma dai-dai yake da tsayawar bugun zuciyar wasu mutanen, musamman Rayye......”
Sauran maganan dake bakin Abban ne kuwa, suka mak’ale, asakamakon jin motsin bud’e kofar falon da akayi,
Wanda hakan yasa cikin sauri duk suka maida kallonsu ga bakin k’ofar.
Ganin Rayyern din da sukayi dafe da kai ne kuma, yasa duk suka mimmik’e,
“Rayyern lafiya kuwa?”
Abba ya tambaya hankalinsa atashe.
Kai Rayyern din ya d’an girgiza musu, batare daya ce komai ba, kuma ya k’arasa shigowa cikin falon, tare da nufan kan 3 seater, din leather cushion dake Cikin falon ya kwanta.
Still kuma hannayensa ya sake maidawa duka biyu ya rik’e kansa.
Al’amarin daya sanya hankalin su Abba da Mamy matukar tashi kenan.
Da sauri Abba ya k’arasa inda Rayyern din ke kwance, hannunsa ya d’aura akan Rayyern din, cikin muryar dake bayyana zallan damuwarsa da farga yace.
“Rayyern me yake damunka, kodai ciwon kanka ne ya tashi!?”
Kai Rayyern din ya jinjina alaman “Eh.” Saboda ayanzu yakai wani stage da bayajin zai iyayin wata magana.
Zazzafan numfashi Abba da Mamyn suka sauƙe, cike kuma da alhinin tashin ciwon kannasa, Abba ya zaro waya dan kiran Ramadan.
Yayinda Mamy kuwa ta matso kusa da Rayyern d’in, anutse ta zauna tare da soma shafa masa tarin sumar dake kansa.
A dai-dai wannan lokacin kuwa, Ramadan ne ke zaune acikin wani had’add’en lambu, dake cikin wani katafaren gida, yayinda ya k’urawa wata fara kyakkyawar matashiyar budurwar dake zaune agefensa idanu.
duk da cewar kuma ak’alla budurwar dake zaune agefen nashi, ba zata wuce 20 years ba, amma tana da cikar halitta mai kyau, da ganinta kuma kasan cewa yar manyan mutane ne, Rayhanna kenan kyakkyawar matashiyar budurwar mai alkunya.
Yayinda ad’an gefe da Rayhannan kuwa Riyyam-nsra ne zaune, yanata yiwa Hamman nasa tsiya.
Cikin kuma ya bawa da zab’in Ramadan d’in yace.
“Gaskiya Hamma Ramadan ka iya zab’en kyakkyawar budurwa, tamkar daga saudiya aka sassak’ota.”
Murmushin Jin dadi Ramadan yayi, tare da sanya hannunsa na dama ya dafa kafad’an Riyyam din, again kuma cikin kasa dauke idanunsa daga kan Rayhanna’n nasan yace.
“Angaya maka cewar ni na wasa ne, ai kwata kwata bana sanya, ko da ka d’auka cewar ni irin suma Hamma Rayyern ne waliyai.”