Sashe 24
Tubali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Way’annan sune magungunan da ya kamata yana shansu a koda yaushe, Insha Allah zai samu lafiya nan bada jimawa ba.
Karb’an takardan Alhaji Ibrahim din yayi, tare da yiwa Rayyern d’in godiya maitarin yawa.
Saidai kuma baikai ga ida godiyar tasa ba, muryarsa ta mak’ale a kasan makoshinsa, sakamakon daura idanunsa da yayi akan sign din da Dr. Rayyern din yayi acan kasan paper’n.
Idanu ya k’urawa sign din cike da ɗan mamaki hadi da al’ajabi, ya d’ago ya kalli Baban nasu, wato Malam Mai-nasara da kuma sauran y’an uwansa.
Cikin tu’ajjudin da yake ciki dinne kuma direct ya mikowa Malam Mai-nasara din takardan.
Aikuwa Malam Mai-nasara na karb’an takardar idanunsa suka sauk’a akan signing din dama salon rubutun kanshi.
Cike da mamaki wanda har saida ya kasa b’oye hakan ya d’ago ya kalli Rayyern.
Rayyern kuwa da Sam bai fahimci komai adangane da irin Kallon da yaga sunayiwa takardar ba, kwata kwata sam baidamu ba.
Saima juyowa da yayi ya kalli Ramadan.
Cikin kuma bada umarni yace.
“Yauwa Ramadan yanzu amshi takardar sunayen magungunan Malam ɗin kaje ka d’auko masa a pharmacy.”
Kai Ramadan ya jinjina tare da cewa.
“To.”
Cikin abunda bai wuce 2 minute ba kuwa Uncle Mustapha ya miƙawa Ramadan takardar sunayen magungunan.
Hakan yasa batare da wani b’ata lokaci ba, Ramadan din ya juya ya tafi, dan d’aukowa Malam din magungunan da zai nasha.
Bayan fitar Ramadan dinne kuma, Naseer ya kama Hannun Riyyam-nsra suma suka fice daga cikin falon.
Haka kuwa mutanen dake cikin falon suka dinga fita daya bayan daya.
Hardai saida falon ya rage daga Malam Mai-nasara sai Rayyern da kuma Uncle Mustapha, Alhaji Ibrahim, da kuma dayan kaninsu mai bimusu Alhaji Abdallah.
Alhaji Abdallah’n dinne kuma ya kalli Dr.Rayyern kana cikin sakin fuska yace.
“Masha Allah Dr. Rayyern munji dadin zuwanka k’warai, mun kuma gamsu da duk wasu bayanan da kayi mana, amma kafun zuwan ka da har mun gama yanke shawarar cewa zamu fitar da Malam din waje, can k’asar Egypt, Saboda ya samu kyakkyawar kulawa, amma dai yanzu Alhamdulillah tunda ga kanan, domin dama da way’anda zamu gani acan din da kuma kai d’in duk abu daya ne.”
Murmushi Rayyern yayi, kana anutse yace.
“A’a basai an fitar dashi ba, sauk’i na Allah Ne kuma Insha Allahu zai samu lafiya.”
“Allah Yasa.” Duk suka amsa cike da gamsuwa.
Yayinda Uncle Mustapha yad’an muskuta had’i da cewar.
“To Dr. Rayyern ka fad’amana kud’in maganin sainayi maka transfer ko.”
Kai Rayyern d’in ya girgiza, tare da hade kafafunsa waje daya ya tankwashe su.
Hannunsa na dama ya d’aura akan na Malam d’in, Cikin yanayin mutumtawa yace.
“A a ku barshi banzo nan dan abiyani ko sisin kobo ba, haka kuma duk wani magani dana sa Ramadan ya kawowa Malam banyi hakan dan abiyani ba, Malam mahaifi ne agareku ni kuma Kaka ne agareni, saboda haka komai da nayiwa Malam nayisa ne saboda matsayi da kuma darajarsa, fata na dai shine Allah Yabashi lafiya.”
“Ameen Summa Ameen.” Gaba ki d’ayansu suka had’a baki wajen fad’an hakan, Yayinda suka sake shaida mutumci, karamci da kuma kyakkyawar tarbiyar da Rayyern din ya samu, Lallai acikin zuk’atansu sun gamsu da cewar Rayyern d’in mutumin k’warai ne, wanda kuma ya taso a hannun iyayen k’warai.
Shikuwa Malam Mai-nasara murmushi ne ya fadada akan fuskarsa, domin kuwa alokacin da yaji Rayyern din ya kirasa da sunan Kaka, bakaramin sanyi yaji acikin zuciya da gangar jikinsa ba, Lallai Tabbas shima ya d’aukesa amatsayin jikansa.
Hannunsa na dama ya d’aura akan Rayyern d’in, Cikin kuma yanayin nuna godiyarsa agaresa yace.
“Masha Allah Allah Ubangiji yayi maka al'barka Rayyern, ya tsare gabanka da bayanka, ya kuma dauwamar da farinciki acikin zuciyarka da na ahalinka.”
Da “Ameen.” Duk suka amsa.
Inda Malam din ya sake d’ago Kai ya kalli Yayan nasa, cikin aminci yace.
“Tabbas Dr. Rayyern ya gwada mana karamcinsa, saboda haka kamar yanda ya daukeni amatsayin Kaka nima na daukesa amatsayin jikana, zan kumayi masa kyauta da karamci kamar yadda yayi mini, Ibrahim shiga cikin dakina, ka bude wajen da nake ajiye kayana na musamman ka d’auko masa sabbin alkyabba da hirami.”
Murmushin farinciki dukansu sukayi inda Alhaji Ibrahim kuwa ya mik’e cikin girmama maganan mahaifinnasu kaitsaye ya nufi dakin Malam Mai-nasara din dake cikin falon.
Har yakai bakin kofarne kuma ya juyo tare da Kallon mahaifin nasu, kana aladabce yace.
“Malam alkyabba da hiramin guda nawa za’a d’auko masa?”
“D’auko masa kala bakwai, saboda zasu fi isansa domin zai saka guda daya acikin kowacce rana, Kaga kenan kala bakwai zasu isar masa har sati guda yana sawa yana tunani.”
Kai Alhaji Ibrahim ya jinjina, tare da bud’e kofar dakin mahaifinnasu ya shige.
Cikin abunda bai wuce mintuna goma ba, kuwa sai gashi ya dawo hannayensa dauke da manya manyan alkyabba, da hirami irin wanda limaman makka suke sakawa ajikinsu, alkyabbu ne masu kyau da kuma tsadar gaske.
Mikawa Malam din Alhaji Ibrahim yayi, Yayinda shikuwa Malam din ya mikawa Rayyern dake zaune, wanda fara’a da kuma farincikinsa ya kasa b’uya.
“Wannan kyautace agareka Rayyern domin kuwa nasan zasuyi maka kyau sosai, shigace irin ta kamala.”
Kai Rayyern ya jinjina cike da tsananin jin dad’i kuma yace.
“Godiya nake maitarin yawa Malam, Allah ya kara arziki da lafiya.”
“Ameen.” Malam Mai-nasara din ya amsa cikin jin dadi.”
Dai-dai lokacin kuwa Ramadan Riyyam da kuma Naseer suka shigo cikin falon.
Karasowa Ramadan yayi ya mik’awa Hamman nasu babban ledan magungunan dake hannunsa.
Karb’an magungunan Rayyern yayi, hade kuma da mik’awa Ramadan alkyabba bakwai din daya same su amatsayin kyauta daga Malam.
“Kyauta na samu daga wajen Malam.”
Yafad’a adai-dai lokacin daya gama mikawa Ramadan din kayan.
Idanu Ramadan din yadan zaro fuskarsa cike da tsananin farinciki yace.
“Masha Allah Malam godiya muke.”
Hararan wasa Rayyern ya watsa masa, kana cikin sigar tsokana yace.
“Godiya muke kaman yaya, nawa nefa ba namu ba.”
Dariya kusan gaba dayansu suka sa, ciki kuwa harda Malam.
Riyyam kuwa jin hakanne yasashi, d’an shagwab’e fuska, tare da matsowa kusa da Malam din yace.
“Ayyah Kaka Malam toni Ina nawa alkyabban.”
Murmushi Malam Mainasara yayi, tare dasa hannu ya shafa kan Riyyama din.
“Kaima taka tananan tana jiranka amma sai ka ƙara girma, yanzu idan na baka yawa zasuyi maka.”
Malam din ya fada da matuk’ar kulawa.
Aikuwa Riyyam kamar dama abunda yake jira kenan, cikin yanayinsa na sakewa daya zame masa sabo, ya kalli Ramadan tare da cewa.
“Yeh za’abani ba za a bawa wani ba.” Ya kare maganan yana meyiwa Ramadan din gwalo.
Abunda ya matuk’ar bawa su Alhaji Ibrahim dariya kenan.
Shikuwa Ramadan durk’usawa agaban Malam din yayi, cikin sigarsa ta shagwab’a shima yace.
“Shikenan na fahimta yanzu wariyar launin fata za’a nunamin, da farko an bawa Hamma Rayyern alkyabba, yanzu kuma an shafa kan Riyyam amma ni ba a shafa nawa ba.”
Ayanzu kam Dariya Malam Mai-nasara yayi, har saida hakwaransa suka bayyana, cikin matsanancin kauna da kuma soyayyar yaran da yakeji acikin ransa, ya sa hannu ya dan jawo Ramadan din jikinsa.
Kansu ya shafa dukansu tare dayi musu addu’a, domin hakanan yakejinsu acikin zuciyarsa tamkar jikokinsa na gaske.
Rayyern kuwa duk abunda kannen nasa sukayi kallonsu kawai yakeyi, bayan kuma ya gama bare magungunan da ya kamata ace Malam din yasha ne, yasa Naseer ya miko masa bottle water marar sanyi.
Da kasan ya bawa Malam magungunan yasha.
Tare dayiwa su Alhaji Ibrahim bayanin yanda akullum Malam din zaina shan maganinsa.
Godiya sukayi mishi sosai, ganin da yayi kuma lokaci yadan ja sosai ne, yasa shi kallon su Ramadan tare da cewa su tashi su tafi.
Cikin aminci sukayi wa Malam din sallama, inda Rayyern ya shaida masa cewar zaidawo ya sake dubashi.
Koda suka tashi tafiya kuwa har wajen motocinsu Uncle Mustapha da kuma Alhaji Abdallah suka rakasu.
Basu koma cikin gidan ba kuma harsaida suka ga tafiyansu Rayyern din.
Daga b’angaren su Raayyern kuwa kaitsaye gida suka nufo.
Direct Rayyern dakinsa ya wuce, saboda yana son yin wanka, sannan akwai kuma wani aiki da zaiyi a laptop d’insa.
Yayinda su Ramadan da Riyyam kuwa, anan falo suka zauna inda Mom ta kawo musu abinci suka ci.
Bayan sun gama cin abincinne kuma suka wuce masallaci danyin sallan azahar, ciki kuwa harda Rayyern wanda ya sanja shigarsa zuwan wata farar jallabiya.
Jannart.
Kwance take akan makeken gadonta, wanda akoda yaushe yake shumfud’e da lallausan bedsheet na alfarma.
Irin kwanciyarnan ta rubda ciki tayi, Yayinda ajikinta take sanye da wata baby gown marar nauyi.
Lumsassun Idanunta ta ware ahankali tare kuma da sauke wani ajiyar zuciya mai
Cike da tarin damuwa.
Lallai Tabbas tana da buk’atar y’anci acikin rayuwarta, rayuwar da har yau ta kasa tantance wacce kalar rayuwa ce, rayuwar da kwata kwata babu haske acikinta sai tarin damuwa, kunci da kuma kadaici.
Mirgina wa tayi a hankali kana taci gaba da tunani.
Yayinda akowanni kwanan duniya da irin kalubalen da take fuskanta, acikin kowanni sa’a kuwa zuciyarta na bugawa da tarin tsananin tsoron abunda zaije ya dawo.
Lallai Tabbas tana da buk’atar haske acikin rayuwarta, haka kuma tana da buk’atar abokin rayuwar da akoda yaushe zai debe mata kewa, Sam arayuwarta batasan wani abu Waishi ingantaccen farinciki ba, akullum damuwa kawai da tsoro ta sani.
Haka kuma akowani bayan minti guda tsoronta yakan rub‘anya, tare da mummunan bugun zuciya akan abunda Yayanta Junaid ke neman aikata mata.
Saudayawan lokuta takan tambayi kanta, cewar shin Ya Junaid wani irin d’an uwane? Meyasa akoda yaushe bashi da fata ko buri saina keta haddinta?
Tabbas tunaninta yakan neman watsewa aduk lokacin da ta tuna cewar Ya Junaid din yayanta ne Uwa daya Uba daya.
Shin Meyasa Rayuwa take garari da ita?
Karar wayarta dake aje bisa bedsite ne ya katse mata duk wani tunanin da takeyi.
Ahankali tasa hannu ta share dan guntun hawayen dake kwance agefen Idanunta, wayartata dake ta faman tsuwa ta dauka, ganin kuma sunan Salman ne ke yawo akan screen din wayar yasata picking da dan hanzari.
“Y’ar Hutu wato kinanan kina hutawa agida ni kuma kinbarni da wahalan aikin ki ko.”
Cewar Salman.
Itakuwa Idanunta ta lumshe tare da d’an gyara kwanciyarta.
Cikin muryarta da tayi sanyi sosai tace.
Karb’an takardan Alhaji Ibrahim din yayi, tare da yiwa Rayyern d’in godiya maitarin yawa.
Saidai kuma baikai ga ida godiyar tasa ba, muryarsa ta mak’ale a kasan makoshinsa, sakamakon daura idanunsa da yayi akan sign din da Dr. Rayyern din yayi acan kasan paper’n.
Idanu ya k’urawa sign din cike da ɗan mamaki hadi da al’ajabi, ya d’ago ya kalli Baban nasu, wato Malam Mai-nasara da kuma sauran y’an uwansa.
Cikin tu’ajjudin da yake ciki dinne kuma direct ya mikowa Malam Mai-nasara din takardan.
Aikuwa Malam Mai-nasara na karb’an takardar idanunsa suka sauk’a akan signing din dama salon rubutun kanshi.
Cike da mamaki wanda har saida ya kasa b’oye hakan ya d’ago ya kalli Rayyern.
Rayyern kuwa da Sam bai fahimci komai adangane da irin Kallon da yaga sunayiwa takardar ba, kwata kwata sam baidamu ba.
Saima juyowa da yayi ya kalli Ramadan.
Cikin kuma bada umarni yace.
“Yauwa Ramadan yanzu amshi takardar sunayen magungunan Malam ɗin kaje ka d’auko masa a pharmacy.”
Kai Ramadan ya jinjina tare da cewa.
“To.”
Cikin abunda bai wuce 2 minute ba kuwa Uncle Mustapha ya miƙawa Ramadan takardar sunayen magungunan.
Hakan yasa batare da wani b’ata lokaci ba, Ramadan din ya juya ya tafi, dan d’aukowa Malam din magungunan da zai nasha.
Bayan fitar Ramadan dinne kuma, Naseer ya kama Hannun Riyyam-nsra suma suka fice daga cikin falon.
Haka kuwa mutanen dake cikin falon suka dinga fita daya bayan daya.
Hardai saida falon ya rage daga Malam Mai-nasara sai Rayyern da kuma Uncle Mustapha, Alhaji Ibrahim, da kuma dayan kaninsu mai bimusu Alhaji Abdallah.
Alhaji Abdallah’n dinne kuma ya kalli Dr.Rayyern kana cikin sakin fuska yace.
“Masha Allah Dr. Rayyern munji dadin zuwanka k’warai, mun kuma gamsu da duk wasu bayanan da kayi mana, amma kafun zuwan ka da har mun gama yanke shawarar cewa zamu fitar da Malam din waje, can k’asar Egypt, Saboda ya samu kyakkyawar kulawa, amma dai yanzu Alhamdulillah tunda ga kanan, domin dama da way’anda zamu gani acan din da kuma kai d’in duk abu daya ne.”
Murmushi Rayyern yayi, kana anutse yace.
“A’a basai an fitar dashi ba, sauk’i na Allah Ne kuma Insha Allahu zai samu lafiya.”
“Allah Yasa.” Duk suka amsa cike da gamsuwa.
Yayinda Uncle Mustapha yad’an muskuta had’i da cewar.
“To Dr. Rayyern ka fad’amana kud’in maganin sainayi maka transfer ko.”
Kai Rayyern d’in ya girgiza, tare da hade kafafunsa waje daya ya tankwashe su.
Hannunsa na dama ya d’aura akan na Malam d’in, Cikin yanayin mutumtawa yace.
“A a ku barshi banzo nan dan abiyani ko sisin kobo ba, haka kuma duk wani magani dana sa Ramadan ya kawowa Malam banyi hakan dan abiyani ba, Malam mahaifi ne agareku ni kuma Kaka ne agareni, saboda haka komai da nayiwa Malam nayisa ne saboda matsayi da kuma darajarsa, fata na dai shine Allah Yabashi lafiya.”
“Ameen Summa Ameen.” Gaba ki d’ayansu suka had’a baki wajen fad’an hakan, Yayinda suka sake shaida mutumci, karamci da kuma kyakkyawar tarbiyar da Rayyern din ya samu, Lallai acikin zuk’atansu sun gamsu da cewar Rayyern d’in mutumin k’warai ne, wanda kuma ya taso a hannun iyayen k’warai.
Shikuwa Malam Mai-nasara murmushi ne ya fadada akan fuskarsa, domin kuwa alokacin da yaji Rayyern din ya kirasa da sunan Kaka, bakaramin sanyi yaji acikin zuciya da gangar jikinsa ba, Lallai Tabbas shima ya d’aukesa amatsayin jikansa.
Hannunsa na dama ya d’aura akan Rayyern d’in, Cikin kuma yanayin nuna godiyarsa agaresa yace.
“Masha Allah Allah Ubangiji yayi maka al'barka Rayyern, ya tsare gabanka da bayanka, ya kuma dauwamar da farinciki acikin zuciyarka da na ahalinka.”
Da “Ameen.” Duk suka amsa.
Inda Malam din ya sake d’ago Kai ya kalli Yayan nasa, cikin aminci yace.
“Tabbas Dr. Rayyern ya gwada mana karamcinsa, saboda haka kamar yanda ya daukeni amatsayin Kaka nima na daukesa amatsayin jikana, zan kumayi masa kyauta da karamci kamar yadda yayi mini, Ibrahim shiga cikin dakina, ka bude wajen da nake ajiye kayana na musamman ka d’auko masa sabbin alkyabba da hirami.”
Murmushin farinciki dukansu sukayi inda Alhaji Ibrahim kuwa ya mik’e cikin girmama maganan mahaifinnasu kaitsaye ya nufi dakin Malam Mai-nasara din dake cikin falon.
Har yakai bakin kofarne kuma ya juyo tare da Kallon mahaifin nasu, kana aladabce yace.
“Malam alkyabba da hiramin guda nawa za’a d’auko masa?”
“D’auko masa kala bakwai, saboda zasu fi isansa domin zai saka guda daya acikin kowacce rana, Kaga kenan kala bakwai zasu isar masa har sati guda yana sawa yana tunani.”
Kai Alhaji Ibrahim ya jinjina, tare da bud’e kofar dakin mahaifinnasu ya shige.
Cikin abunda bai wuce mintuna goma ba, kuwa sai gashi ya dawo hannayensa dauke da manya manyan alkyabba, da hirami irin wanda limaman makka suke sakawa ajikinsu, alkyabbu ne masu kyau da kuma tsadar gaske.
Mikawa Malam din Alhaji Ibrahim yayi, Yayinda shikuwa Malam din ya mikawa Rayyern dake zaune, wanda fara’a da kuma farincikinsa ya kasa b’uya.
“Wannan kyautace agareka Rayyern domin kuwa nasan zasuyi maka kyau sosai, shigace irin ta kamala.”
Kai Rayyern ya jinjina cike da tsananin jin dad’i kuma yace.
“Godiya nake maitarin yawa Malam, Allah ya kara arziki da lafiya.”
“Ameen.” Malam Mai-nasara din ya amsa cikin jin dadi.”
Dai-dai lokacin kuwa Ramadan Riyyam da kuma Naseer suka shigo cikin falon.
Karasowa Ramadan yayi ya mik’awa Hamman nasu babban ledan magungunan dake hannunsa.
Karb’an magungunan Rayyern yayi, hade kuma da mik’awa Ramadan alkyabba bakwai din daya same su amatsayin kyauta daga Malam.
“Kyauta na samu daga wajen Malam.”
Yafad’a adai-dai lokacin daya gama mikawa Ramadan din kayan.
Idanu Ramadan din yadan zaro fuskarsa cike da tsananin farinciki yace.
“Masha Allah Malam godiya muke.”
Hararan wasa Rayyern ya watsa masa, kana cikin sigar tsokana yace.
“Godiya muke kaman yaya, nawa nefa ba namu ba.”
Dariya kusan gaba dayansu suka sa, ciki kuwa harda Malam.
Riyyam kuwa jin hakanne yasashi, d’an shagwab’e fuska, tare da matsowa kusa da Malam din yace.
“Ayyah Kaka Malam toni Ina nawa alkyabban.”
Murmushi Malam Mainasara yayi, tare dasa hannu ya shafa kan Riyyama din.
“Kaima taka tananan tana jiranka amma sai ka ƙara girma, yanzu idan na baka yawa zasuyi maka.”
Malam din ya fada da matuk’ar kulawa.
Aikuwa Riyyam kamar dama abunda yake jira kenan, cikin yanayinsa na sakewa daya zame masa sabo, ya kalli Ramadan tare da cewa.
“Yeh za’abani ba za a bawa wani ba.” Ya kare maganan yana meyiwa Ramadan din gwalo.
Abunda ya matuk’ar bawa su Alhaji Ibrahim dariya kenan.
Shikuwa Ramadan durk’usawa agaban Malam din yayi, cikin sigarsa ta shagwab’a shima yace.
“Shikenan na fahimta yanzu wariyar launin fata za’a nunamin, da farko an bawa Hamma Rayyern alkyabba, yanzu kuma an shafa kan Riyyam amma ni ba a shafa nawa ba.”
Ayanzu kam Dariya Malam Mai-nasara yayi, har saida hakwaransa suka bayyana, cikin matsanancin kauna da kuma soyayyar yaran da yakeji acikin ransa, ya sa hannu ya dan jawo Ramadan din jikinsa.
Kansu ya shafa dukansu tare dayi musu addu’a, domin hakanan yakejinsu acikin zuciyarsa tamkar jikokinsa na gaske.
Rayyern kuwa duk abunda kannen nasa sukayi kallonsu kawai yakeyi, bayan kuma ya gama bare magungunan da ya kamata ace Malam din yasha ne, yasa Naseer ya miko masa bottle water marar sanyi.
Da kasan ya bawa Malam magungunan yasha.
Tare dayiwa su Alhaji Ibrahim bayanin yanda akullum Malam din zaina shan maganinsa.
Godiya sukayi mishi sosai, ganin da yayi kuma lokaci yadan ja sosai ne, yasa shi kallon su Ramadan tare da cewa su tashi su tafi.
Cikin aminci sukayi wa Malam din sallama, inda Rayyern ya shaida masa cewar zaidawo ya sake dubashi.
Koda suka tashi tafiya kuwa har wajen motocinsu Uncle Mustapha da kuma Alhaji Abdallah suka rakasu.
Basu koma cikin gidan ba kuma harsaida suka ga tafiyansu Rayyern din.
Daga b’angaren su Raayyern kuwa kaitsaye gida suka nufo.
Direct Rayyern dakinsa ya wuce, saboda yana son yin wanka, sannan akwai kuma wani aiki da zaiyi a laptop d’insa.
Yayinda su Ramadan da Riyyam kuwa, anan falo suka zauna inda Mom ta kawo musu abinci suka ci.
Bayan sun gama cin abincinne kuma suka wuce masallaci danyin sallan azahar, ciki kuwa harda Rayyern wanda ya sanja shigarsa zuwan wata farar jallabiya.
Jannart.
Kwance take akan makeken gadonta, wanda akoda yaushe yake shumfud’e da lallausan bedsheet na alfarma.
Irin kwanciyarnan ta rubda ciki tayi, Yayinda ajikinta take sanye da wata baby gown marar nauyi.
Lumsassun Idanunta ta ware ahankali tare kuma da sauke wani ajiyar zuciya mai
Cike da tarin damuwa.
Lallai Tabbas tana da buk’atar y’anci acikin rayuwarta, rayuwar da har yau ta kasa tantance wacce kalar rayuwa ce, rayuwar da kwata kwata babu haske acikinta sai tarin damuwa, kunci da kuma kadaici.
Mirgina wa tayi a hankali kana taci gaba da tunani.
Yayinda akowanni kwanan duniya da irin kalubalen da take fuskanta, acikin kowanni sa’a kuwa zuciyarta na bugawa da tarin tsananin tsoron abunda zaije ya dawo.
Lallai Tabbas tana da buk’atar haske acikin rayuwarta, haka kuma tana da buk’atar abokin rayuwar da akoda yaushe zai debe mata kewa, Sam arayuwarta batasan wani abu Waishi ingantaccen farinciki ba, akullum damuwa kawai da tsoro ta sani.
Haka kuma akowani bayan minti guda tsoronta yakan rub‘anya, tare da mummunan bugun zuciya akan abunda Yayanta Junaid ke neman aikata mata.
Saudayawan lokuta takan tambayi kanta, cewar shin Ya Junaid wani irin d’an uwane? Meyasa akoda yaushe bashi da fata ko buri saina keta haddinta?
Tabbas tunaninta yakan neman watsewa aduk lokacin da ta tuna cewar Ya Junaid din yayanta ne Uwa daya Uba daya.
Shin Meyasa Rayuwa take garari da ita?
Karar wayarta dake aje bisa bedsite ne ya katse mata duk wani tunanin da takeyi.
Ahankali tasa hannu ta share dan guntun hawayen dake kwance agefen Idanunta, wayartata dake ta faman tsuwa ta dauka, ganin kuma sunan Salman ne ke yawo akan screen din wayar yasata picking da dan hanzari.
“Y’ar Hutu wato kinanan kina hutawa agida ni kuma kinbarni da wahalan aikin ki ko.”
Cewar Salman.
Itakuwa Idanunta ta lumshe tare da d’an gyara kwanciyarta.
Cikin muryarta da tayi sanyi sosai tace.