Sashe 61
Tubali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yayinda Ramadan da Riyyam kuwa suka dawo Cikin falon suka ci gaba da hirararsu, daga karshe ma game suka had’a, suka soma yi.
Ganin hakanne kuma yasa Abba da Mamy wucewa sashinsu.
Rayyern kuwa yana shiga dakinnasa kwanciya yayi, Cikin mintuna kad’an bacci yayi nasaran daukarsa.
Acan falon kasa kuwa Ramadan da Riyyam, duk kowannensu saman kujera ya d’ale ya kwanta, su kansu ba zasu iya sanin tayaya nema bacci ya kwashesu ba, kowannensu da abun buga game din ahannunsa, haka sukayi bacci kasancewar dare ya nisa.
A sashin Jannart kuwa yau tun 9 tayi baccinta mai cike da nutsuwa, Yayinda takejin zuciyarta wasai babu sauran wani fargaba.
Washegari.
Friday.
Tun tashinsa karfe 7 ya gama shirya kansa, saidai shigarsa ta yaudin ta banbanta dana kullum.
saboda wani riga da wando mai Taushin gaske ya saka ajikinsa, sabanin suit daya saba sakawa akowacce rana.
Sosai kayan Yayi masa kyau, musamman daya daura boyfriend jacket mai kyau akan kayan.
Wasu bakaken shoe masu tsada da watch ya daura a tsintsiyar hannunsa .
Bayan ya gama kimtsa kannasa ne kuma, ya dauki wayarsa tare da duba sakonnin da suke ta shigo masa ta Twitter, saboda yanda duniyat Twitter din ta Dinke da hotunansa, gaba daya shi kawai ake watsawa, da kuma bayani akan hirar da akayi dashi.
Kashe data dinnasa yayi, tare da juyawa ya nufi k’asa kaitsaye.
Anan cikin falon ya samu su Abba, harma da Riyyam nsra wanda yake ta hamma da alama bacci bai ishesa ba.
Dan Koda asuba ma Abba ne daya fito yagansu kwance afalo, shi ya tashesu tare da saka su agaba suka wuce masallaci.
Karasowa yayi ya zauna akan dining table din, bayan kuma Mom tayi saving dinsa ne, ya soma cin abincin atsanake, saidai kuma bai wani ci sosai ba, ya mik’e tsaye.
Yaudin ma dai atare suka fita shida Ramadan, saidai kuma Riyyam-nsra ya dage kan cewar, tare zasu tafi Hospital shida Ramadan.
Hakan kuwa akayi inda Ramadan din ya dauki Riyyam din suka wuce Hospital, shikuwa Rayyern dama yau ba Hospital din zaije kaitsaye ba.
Bayan anwangale musu gate din gidan sun fito da tsalatsalan motocinsu ne, kaitsaye su Riyyam suka wuce Hospital, shikuwa Company’n sa ya nufa.
Koda ya isa company din kuwa ya samu, ma aikata madasa in juna suna ta aikinsu, Domin yau din injunan da zasuna had’a kwalaye da buhuna ake kafawa amazauninsu.
Sosai ya jinjina kansa ganin yanda aikin nasu ke tafiya yanda ya kamata.
Kasancewar kuma akwai aikin da zaiyi ne yasa, kaitsaye ya haura sama inda Office d’insa yake.
Acan gida kuwa Baba Maud’o na zaune yaji karan horn din mota, atunaninsa ko su Rayyern dinne suka dawo, hakan yasa ya wangale gate din gidan.
Barrister Kabir kuwa dake cikin motar, kaitsaye ya shigo da motar tasa cikin gidan.
Bayan ya gama dai-dai-ta parking din motar tasa ne kuma, ya bud’e ya fito, saidai kuma ayau din bashi kad’ai yazo ba, atare dashi akwai Dr.Sajo.
Karasowa wajen Baba Maud’on sukayi tare da bashi hannu sukayi musabaha.
Baba Maud’o kuwa fuska asake ya amsa musu, sannan kuma da kansa yayi musu iso zuwa cikin gidan, har cikin babban falon kuma ya kaisu.
Ganinsu ne kuma yasa Abba fadada fara’arsa, tare da sawa Mamy tayi musu tarba maikyau.
Bayan sun gaggaisa ne kuma, Barrister Kabir ya gyara zama, tare da Kallon Abban ya gabatar masa da Dr. Sajo.
Haka dai suka Dan tattauna, agame da abunda suke shirin had’awa.
Bayan kuma sunyi tattaunawa mai tsawo ne, suka yanke shawara akan cewar yau Idan an sauk’o daga sallan Jumm’a za’a daura auren.
Da wannan batun sukayi sallama.
Inda Abban ya rakosu har waje, bayan sun tafi ne kuma ya zauna anan awajen Baba Maud’o suka d’an soma tattauna wasu batu.
Acan Office din Rayyern kuwa. Ganin 11:30 am ne yasa shi mik’ewa. Tare da barin duk wani abu da yakeyi.
Kaitsaye kasa ya sauko, saboda yanason sake komawa gida saboda yin shirin zuwa masallaci.
Koda ya shiga motar tasa kuwa cewa Hadi yayi su wuce gida.
Take kuwa kaitsaye suka nufo gida.
Koda ya dawo gidan, wanka ya sakeyi inda ya shirya kansa cikin riga da wando da kuma babbar riga, ta hadaddiyar getzner’n da ak’alla kudinta ya haura sama da 100k, sosai kayan sukayi masa kyau kasan cewar kalarsu lemon green ne kana zaren da aka watsawa garen su kuma shudi ne da fari da baƙi sosai sukayi mishi kyau, musamman daya kafa hulan zanna bukar blue color Kansa, ga kuma wani tsadadden takalmin toms suma blue da agogo daya saka, Tabbas yayi kyau kwarai.
Domin shigar tasa bawai gama gari bace, shigace ta musamman, wacce ta kara bayyana kyau da kwarjininsa.
Bayan ya gama kimtsawa ne kuma, ya feshe jikinsa da turare tare da sauk’owa k’asa, saboda jiyo hayaniyar Ramadan da kuma Riyyam da yayi, wanda suma sun shirya ne tsab, Cikin sabin getzners dinsu, masu kyau.
Kallonsu Riyyam din kawai yayi kana a takaice yace.
“Ka kwaso kayanka ka dawo nan, ka dena kwana a hotel”.
Ya ƙare mgnar cikin bada umarni.
Cikin yanayin ba zata jin mgnar Riyyam-nsra ya kalleshi da alamun zaiyi mgn sai kuma yayi shiru.
Ganin tuni ya fice batare kuma daya ƙara ce musu komai ba.
kaitsaye ya fice daga cikin falon.
cikin sauri-sauri kuma ya nufi motarsa saboda bayason rasa hud’uba.
Bayan ya fita daga gidanne kuma suma suka fito inda suka shiga motar Ramadan daketa murna da farin cikin mgnar Hamma Rayyern ɗin nasu.
kaitsaye masallacin Alfruq’an suma suka wuce.
Acan gidansu Jannart kuwa hakanan tun tashinta yau din takejin zuciyarta na yawan tsinkewa, ga kuma wani irin faduwar gaba da takeji akai akai.
Sai-dai rashin sanin takamaimai abun yi, yasa ta fara ambaton sunan Allah a cikin zuciyarta.
Barrister Kabir kuwa, bayan yayi shirin zuwa masallaci, yau din ko motarsa bai dauka ba, da kafansa ya fito inda ya tako har bakin titi, taxi ya tara, tare kuma da yiwa mai taxi din bayanin inda zai kaishi.
Wanda kuma bako Ina bane face masallacin dake gefen gidan Dr. Sajo.
Koda mai taxi din ya saukesa a masallacin, kaitsaye wajen Dr. Sajo ya nufa, atare sukayi sallan Jumma’a, bayan sun idar da sallan ne kuma, Dr. Sajo ya fito musu da mota.
Kaitsaye suka nufi unguwar Nassarawa GRA.
Yayinda acan masallacin alfurq’an kuwa, bayan an sallame sallan jumma’an, Ramadan da Riyyam-nsra suka sulale, kaitsaye basu zame ko inaba kuwa sai kasuwa, saboda kafun su fita Abban ya basu kudi yace su sayo masa huhun goro da kuma katton katton na mintuna.
Sudai haka suka je suka sayo batare da sanin na meye bane.
Koda suka dawo gida, anan cikin falon Abban suka jibge huhun goron da kuma mintunan da suka sayo.
Dawowarsu kuwa yayi dai-dai da isowan su Barrister Kabir da kuma Dr. Sajo.
Inda Abba da kansa yazo yayi musu iso zuwa babban falon k’asa.
Bayan sun zazzauna ne kuma ya fita ya kira Baba Maud’o, inda yace.
“Baba Maud’o ka shigo, yau abun na musamman za’ayi acikin gidannan, Insha Allah yanzu za’a daura auren Rayyern.”
Idanu Baba Maud’o ya d’an fitar, lokaci daya kuma yaji wani irin farinciki ya lullub’e sa, wanda hakan yasa Cikin matuk’ar jin dadi yace.
“Masha Allah lokaci yayi kenan, yau dai Ranar Rayyernu ta tsaya, To Allah yasa hakan shine mafi alkhairi.”
Da “Ameen.” Abba ya amsa.
Dai-dai lokacin kuma suka shigo cikin falon shida Baba Maud’o.
Acan waje kuwa yanzu motar Rayyern din ke isowa, Jin sunyi horn ba a bud’e musu bane kuma, yasa Hadi fitowa da kansa ya bud’e musu gate din suka shiga ciki.
Da mamaki Rayyern yake Kallon bakuwar motar dake fake afarfajiar gidan nasu, yayinda daga gefenta kuma motar Usman PA ne wanda yazo babu jimawa, kuma shima ya shigo yana can cikin falon Abban.
Ahankali ya bud’e murfin motar ya fito, Yana fitowa dinne kuma, Abba ma ya fito daga cikin falo, Kallon Rayyern din yayi, lokaci guda kuma ya hade fuskarsa, cikin tsare gida, ta yanda yasan Rayyern din bazai samu daman tambayarsa wani abuba yace.
“Hadi ka shigo daga ciki, kaima Rayyern ka biyoni.”
To Hadi yace tare da rufawa Abban baya, shima Rayyern din haka cikin daurewar Kai yabi bayan Abban nasa.
Suna shiga cikin falon kuwa, yaji zuciyarsa tayi wani irin harbawa, saboda yanda yaga mutane atare.
Daya bayan daya yake bin kowannesu da kallo, Koda ya sauke idanunsa akan Barrister Kabir, ji yayi wani irin abu ya tsarga mai.
“Oh My God meye kuma wannan mutumin ya sake zuwa yi agidan mu? Waishi bazai tab’a fahimta bane, nace masa ban shiryawa auren yartasa ba banasonta wai ko ana dole ne ai gaggawa dai bata da kyau.”
Yayi maganan azuciyarsa, tare da yin kicin kicin da fuskarsa.
Gudun kada yaji wata magana ta taso ne kuma yasa, cikin nitsuwa.
Ya ɗan motso ya gaidasu a mutunce.
Kana sauri-sauri ya soma kokarin haurawa sama.
“Rayyern zo zauna.”
Muryar Abba ta katse shi daga tafiyan da yakeyi, wanda kuma hakan yasa dolensa ya dawo cikin falon.
Zama yayi akusa da Abban nasa, tare da dago kansa ahankali yace.
“Abba Lafiya kuwa, meke faruwa?”
“Lafiya kalau sai alkhairi.”
Abban ya fad’a yana me d’an gyara zamansa, tare da fuskantar Baba Maud’o, cikin mutumtawa Hadi da karramawa yace.
“To Baba Maud’o kaine babba amatsayinka na babba kuma Kai ya kamata ka fada mana wanda zai zama waliyin Rayyern.”
Murmushi Baba Maud’o yayi, cikin muryar tausasawa yace.
“Kai ne zaka waliyancesa Alhaji, ai babu damuwa Dan uba ya waliyanci dansa.”
Baki Abban ya bud’e daniyar cewa wani abu, amma kuma saiya fasa saboda wani tunani daya fado cikin zuciyarsa.
Ajiyar zuciya yadan sauke tare da gyara zamansa yace .
“To shikenan ba matsala, wanene waliyin amarya?.”
“Gashi nan.”
Barrister Kabir ya fad’a yana mai nuna Dr Sajo, yana me fuskantar sauran mutanen dake cikin falon kuma da kyau.
Kai Abba yajinjina tare da juyawa ya kalli Rayyern.
Cikin yanayin dake nuna babu alaman wasa acikin magana ko fuskarsa yace.
“Rayyern kawo sadaki.”
Wani irin karya wuya Rayyern yayi, lokaci daya kuma ya narke fuska cike da tsananin mamaki yace.
“Sadaki kuma Abba? Sadakin menene, nifa...”
Ganin hakanne kuma yasa Abba da Mamy wucewa sashinsu.
Rayyern kuwa yana shiga dakinnasa kwanciya yayi, Cikin mintuna kad’an bacci yayi nasaran daukarsa.
Acan falon kasa kuwa Ramadan da Riyyam, duk kowannensu saman kujera ya d’ale ya kwanta, su kansu ba zasu iya sanin tayaya nema bacci ya kwashesu ba, kowannensu da abun buga game din ahannunsa, haka sukayi bacci kasancewar dare ya nisa.
A sashin Jannart kuwa yau tun 9 tayi baccinta mai cike da nutsuwa, Yayinda takejin zuciyarta wasai babu sauran wani fargaba.
Washegari.
Friday.
Tun tashinsa karfe 7 ya gama shirya kansa, saidai shigarsa ta yaudin ta banbanta dana kullum.
saboda wani riga da wando mai Taushin gaske ya saka ajikinsa, sabanin suit daya saba sakawa akowacce rana.
Sosai kayan Yayi masa kyau, musamman daya daura boyfriend jacket mai kyau akan kayan.
Wasu bakaken shoe masu tsada da watch ya daura a tsintsiyar hannunsa .
Bayan ya gama kimtsa kannasa ne kuma, ya dauki wayarsa tare da duba sakonnin da suke ta shigo masa ta Twitter, saboda yanda duniyat Twitter din ta Dinke da hotunansa, gaba daya shi kawai ake watsawa, da kuma bayani akan hirar da akayi dashi.
Kashe data dinnasa yayi, tare da juyawa ya nufi k’asa kaitsaye.
Anan cikin falon ya samu su Abba, harma da Riyyam nsra wanda yake ta hamma da alama bacci bai ishesa ba.
Dan Koda asuba ma Abba ne daya fito yagansu kwance afalo, shi ya tashesu tare da saka su agaba suka wuce masallaci.
Karasowa yayi ya zauna akan dining table din, bayan kuma Mom tayi saving dinsa ne, ya soma cin abincin atsanake, saidai kuma bai wani ci sosai ba, ya mik’e tsaye.
Yaudin ma dai atare suka fita shida Ramadan, saidai kuma Riyyam-nsra ya dage kan cewar, tare zasu tafi Hospital shida Ramadan.
Hakan kuwa akayi inda Ramadan din ya dauki Riyyam din suka wuce Hospital, shikuwa Rayyern dama yau ba Hospital din zaije kaitsaye ba.
Bayan anwangale musu gate din gidan sun fito da tsalatsalan motocinsu ne, kaitsaye su Riyyam suka wuce Hospital, shikuwa Company’n sa ya nufa.
Koda ya isa company din kuwa ya samu, ma aikata madasa in juna suna ta aikinsu, Domin yau din injunan da zasuna had’a kwalaye da buhuna ake kafawa amazauninsu.
Sosai ya jinjina kansa ganin yanda aikin nasu ke tafiya yanda ya kamata.
Kasancewar kuma akwai aikin da zaiyi ne yasa, kaitsaye ya haura sama inda Office d’insa yake.
Acan gida kuwa Baba Maud’o na zaune yaji karan horn din mota, atunaninsa ko su Rayyern dinne suka dawo, hakan yasa ya wangale gate din gidan.
Barrister Kabir kuwa dake cikin motar, kaitsaye ya shigo da motar tasa cikin gidan.
Bayan ya gama dai-dai-ta parking din motar tasa ne kuma, ya bud’e ya fito, saidai kuma ayau din bashi kad’ai yazo ba, atare dashi akwai Dr.Sajo.
Karasowa wajen Baba Maud’on sukayi tare da bashi hannu sukayi musabaha.
Baba Maud’o kuwa fuska asake ya amsa musu, sannan kuma da kansa yayi musu iso zuwa cikin gidan, har cikin babban falon kuma ya kaisu.
Ganinsu ne kuma yasa Abba fadada fara’arsa, tare da sawa Mamy tayi musu tarba maikyau.
Bayan sun gaggaisa ne kuma, Barrister Kabir ya gyara zama, tare da Kallon Abban ya gabatar masa da Dr. Sajo.
Haka dai suka Dan tattauna, agame da abunda suke shirin had’awa.
Bayan kuma sunyi tattaunawa mai tsawo ne, suka yanke shawara akan cewar yau Idan an sauk’o daga sallan Jumm’a za’a daura auren.
Da wannan batun sukayi sallama.
Inda Abban ya rakosu har waje, bayan sun tafi ne kuma ya zauna anan awajen Baba Maud’o suka d’an soma tattauna wasu batu.
Acan Office din Rayyern kuwa. Ganin 11:30 am ne yasa shi mik’ewa. Tare da barin duk wani abu da yakeyi.
Kaitsaye kasa ya sauko, saboda yanason sake komawa gida saboda yin shirin zuwa masallaci.
Koda ya shiga motar tasa kuwa cewa Hadi yayi su wuce gida.
Take kuwa kaitsaye suka nufo gida.
Koda ya dawo gidan, wanka ya sakeyi inda ya shirya kansa cikin riga da wando da kuma babbar riga, ta hadaddiyar getzner’n da ak’alla kudinta ya haura sama da 100k, sosai kayan sukayi masa kyau kasan cewar kalarsu lemon green ne kana zaren da aka watsawa garen su kuma shudi ne da fari da baƙi sosai sukayi mishi kyau, musamman daya kafa hulan zanna bukar blue color Kansa, ga kuma wani tsadadden takalmin toms suma blue da agogo daya saka, Tabbas yayi kyau kwarai.
Domin shigar tasa bawai gama gari bace, shigace ta musamman, wacce ta kara bayyana kyau da kwarjininsa.
Bayan ya gama kimtsawa ne kuma, ya feshe jikinsa da turare tare da sauk’owa k’asa, saboda jiyo hayaniyar Ramadan da kuma Riyyam da yayi, wanda suma sun shirya ne tsab, Cikin sabin getzners dinsu, masu kyau.
Kallonsu Riyyam din kawai yayi kana a takaice yace.
“Ka kwaso kayanka ka dawo nan, ka dena kwana a hotel”.
Ya ƙare mgnar cikin bada umarni.
Cikin yanayin ba zata jin mgnar Riyyam-nsra ya kalleshi da alamun zaiyi mgn sai kuma yayi shiru.
Ganin tuni ya fice batare kuma daya ƙara ce musu komai ba.
kaitsaye ya fice daga cikin falon.
cikin sauri-sauri kuma ya nufi motarsa saboda bayason rasa hud’uba.
Bayan ya fita daga gidanne kuma suma suka fito inda suka shiga motar Ramadan daketa murna da farin cikin mgnar Hamma Rayyern ɗin nasu.
kaitsaye masallacin Alfruq’an suma suka wuce.
Acan gidansu Jannart kuwa hakanan tun tashinta yau din takejin zuciyarta na yawan tsinkewa, ga kuma wani irin faduwar gaba da takeji akai akai.
Sai-dai rashin sanin takamaimai abun yi, yasa ta fara ambaton sunan Allah a cikin zuciyarta.
Barrister Kabir kuwa, bayan yayi shirin zuwa masallaci, yau din ko motarsa bai dauka ba, da kafansa ya fito inda ya tako har bakin titi, taxi ya tara, tare kuma da yiwa mai taxi din bayanin inda zai kaishi.
Wanda kuma bako Ina bane face masallacin dake gefen gidan Dr. Sajo.
Koda mai taxi din ya saukesa a masallacin, kaitsaye wajen Dr. Sajo ya nufa, atare sukayi sallan Jumma’a, bayan sun idar da sallan ne kuma, Dr. Sajo ya fito musu da mota.
Kaitsaye suka nufi unguwar Nassarawa GRA.
Yayinda acan masallacin alfurq’an kuwa, bayan an sallame sallan jumma’an, Ramadan da Riyyam-nsra suka sulale, kaitsaye basu zame ko inaba kuwa sai kasuwa, saboda kafun su fita Abban ya basu kudi yace su sayo masa huhun goro da kuma katton katton na mintuna.
Sudai haka suka je suka sayo batare da sanin na meye bane.
Koda suka dawo gida, anan cikin falon Abban suka jibge huhun goron da kuma mintunan da suka sayo.
Dawowarsu kuwa yayi dai-dai da isowan su Barrister Kabir da kuma Dr. Sajo.
Inda Abba da kansa yazo yayi musu iso zuwa babban falon k’asa.
Bayan sun zazzauna ne kuma ya fita ya kira Baba Maud’o, inda yace.
“Baba Maud’o ka shigo, yau abun na musamman za’ayi acikin gidannan, Insha Allah yanzu za’a daura auren Rayyern.”
Idanu Baba Maud’o ya d’an fitar, lokaci daya kuma yaji wani irin farinciki ya lullub’e sa, wanda hakan yasa Cikin matuk’ar jin dadi yace.
“Masha Allah lokaci yayi kenan, yau dai Ranar Rayyernu ta tsaya, To Allah yasa hakan shine mafi alkhairi.”
Da “Ameen.” Abba ya amsa.
Dai-dai lokacin kuma suka shigo cikin falon shida Baba Maud’o.
Acan waje kuwa yanzu motar Rayyern din ke isowa, Jin sunyi horn ba a bud’e musu bane kuma, yasa Hadi fitowa da kansa ya bud’e musu gate din suka shiga ciki.
Da mamaki Rayyern yake Kallon bakuwar motar dake fake afarfajiar gidan nasu, yayinda daga gefenta kuma motar Usman PA ne wanda yazo babu jimawa, kuma shima ya shigo yana can cikin falon Abban.
Ahankali ya bud’e murfin motar ya fito, Yana fitowa dinne kuma, Abba ma ya fito daga cikin falo, Kallon Rayyern din yayi, lokaci guda kuma ya hade fuskarsa, cikin tsare gida, ta yanda yasan Rayyern din bazai samu daman tambayarsa wani abuba yace.
“Hadi ka shigo daga ciki, kaima Rayyern ka biyoni.”
To Hadi yace tare da rufawa Abban baya, shima Rayyern din haka cikin daurewar Kai yabi bayan Abban nasa.
Suna shiga cikin falon kuwa, yaji zuciyarsa tayi wani irin harbawa, saboda yanda yaga mutane atare.
Daya bayan daya yake bin kowannesu da kallo, Koda ya sauke idanunsa akan Barrister Kabir, ji yayi wani irin abu ya tsarga mai.
“Oh My God meye kuma wannan mutumin ya sake zuwa yi agidan mu? Waishi bazai tab’a fahimta bane, nace masa ban shiryawa auren yartasa ba banasonta wai ko ana dole ne ai gaggawa dai bata da kyau.”
Yayi maganan azuciyarsa, tare da yin kicin kicin da fuskarsa.
Gudun kada yaji wata magana ta taso ne kuma yasa, cikin nitsuwa.
Ya ɗan motso ya gaidasu a mutunce.
Kana sauri-sauri ya soma kokarin haurawa sama.
“Rayyern zo zauna.”
Muryar Abba ta katse shi daga tafiyan da yakeyi, wanda kuma hakan yasa dolensa ya dawo cikin falon.
Zama yayi akusa da Abban nasa, tare da dago kansa ahankali yace.
“Abba Lafiya kuwa, meke faruwa?”
“Lafiya kalau sai alkhairi.”
Abban ya fad’a yana me d’an gyara zamansa, tare da fuskantar Baba Maud’o, cikin mutumtawa Hadi da karramawa yace.
“To Baba Maud’o kaine babba amatsayinka na babba kuma Kai ya kamata ka fada mana wanda zai zama waliyin Rayyern.”
Murmushi Baba Maud’o yayi, cikin muryar tausasawa yace.
“Kai ne zaka waliyancesa Alhaji, ai babu damuwa Dan uba ya waliyanci dansa.”
Baki Abban ya bud’e daniyar cewa wani abu, amma kuma saiya fasa saboda wani tunani daya fado cikin zuciyarsa.
Ajiyar zuciya yadan sauke tare da gyara zamansa yace .
“To shikenan ba matsala, wanene waliyin amarya?.”
“Gashi nan.”
Barrister Kabir ya fad’a yana mai nuna Dr Sajo, yana me fuskantar sauran mutanen dake cikin falon kuma da kyau.
Kai Abba yajinjina tare da juyawa ya kalli Rayyern.
Cikin yanayin dake nuna babu alaman wasa acikin magana ko fuskarsa yace.
“Rayyern kawo sadaki.”
Wani irin karya wuya Rayyern yayi, lokaci daya kuma ya narke fuska cike da tsananin mamaki yace.
“Sadaki kuma Abba? Sadakin menene, nifa...”