Sashe 27
Tubali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
K’arasawa yayi wajen tarin dokunan da akeyin wasan dasu, tare da zab’o wani farin doki, wanda mafi yawanci idan yazo shi yake hawa.
Batare da wani bata lokaci ba kuma ya dale saman dokin tare da rik’e Sandar buga k’wallon nasa ya soma sukuwa, tare da gabatar da wasan.
Mai-nasara hospital.
Salman da kuma Jannart dake tsaye abakin k’ofar office d’inne suka tsaya suna Kallon juna.
Salman ne ya gyara tsayuwarsa tare da cewa.
“Please Jananrt mushiga mana, kinfi kowa sanin irin wahalan da muka sha, kafun mu samu aka nuna mana wannan office din, wannan ita kadaice daman mu ta karshe, kada muyi wasa da ita.”
Kai Jannart ta jinjina kana asanyaye tace.
“To.”
Knocking kofar Salman yayi, inda Dr Sulaiman dake zaune akan wata hamshakiyar kujera ya bada izinin shigowa.
Hakanne kuwa yasa suka kutsa Kai suka shiga bakinsu d’auke da sallama.
Amsa musu sallaman Sulaiman yayi, tare da dago kansa ya kallesu.
D’an Kallon juna suka tsayayi na tsawon sakanni, kafun daga bisani Dr.Sulaiman din yace.
“Bismillah’nku.”
Ya kare maganan yana meyi musu nuni da wasu kujeru guda biyu dake gabansa.
Yayinda kuma acikin mintuna kadan na Kallon daya musu, ya fahimci cewar sudin ba marassa lafiya bane.
Zama sukayi akan kujerun daya nuna musu d’in, Salman ne ya mik’awa Sulaiman din hannu suka gaisa, Yayinda ita kuma Jannart ta gaidashi da sassanyar muryarta, wanda har hakan yasa shi kasa jurewa saida ya dago ya sake Kallon ta, Yayinda azuciyarsa yake mamakin jin ta gaishe shi da Hausa, domin sam baiyi mata Kallon y’ar Nigeria kuma maijin Hausa ba, kasancewar yanayin kamannin ta da kuma shigarta da tsarinta dabanne, bawai irin normal mata da kowa ya sani bane, ita din akwai abu na musamman atattare da ita, wanda kowanni irin Namiji idan ya kalleta saiya gane hakan.
“Meke tafe daku? Ko kuma patient kuka kawo?.”
Salaiman ya tambaya.
Jin hakan ne yasa Salman d’an gyara zama, tare da fuskarta Sulaiman d’in, kana atausashe yace.
“Sunana Salman Aliyu, wannan kuma abokiyar aikina ce sunanta Jannart Idi Sale Dakata, Mu y’an Jarida ne, ma’aikata Tashar Arewa24.”
ID Card d’insu suka zaro tare da nunawa Salaiman daya zuba musu ido.
Salman ne ya cigaba da cewa.
“Munzo nanne bisa dogaro da kuma fatan, dacewar samun ganin Dr.Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara, Dan Allah Dr. Idan akwai taimakon da zakayi mana, ka taimaka muganshi, wallahi ganin nasa nada matuk’ar muhimmmanci, musamman ga Jannart.”
Ajiyar zuciya Sulaiman ya sauke, tare da maida hankalinsa ga Jannart, domin kuwa idan har abunda tunaninsa ya basa gaskiya ne, to Lallai ya kamata ace ya taimaka musu.
Domin ya raya aransa cewa aiki aka basu domin su tattauna da Dr.Rayyern d’in.
Zamansa ya gyara kana anutse yace.
“Babu damuwa tunda dai harkunzo nan Insha Allah zaku gansa, duk da cewar ayanzu baya cikin hospital d’in, amma Ina da tabbacin inda zaku sameshi, saidai kuma ganin nasa ba shine ba, dan Ina da tabbacin ba lallaine Dr. Rayyern ya amince kuyi hira dashi ba, saboda aduk k’asarnan babu wani gidan Jarida daya tab’a amincewa sukayi hira dashi.”
Idanu Jannart ta d’an lumshe ahankali, Yayinda ajikinta takejin Wannan shine last chance dinta, akasin haka kuwa zata iya rasa aikinta, wanda kuma shine ke sata acikin farinciki.
D’an cije labb’an bakinta tayi, kana cikin siririyar muryarta tace.
“Please Dr. I need your help please!! Banason nayi losing job d’ina!!!”
Takai k’arshen maganan muryarta araunane.
Wanda hakan yasa Dr.Sulaiman Jin tausayin yarinyar, saidai kuma har acikin zuciyarsa yayi mamakin, Jin tace bataso ta rasa aikinta.
Domin yasan kamarta dinnan ba ace daga gidan talakawa ta fito ba, Sam Kwata-kwata ma batayi kama da hakan ba bare kuma waye bai san sunan mahaifintaba Alhaji idi Saleh Dakata.
Sake gyara zamansa yayi, tare da cewa.
“Badamuwa zan taimaka muku Insha Allah, yau Wednessday kuma duk ranan wednessday at this time Dr. Rayyern yakan je wajen wasan Polo, ba kuma ya barin wajen sai 5 na yamma, saboda haka zan baku Andreas din wajen, zakuma ku iya zuwa kusa meshi.
Wani irin sanyi Jannart taji acikin zuciyarta, Yayinda Salman kuwa yayiwa Dr.Sulaiman din Godiya.
Shikuwa Dr. Sulaiman a paper ya rubuta musu adress din wajen, tare kuma da yi musu fatan nasara.
Godiya sosai sukayi masa kafun sukayi masa sallama, cikin hanzari suka fito daga cikin asibitin.
Direct wajen da motar Salman din ke fake suka nufa.
Suna shiga kuwa ya tada motar suka nufi wajen buga wasan Polo’n kaitsaye.
Tafiyar da bata wuce ta 20mn sukayi ba, sai gasu abakin kofar babban mashigar wajen wasan Polo’n da yake duka a unguwa ɗaya ce.
Bayan kuma Salman yayi parking motar ne suka fito, direct mashigan wajen suka nufa.
Amma sai guard din dake tsaron wajen suka dakatar dasu, had’e da cewa bazasu shiga ba, anyi clossing wajen na two hours, suje anjima su dawo.
Rau-rau Jannart tayi da ido, Yayinda Salman kuwa ya zaro ID card d’insa ya nuna musu, cikin sanin makamar aikinsa kuma yace.
“Mu y’an Jarida ne, ankuma tabbatar mana da cewar mutumin da muke nema yana cikin wajen nan, please dan Allah kubari mugansa, abune na gaggawa.”
Dan Kallon juna guard din sukayi, kaman zasu hanasu kuma sai suka matsa musu alaman su shige.
Aikuwa wani irin sanyi Jannart taji zuciyarta tayi, cikin sauri kuwa suka sakai suka wuce cikin wajen.
Y’an tsirarun mutanen dake wajen suka soma wuce wa, ganin kuma kamar babu alaman yalwan mutane awajenne yasa sukayi tsaya, saboda su kansu basu San ta Ina zasu fara nemansa ba.
Jannart dinne ta kalli Salman kana zuciyarta akarye tace.
“Anya kuwa Salman kana ga zamu sameshi anan wajen?”
Shiru Salman din yayi, alamun nazari dai-dai lokacin kuwa wani ma’aikacin wajen yazo gilmawa ta gabansu.
Salman dinne ya tare mutumin, tare da cewa.
“Dan Allah Malam muna tambaya ne,".
"Allah yasa na sani."
Ya basu amsa yana kallon Jannart.
Numfashin gajiya Salman ya sauƙe tare da cewa.
"Please Dr. Rayyern Basheer Mainasara muke nema.”
Idanu sauran ma’aikatan wajen da sukaji abunda Salman din ya fada suka zuba musu.
Shikuwa wanda Salman din ya tambaya, kansa ya girgiza cike da mamaki kuma yace.
“Dr. Rayyern Bashir Mai-nasara kuma anan wajen? gaskiya bana tunanin hakan, saboda muma bamu sanshi ba, sunansa kawai dai mukeji, amma dama yana zuwa nan dinne.”
Baki Jannart ta cije tare da sanya hannayenta ta kama waist dinta.
Cike da takaici tace.
“Again na sake rasa damata.”
“Calm down Jannart, mu k’arasa can cikin wajen mu duba ko zamu dace.”
Salman ya ce mata.
Fuskarta ta kwab’e saboda zuwa yanzu ta fara gajiya da gantalin neman mutumin tunda shi ba kuɗi bane.
Amma da yake ta San wannan din shine last hope dinta, hakan yasa tabi bayan Salman suka shige cikin inda ake gudanar da asalin wasan Polo din.
A dai-dai lokacin kuwa Rayyern yayi nisa acikin wasan nasa, sai sukuwa yakeyi akan doki cike da k’warewa da jin daɗin yanayin wurin shiru ba hayani ba mai takura mishi.
Yayinda kuma ya kasance shi kad’ai ne awajen yake sashi karsashi.
D’an shigowa su Jannart da Salman sukayi Cikin wajen, Saidai kuma ganin da sukayi babu kowa awajenne yasa Jannart jingina bayanta da jikin wani k’arfe.
Akasalance tace.
“Salman zuwa yanzu Tabbas inaji ajikina cewar na kusa rasa aikina, wannan ɗan is ɗin mutumin ba saukin ganine dashi ba, kalli wajen nan fa babu kowa sai wancan mutumin daya bamu baya yana ta sukuwa akan doki shima ɗaya kamar mara aikin yi.”
Takai karshen maganan nata tana me Kallon bayan Dr Rayyern, da yake nesa dasu sosai.
Dan kallonta Salman yayi cikin kuma son k’arfafa mata guiwa yace.
“Karki damu Jannart Insha Allah zamu hadu dashi, Yanzu dai mukarasa wajen wancan mutumin sai mu tambayeshi koya San wani abu dangane da wanda muke nema.”
Still fuskarta ta kwab’e tare da cewa.
“shikenan muje.”
Hakan kuwa akayi inda suka k’arasa shiga can cikin wajen wasan dake malale da koriyar ciyawa mai cike da damshi.
Suna kara kusantan cikin wurin wasanne kuwa Rayyern din ya juyo da akalar dokinsa.
Sai-dai kuma Sam baisauke idanunsa akansu ba.
Idanu gaba dayansu suka zazzaro, Yayinda Jannart kuwa cike da mamaki tadan matsa bayan Salman.
Tana fadin
“Laaa Salman wannan mutumin nefa da na fasawa waya a airport, wayyo Allah Salman nikam kazo mu gudu, tun kafun ma ya ganmu.”
Kai Salman din ya girgiza tare da cewa.
“Mu gudu kuma Jannart? saikace marasa gskiya muje dai ki bashi hakuri dama ai aranar baki bashi hakuri ba, daga ganinsa ma Babban mutum ne watakila ma zai iya taimaka mana muga Dr. Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara din.”
Fiki-fiki tayi da idanunta, kana adan tsorace tace.
“Shikenan muje.”
Nanfa suka nufi wajen Rayyern d’in.
Dai-dai lokacin kuwa Rayyern dayake matuk’ar gudu akan doki, batare daya d’ago ko waiwaye ba ya taho aguje.
Kaitsaye kuma direct inda su Jannart d’in ke tsaye ya nufa.
Gadan gadan.
Su Jannart din kuwa kansu basu ankar ba, saida dokin ya kusan zuwa gab dasu.
Wani irin k’ara mai cike da tsoro da firgici Jannart ta saka da karfi, tare kuma da daura hannayenta akanta ta rumtse Idanunta k’am, domin ta gama sadak’arwa akan cewar dokin ya nuk’urk’usheta ma angama lokaci ɗaya numfashin ta ya fara fizgan firgici.
Domin hatta Salman dake gefenta shima yayi surrender.
Rayyern kuwa Sam bai Ankara ba saida ihun Jannart din ya shiga dodon kunnensa, wanda hakan yasa cikin sauri ya dago kansa.
Ganin yana gab da bi ta kansu ne, yasashi saurin.
Damƙe igiyar linzamin dokin da ƙarfi ya tsayar dashi cak.
Saboda ganin macen da yayi agabansa ne kuma ya sashi dirowa daga saman dokin.
Bayan ya juyashi.
Wani irin dogon tsaki yaja.
Tare da Kallon Salman wanda keta sauk’e ajiyar zuciya, kana ya watsawa Jannart din dake gabansa wani kallon da yasa cikinta ya murda ya haɗe da numfashin dake sauya salon fita da shiga.
Cikin tsuke fuska yace.
“Bakwa ganine, yanzu idan da nabi takanku fa?”
“Kayi hakuri dan Allah!” Salman ya fad’a asanyaye.
Itakuwa Jannart sai ayanzu ta bud’e idanunta, Yayinda gaba daya jikinta ke kakkarwa.
Hannu tasa ta dafe ƙirjinta.
Rayyern kuwa y’ar gajerar tsaki yaja, batare kuma daya sake ce musu komai ba ya juya ya nufi inda kayayyakinsa suke.
Batare da wani bata lokaci ba kuma ya dale saman dokin tare da rik’e Sandar buga k’wallon nasa ya soma sukuwa, tare da gabatar da wasan.
Mai-nasara hospital.
Salman da kuma Jannart dake tsaye abakin k’ofar office d’inne suka tsaya suna Kallon juna.
Salman ne ya gyara tsayuwarsa tare da cewa.
“Please Jananrt mushiga mana, kinfi kowa sanin irin wahalan da muka sha, kafun mu samu aka nuna mana wannan office din, wannan ita kadaice daman mu ta karshe, kada muyi wasa da ita.”
Kai Jannart ta jinjina kana asanyaye tace.
“To.”
Knocking kofar Salman yayi, inda Dr Sulaiman dake zaune akan wata hamshakiyar kujera ya bada izinin shigowa.
Hakanne kuwa yasa suka kutsa Kai suka shiga bakinsu d’auke da sallama.
Amsa musu sallaman Sulaiman yayi, tare da dago kansa ya kallesu.
D’an Kallon juna suka tsayayi na tsawon sakanni, kafun daga bisani Dr.Sulaiman din yace.
“Bismillah’nku.”
Ya kare maganan yana meyi musu nuni da wasu kujeru guda biyu dake gabansa.
Yayinda kuma acikin mintuna kadan na Kallon daya musu, ya fahimci cewar sudin ba marassa lafiya bane.
Zama sukayi akan kujerun daya nuna musu d’in, Salman ne ya mik’awa Sulaiman din hannu suka gaisa, Yayinda ita kuma Jannart ta gaidashi da sassanyar muryarta, wanda har hakan yasa shi kasa jurewa saida ya dago ya sake Kallon ta, Yayinda azuciyarsa yake mamakin jin ta gaishe shi da Hausa, domin sam baiyi mata Kallon y’ar Nigeria kuma maijin Hausa ba, kasancewar yanayin kamannin ta da kuma shigarta da tsarinta dabanne, bawai irin normal mata da kowa ya sani bane, ita din akwai abu na musamman atattare da ita, wanda kowanni irin Namiji idan ya kalleta saiya gane hakan.
“Meke tafe daku? Ko kuma patient kuka kawo?.”
Salaiman ya tambaya.
Jin hakan ne yasa Salman d’an gyara zama, tare da fuskarta Sulaiman d’in, kana atausashe yace.
“Sunana Salman Aliyu, wannan kuma abokiyar aikina ce sunanta Jannart Idi Sale Dakata, Mu y’an Jarida ne, ma’aikata Tashar Arewa24.”
ID Card d’insu suka zaro tare da nunawa Salaiman daya zuba musu ido.
Salman ne ya cigaba da cewa.
“Munzo nanne bisa dogaro da kuma fatan, dacewar samun ganin Dr.Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara, Dan Allah Dr. Idan akwai taimakon da zakayi mana, ka taimaka muganshi, wallahi ganin nasa nada matuk’ar muhimmmanci, musamman ga Jannart.”
Ajiyar zuciya Sulaiman ya sauke, tare da maida hankalinsa ga Jannart, domin kuwa idan har abunda tunaninsa ya basa gaskiya ne, to Lallai ya kamata ace ya taimaka musu.
Domin ya raya aransa cewa aiki aka basu domin su tattauna da Dr.Rayyern d’in.
Zamansa ya gyara kana anutse yace.
“Babu damuwa tunda dai harkunzo nan Insha Allah zaku gansa, duk da cewar ayanzu baya cikin hospital d’in, amma Ina da tabbacin inda zaku sameshi, saidai kuma ganin nasa ba shine ba, dan Ina da tabbacin ba lallaine Dr. Rayyern ya amince kuyi hira dashi ba, saboda aduk k’asarnan babu wani gidan Jarida daya tab’a amincewa sukayi hira dashi.”
Idanu Jannart ta d’an lumshe ahankali, Yayinda ajikinta takejin Wannan shine last chance dinta, akasin haka kuwa zata iya rasa aikinta, wanda kuma shine ke sata acikin farinciki.
D’an cije labb’an bakinta tayi, kana cikin siririyar muryarta tace.
“Please Dr. I need your help please!! Banason nayi losing job d’ina!!!”
Takai k’arshen maganan muryarta araunane.
Wanda hakan yasa Dr.Sulaiman Jin tausayin yarinyar, saidai kuma har acikin zuciyarsa yayi mamakin, Jin tace bataso ta rasa aikinta.
Domin yasan kamarta dinnan ba ace daga gidan talakawa ta fito ba, Sam Kwata-kwata ma batayi kama da hakan ba bare kuma waye bai san sunan mahaifintaba Alhaji idi Saleh Dakata.
Sake gyara zamansa yayi, tare da cewa.
“Badamuwa zan taimaka muku Insha Allah, yau Wednessday kuma duk ranan wednessday at this time Dr. Rayyern yakan je wajen wasan Polo, ba kuma ya barin wajen sai 5 na yamma, saboda haka zan baku Andreas din wajen, zakuma ku iya zuwa kusa meshi.
Wani irin sanyi Jannart taji acikin zuciyarta, Yayinda Salman kuwa yayiwa Dr.Sulaiman din Godiya.
Shikuwa Dr. Sulaiman a paper ya rubuta musu adress din wajen, tare kuma da yi musu fatan nasara.
Godiya sosai sukayi masa kafun sukayi masa sallama, cikin hanzari suka fito daga cikin asibitin.
Direct wajen da motar Salman din ke fake suka nufa.
Suna shiga kuwa ya tada motar suka nufi wajen buga wasan Polo’n kaitsaye.
Tafiyar da bata wuce ta 20mn sukayi ba, sai gasu abakin kofar babban mashigar wajen wasan Polo’n da yake duka a unguwa ɗaya ce.
Bayan kuma Salman yayi parking motar ne suka fito, direct mashigan wajen suka nufa.
Amma sai guard din dake tsaron wajen suka dakatar dasu, had’e da cewa bazasu shiga ba, anyi clossing wajen na two hours, suje anjima su dawo.
Rau-rau Jannart tayi da ido, Yayinda Salman kuwa ya zaro ID card d’insa ya nuna musu, cikin sanin makamar aikinsa kuma yace.
“Mu y’an Jarida ne, ankuma tabbatar mana da cewar mutumin da muke nema yana cikin wajen nan, please dan Allah kubari mugansa, abune na gaggawa.”
Dan Kallon juna guard din sukayi, kaman zasu hanasu kuma sai suka matsa musu alaman su shige.
Aikuwa wani irin sanyi Jannart taji zuciyarta tayi, cikin sauri kuwa suka sakai suka wuce cikin wajen.
Y’an tsirarun mutanen dake wajen suka soma wuce wa, ganin kuma kamar babu alaman yalwan mutane awajenne yasa sukayi tsaya, saboda su kansu basu San ta Ina zasu fara nemansa ba.
Jannart dinne ta kalli Salman kana zuciyarta akarye tace.
“Anya kuwa Salman kana ga zamu sameshi anan wajen?”
Shiru Salman din yayi, alamun nazari dai-dai lokacin kuwa wani ma’aikacin wajen yazo gilmawa ta gabansu.
Salman dinne ya tare mutumin, tare da cewa.
“Dan Allah Malam muna tambaya ne,".
"Allah yasa na sani."
Ya basu amsa yana kallon Jannart.
Numfashin gajiya Salman ya sauƙe tare da cewa.
"Please Dr. Rayyern Basheer Mainasara muke nema.”
Idanu sauran ma’aikatan wajen da sukaji abunda Salman din ya fada suka zuba musu.
Shikuwa wanda Salman din ya tambaya, kansa ya girgiza cike da mamaki kuma yace.
“Dr. Rayyern Bashir Mai-nasara kuma anan wajen? gaskiya bana tunanin hakan, saboda muma bamu sanshi ba, sunansa kawai dai mukeji, amma dama yana zuwa nan dinne.”
Baki Jannart ta cije tare da sanya hannayenta ta kama waist dinta.
Cike da takaici tace.
“Again na sake rasa damata.”
“Calm down Jannart, mu k’arasa can cikin wajen mu duba ko zamu dace.”
Salman ya ce mata.
Fuskarta ta kwab’e saboda zuwa yanzu ta fara gajiya da gantalin neman mutumin tunda shi ba kuɗi bane.
Amma da yake ta San wannan din shine last hope dinta, hakan yasa tabi bayan Salman suka shige cikin inda ake gudanar da asalin wasan Polo din.
A dai-dai lokacin kuwa Rayyern yayi nisa acikin wasan nasa, sai sukuwa yakeyi akan doki cike da k’warewa da jin daɗin yanayin wurin shiru ba hayani ba mai takura mishi.
Yayinda kuma ya kasance shi kad’ai ne awajen yake sashi karsashi.
D’an shigowa su Jannart da Salman sukayi Cikin wajen, Saidai kuma ganin da sukayi babu kowa awajenne yasa Jannart jingina bayanta da jikin wani k’arfe.
Akasalance tace.
“Salman zuwa yanzu Tabbas inaji ajikina cewar na kusa rasa aikina, wannan ɗan is ɗin mutumin ba saukin ganine dashi ba, kalli wajen nan fa babu kowa sai wancan mutumin daya bamu baya yana ta sukuwa akan doki shima ɗaya kamar mara aikin yi.”
Takai karshen maganan nata tana me Kallon bayan Dr Rayyern, da yake nesa dasu sosai.
Dan kallonta Salman yayi cikin kuma son k’arfafa mata guiwa yace.
“Karki damu Jannart Insha Allah zamu hadu dashi, Yanzu dai mukarasa wajen wancan mutumin sai mu tambayeshi koya San wani abu dangane da wanda muke nema.”
Still fuskarta ta kwab’e tare da cewa.
“shikenan muje.”
Hakan kuwa akayi inda suka k’arasa shiga can cikin wajen wasan dake malale da koriyar ciyawa mai cike da damshi.
Suna kara kusantan cikin wurin wasanne kuwa Rayyern din ya juyo da akalar dokinsa.
Sai-dai kuma Sam baisauke idanunsa akansu ba.
Idanu gaba dayansu suka zazzaro, Yayinda Jannart kuwa cike da mamaki tadan matsa bayan Salman.
Tana fadin
“Laaa Salman wannan mutumin nefa da na fasawa waya a airport, wayyo Allah Salman nikam kazo mu gudu, tun kafun ma ya ganmu.”
Kai Salman din ya girgiza tare da cewa.
“Mu gudu kuma Jannart? saikace marasa gskiya muje dai ki bashi hakuri dama ai aranar baki bashi hakuri ba, daga ganinsa ma Babban mutum ne watakila ma zai iya taimaka mana muga Dr. Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara din.”
Fiki-fiki tayi da idanunta, kana adan tsorace tace.
“Shikenan muje.”
Nanfa suka nufi wajen Rayyern d’in.
Dai-dai lokacin kuwa Rayyern dayake matuk’ar gudu akan doki, batare daya d’ago ko waiwaye ba ya taho aguje.
Kaitsaye kuma direct inda su Jannart d’in ke tsaye ya nufa.
Gadan gadan.
Su Jannart din kuwa kansu basu ankar ba, saida dokin ya kusan zuwa gab dasu.
Wani irin k’ara mai cike da tsoro da firgici Jannart ta saka da karfi, tare kuma da daura hannayenta akanta ta rumtse Idanunta k’am, domin ta gama sadak’arwa akan cewar dokin ya nuk’urk’usheta ma angama lokaci ɗaya numfashin ta ya fara fizgan firgici.
Domin hatta Salman dake gefenta shima yayi surrender.
Rayyern kuwa Sam bai Ankara ba saida ihun Jannart din ya shiga dodon kunnensa, wanda hakan yasa cikin sauri ya dago kansa.
Ganin yana gab da bi ta kansu ne, yasashi saurin.
Damƙe igiyar linzamin dokin da ƙarfi ya tsayar dashi cak.
Saboda ganin macen da yayi agabansa ne kuma ya sashi dirowa daga saman dokin.
Bayan ya juyashi.
Wani irin dogon tsaki yaja.
Tare da Kallon Salman wanda keta sauk’e ajiyar zuciya, kana ya watsawa Jannart din dake gabansa wani kallon da yasa cikinta ya murda ya haɗe da numfashin dake sauya salon fita da shiga.
Cikin tsuke fuska yace.
“Bakwa ganine, yanzu idan da nabi takanku fa?”
“Kayi hakuri dan Allah!” Salman ya fad’a asanyaye.
Itakuwa Jannart sai ayanzu ta bud’e idanunta, Yayinda gaba daya jikinta ke kakkarwa.
Hannu tasa ta dafe ƙirjinta.
Rayyern kuwa y’ar gajerar tsaki yaja, batare kuma daya sake ce musu komai ba ya juya ya nufi inda kayayyakinsa suke.