Sashe 72
Tubali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Still Rayyern din bacci yake.
Yayinda ya lullub’e duka jikinsa da blanket.
Karasa shigowa dakin Abba yayi,
Idanu ya ɗan zuwa fuskar Rayyern ɗin yana mai tuno wata kamanceceniya.
Numfashi ya ɗan fesar tare kuma da matsowa ya daura hannunsa dai-dai kan wuyan Rayyern din, Jin da yayi jikin Rayyern d’in babu alaman zafi ne, yasa shi soma kiran sunansa a nitse.
“Rayyern! Rayyern!! Rayyern!!!.”
Abban ya kira sunansa sau uku cikin kuma yanayin Dan daga murya.
Take kuma sauti da Amon muryar Abban ya ratsa kunnuwansa, wanda hakan ya sashi soma bud’e lumsasssun idanunsa ahankali, lokaci daya kuma jijiyoyin kansa suka amsa.
Saidai Ganin Abban nasa da yayi atsaye ne yasashi karasa bude idanunsa.
Abba kuwa gyara tsayuwarsa yayi, tare da cewa.
“Katashi daga wannan baccin da kakeyi kaje kaci abinci, sam baka karya ba, sannan kuma ka kawo kudi za’aje a iyawa matarka sayayya.”
Jin an ambaci mata ne kuma yasa shi shagwab’e fuska, tare da karyar da wuyansa gefe, cikin zallar yanayin shagwab’a yace.
“Abba kudi kuma, ni fa banida kudi.”
Tsareshi da ido Abban yayi, kana cikin tsare gida yace.
“Ka kawo kudi za’ayiwa matarka sayayya nace, ko kamanta cewar yanzu duk wani ci da sha da tufatarwar ta yana wuyanka ne?”
Bakinsa ya d’an tura gaba, kana cikin lumshe ido, ya mirgina gefe tare da saka hannunsa akan bedside drawer, ya d’auko Atm card d’insa, mikawa Abban atm card din yayi, still yana ta tura baki tamkar wani karamin yaro.
Abba kuwa karb’an atm card din yayi, batare daya sake cewa Rayyern din komai ba ya juya ya fice sabida yasan Ramadan yasan pin number sa.
Yana fita kuwa Rayyern ya sake langwab’ar da kansa, cikin wani irin takaicin yarinyar da aka tashesa daga baccin da yakeyi ta sanadiyarta, kwana daya kawai tak da tayi agidannasu, yau gashi har an fara takura rayuwarsa da shiga sabgar sa a kanta.
Abba kuwa Koda ya sauko kasa, atm card din ya bawa Mamy tare da cewa.
“Kisaya mata duk wani abu da kikasan zata buk’ata, maganan suturun sawa kuma ki saya mata isassu, komai da komai ahada a saya mata.”
“To Insha Allah, zan saya mata duk wani abu daya dace.”
Ramadan dake gefe ne kuma yace.
“Mamy nida Riyyam zamuyi miki rakiya, ko Riyyam.”
Ya ƙare mgnar yana kallon Riyyam-nsra.
Kai Riyyam ya jinjina cikin sauri, hade da cewa.
“Eh Mamy zamu rakaki, Ado Bayero Mall zamuje ko Jifatu, ko kuma Mudassir and Brothers?”
Murmushi Mamy tayi, tare da cewa.
“Shoprite dindai zamu fara zuwa, saboda nasan akwai komai da komai, Idan akazo b’angaren dogin riguna kuma, sai muje Jifatu, yanzu dai bari naje na shirya saina zo mutafi.”
“To.”
Suka amsa mata.
Ramadan kuma juyowa yayi ya kalli Riyyam-nsra tare da cewa.
“Wai ni kam yaushe kasan Kano haka!?.”
Kai ya shafa tare da cewa.
“Nida jihata ƙasata!”.
Kiran wayarshi da akayi ne yasa baibi ta kan furucin Riyyam-nsra ba.
Yayinda ita kuwa Mamy kaitsaye bedroom dinta ta wuce, bayan tayi wankane kuma ta shirya kanta acikin, wani tsadadden leshi, tare da yafa mayafinta cikin kamala ta fito.
Kaitsaye kuma d’akin Jannart din ta nufa.
Koda ta shiga falon, yanzun ma bata iske Jannart dinba shiyasa kaitsaye ta wuce cikin d’akin.
A dai-dai lokacin kuwa Jannart din, zaune take abakin gado, hannunta rike da wani dan littafi na turanci tana karantawa, wanda kuma yana daya daga cikin, yan abubuwan da ta taho dashi.
Ganin Mamy da tayi ne kuma, yasa tayi saurin sunkuyar da kanta k’asa, Mamy kuwa murmushi tayi, kana cikin kulawa tace.
“Jannart nida Ramadan da Riyyam zamuje kasuwa, sannan Abbanku ma zasu fita yanzu saboda naji dazu suna magana da Baba Maud’o akan cewar zasuje wani waje.”
Cikin girmama tace.
“Toh Mamy sai kun dawo Allah ya kiyaye hanya”.
Amin Mamy kana ta daura da cewa.
“Yanzu ki fad’amin me dame kikeso asayo miki Idan munje.”
Kai Jannart din ta dan sunkuyar k’asa, cikin sanyin murya, had’i da tsantsar ladabinta ga Mamyn tace.
“Mamy duk abunda kika sayamin yayi.”
Kai Mamyn ta jinjina cike da gamsuwa kuma tace.
“Masha Allah! To bari muje saimun dawo ko. Idan zaman dakin ya isheki, zaki iya fitowa falonki kisha iska, ko kallo kiyi nasan zai d’ebe miki kewa kafin mu dawo”.
“To Mamy, amman sai yaushe zaku dawo ne?”.
Jannart din ta tambaya, cikin tausasa murya.
Murmushi Mamyn tayi, again kuma itama cikin kulawa tace.
“Jannart kinsan yanayin kasuwa, Idan ka shigesa sai abunda Allah yayi, kana lisssafin zaka dawo da wurwuri, kuma sai kaga ba haka abun yake ba.”
Kai Jannart din ta jinjina, inda Mamy kuwa ta cigaba da cewa.
“Ni kaina bansan yaushe zamu dawo ba, saboda iya yanayin cikowan jama’a,n da muka samu, iya jimawan mu, amma dai Ina da yakinin bazamu wuce azahar ba.”
“Mamy har azahar.”
Jannart din ta tambaya fuska a karye.
“Eh mana Jannart, domin ya danganta da irin abubuwan da zamu saya, kuma kinga yanzu ma ana neman wajen karfe sha d’aya bamu tafiba.”
Kai Jannart din ta jinjina tare da gyara zamanta, tace.
“To Mamy saikun dawo Allah ya tsare.”
Da “Ameen.”
Mamyn ta amsa, harta juya zata fitane kuma idanunta suka Sauk’a, akan breakfast din da ta kawowa Jannart din, wanda ko tab’ashi batayi ba.
Kallonta Mamyn tayi, kana cikin kulawa tace.
“Jannart Meyasa baki ci abincin dana kawo miki ba?.”
Kai Jannart din ta dan sunkuyar kasa, kana murya asanyaye tace.
“Mamy banajin yunwa sosai ne, amma zanci zuwa anjima.”
“A’akam, banyarda da hakan ba, sam ban lamunci zama da yunwa ba sauk’o maza kici abinci kinji.”
Mamyn ta fad’a tana me kamo hannunta, ta zaunar da ita akan sofa, tare da matso mata kwanon abincin gabanta, cikin kulawa kuma tace.
“Kici abinci kinji, kada ki zauna da yunwa, domin yunwa tana illatar da lafiya, ko ke dinma irin Mijin naki ne, baku damu da abinci ba sai kayan kwalama.”
Shiru Jannart din tayi, kana Cikin matukar kunya, ta sadda kanta kasa, domin aduk sanda taji ance mijinta, wani irin abu ne takeji mai nauyi ya tsaya akan kirjinta to waye mijin? Ya yake? Me halinsa?.
Wadanan sune tambayoyin da takewa kanta tun jiya.
Mamy kuwa zuba mata abincin acikin plate tayi, tare da cewa.
“Idan kina buk’atar wani abu kafun mudawo, akwai kitchine anan cikin falon mu.
Taso ma muje na nuna miki.”
Mamyn ta fad’a tana me kamo, hannunta babu musu kuwa Jannart din ta mik’e, tare dabin bayan Mamyn suka fito, har cikin babban falon.
“Kinga wannan shine kitchine dinmu, wacccan kofan kuma anan part dina dana Abbansu Rayyern yake akwai kofar shiga da fita ta cikin falonmu wanda ba sai anbi ta nan ba.”
Mamyn ta fad’a tana meyi mata nuni da kitchine da kuma sashin su ita da Abba.
Kai Jannart din ta jinjina cike da gamsuwa.
“Can kuma dakunan k’asane irin Part ɗin dake sama ne. sai kuma sama inda anan bedroom na Rayyern, da kuma Ramadan suke, sai kuma extra part guda d’aya da yake can ta woje.
Sai nasu Baba Mauɗo, sai wanda kike ciki.
A can saman Mai gidanki yake.”
Mamyn ta k’are maganan tana meyi mata nuni da saman.
Jannart kuwa, kanta tad’an sadda k’asa, tare kuma da soma wasa da y’an yatsun hannunta, kana cikin sanyin murya tace.
“Mamy To meza’a girka yau d’in, kafun kudawo zan girka tunda dama ina zaune ne kawai babu abunda nakeyi.”
Murmushi Mamy tayi, tare da girgiza Kanta, kana cikin tsananin kulawa tace.
“A'a ki huta kinji Januart, bana son ki shiga kitchine daga yanzu.
Idan na dawo, zan girka abincin karki damu, ai bazamu wani jima sosai ba”
Dan juya kanta, tayi, saboda zuwan su Ramadan da kuma Riyyam kallonsu ta ɗanyi kana ta juyo ta kalli Mamy, atsanake cikin yanayin dake nuna biyayyarta tace.
“Da gaske Allah Mamy zanyi girkin, kinga zaku dawo a gajiye.”
Riyyam-nsra da yake karasowa wajennasu ne yayi saurin cab’e zancen da cewa.
“Please mana Mamy kibar My Aunty tayi mana girki yau, nasan abincinta dole zaiyi dadi.”
Jin muryar Riyyam-nsra dinne kuma yasa Jannart ɗin.
Dan dago da kanta, ta kallesu dai dai lokacinne kuma Ramadan ma
Ya karaso wajen.
Fuskarsa dauke da murmushi kuma yake Kallon matar Hamman nasa.
Cikin sakin fuska da kuma walwala yace.
“Good morning my beautiful Aunty, ya kwanan bak’unta.”
Murmushi ta ɗanyi kana ta ɗan kalleshi.
Tare da cewa tace.
“Morning.”
Riyyam ne yayi saurin matsowa kusa da ita, tare da danyin kasa da muryarsa, cikin kulawa yace.
“Aha My Aunty kin tunani ko?”.
cikin ɗan sakin fuska ta gyaɗa mishi kai, alamun ta tunoshi haduwarsu a airport,
Cikin yanayin rawan kansa yace.
“Aunty Jannart ni sunana Riyyam-nsra, tiktokers nasan kinsani ko?”.
Murmushi tayi tare da gyaɗa kai, ganin yadda ya tsareta da ido.
Kuma tabbas ta tunoshi haɗuwarsu a airport.
Shima murmushi yayi tare da cewa.
“Yauwa shi kuma wannan Hamma Ramadan sunansa, kuma yaya nane, akwai kuma babban yayanmu Hamma Rayyern.”
“Please kiyi mana abinci maidadi kinji, wanda zaisa kunnuwanmu su motsa.”
Ba iya Mamy da Ramadan ba harta ita saida ta saki murmushi mai hade da dan dariya.
Mamy kuwa Ganin lokaci na k’ure musu ne yasa, tace.
“Jannart rabu da shirmen Riyyam, koma daki kije kici abincinki.
Maganan girki kuma tunda kin dage sai kinyi, ki dafa mana abu mai sauki kawai.”
Kai Jannart din ta jinjina, sannan cikin zazzakar muryarta tace.
“Mamy ku dawo lafiya.”
Da “Ameen” duk sauka amsa, inda Mamy ta had’a kan Ramadan da Riyyam sukayi waje.
Itakuwa Jannart d’akinta ta koma, duk da cewar bata wani jin yunwa amma haka ta zauna ta d’an ci abincin, bayan ta kammala ne kuma ta d’aura da, lemon strawberry da Mamyn ta had’o mata dashi.
Gyatsa mai sanyi tayi tare da cewa.
“Alhamdulillah”.
Kana ta yunƙura
A nitse ta mik’e tsaye tare da d’aukan plates din da taci abincin ta fita dashi.
A hankali ta buɗe ƙofar falon nata.
Kana ta sako kanta.
Cikin Babban falon.
Numfashi ta dan fesar sabida wani irin masifeffen sanyin AC'n da suke busowa duka biyu.
A hankali take takowa har ta iso tsakiyar falon.
“Masha Allah, Mamy ba dai tsabta ba”.
Ta faɗi haka tana jujjuya kai tana kallon komai doke cikin falon.
Tsab-tsab sai ƙamshi da sanyi daya wadaci falon.
Yayinda ya lullub’e duka jikinsa da blanket.
Karasa shigowa dakin Abba yayi,
Idanu ya ɗan zuwa fuskar Rayyern ɗin yana mai tuno wata kamanceceniya.
Numfashi ya ɗan fesar tare kuma da matsowa ya daura hannunsa dai-dai kan wuyan Rayyern din, Jin da yayi jikin Rayyern d’in babu alaman zafi ne, yasa shi soma kiran sunansa a nitse.
“Rayyern! Rayyern!! Rayyern!!!.”
Abban ya kira sunansa sau uku cikin kuma yanayin Dan daga murya.
Take kuma sauti da Amon muryar Abban ya ratsa kunnuwansa, wanda hakan ya sashi soma bud’e lumsasssun idanunsa ahankali, lokaci daya kuma jijiyoyin kansa suka amsa.
Saidai Ganin Abban nasa da yayi atsaye ne yasashi karasa bude idanunsa.
Abba kuwa gyara tsayuwarsa yayi, tare da cewa.
“Katashi daga wannan baccin da kakeyi kaje kaci abinci, sam baka karya ba, sannan kuma ka kawo kudi za’aje a iyawa matarka sayayya.”
Jin an ambaci mata ne kuma yasa shi shagwab’e fuska, tare da karyar da wuyansa gefe, cikin zallar yanayin shagwab’a yace.
“Abba kudi kuma, ni fa banida kudi.”
Tsareshi da ido Abban yayi, kana cikin tsare gida yace.
“Ka kawo kudi za’ayiwa matarka sayayya nace, ko kamanta cewar yanzu duk wani ci da sha da tufatarwar ta yana wuyanka ne?”
Bakinsa ya d’an tura gaba, kana cikin lumshe ido, ya mirgina gefe tare da saka hannunsa akan bedside drawer, ya d’auko Atm card d’insa, mikawa Abban atm card din yayi, still yana ta tura baki tamkar wani karamin yaro.
Abba kuwa karb’an atm card din yayi, batare daya sake cewa Rayyern din komai ba ya juya ya fice sabida yasan Ramadan yasan pin number sa.
Yana fita kuwa Rayyern ya sake langwab’ar da kansa, cikin wani irin takaicin yarinyar da aka tashesa daga baccin da yakeyi ta sanadiyarta, kwana daya kawai tak da tayi agidannasu, yau gashi har an fara takura rayuwarsa da shiga sabgar sa a kanta.
Abba kuwa Koda ya sauko kasa, atm card din ya bawa Mamy tare da cewa.
“Kisaya mata duk wani abu da kikasan zata buk’ata, maganan suturun sawa kuma ki saya mata isassu, komai da komai ahada a saya mata.”
“To Insha Allah, zan saya mata duk wani abu daya dace.”
Ramadan dake gefe ne kuma yace.
“Mamy nida Riyyam zamuyi miki rakiya, ko Riyyam.”
Ya ƙare mgnar yana kallon Riyyam-nsra.
Kai Riyyam ya jinjina cikin sauri, hade da cewa.
“Eh Mamy zamu rakaki, Ado Bayero Mall zamuje ko Jifatu, ko kuma Mudassir and Brothers?”
Murmushi Mamy tayi, tare da cewa.
“Shoprite dindai zamu fara zuwa, saboda nasan akwai komai da komai, Idan akazo b’angaren dogin riguna kuma, sai muje Jifatu, yanzu dai bari naje na shirya saina zo mutafi.”
“To.”
Suka amsa mata.
Ramadan kuma juyowa yayi ya kalli Riyyam-nsra tare da cewa.
“Wai ni kam yaushe kasan Kano haka!?.”
Kai ya shafa tare da cewa.
“Nida jihata ƙasata!”.
Kiran wayarshi da akayi ne yasa baibi ta kan furucin Riyyam-nsra ba.
Yayinda ita kuwa Mamy kaitsaye bedroom dinta ta wuce, bayan tayi wankane kuma ta shirya kanta acikin, wani tsadadden leshi, tare da yafa mayafinta cikin kamala ta fito.
Kaitsaye kuma d’akin Jannart din ta nufa.
Koda ta shiga falon, yanzun ma bata iske Jannart dinba shiyasa kaitsaye ta wuce cikin d’akin.
A dai-dai lokacin kuwa Jannart din, zaune take abakin gado, hannunta rike da wani dan littafi na turanci tana karantawa, wanda kuma yana daya daga cikin, yan abubuwan da ta taho dashi.
Ganin Mamy da tayi ne kuma, yasa tayi saurin sunkuyar da kanta k’asa, Mamy kuwa murmushi tayi, kana cikin kulawa tace.
“Jannart nida Ramadan da Riyyam zamuje kasuwa, sannan Abbanku ma zasu fita yanzu saboda naji dazu suna magana da Baba Maud’o akan cewar zasuje wani waje.”
Cikin girmama tace.
“Toh Mamy sai kun dawo Allah ya kiyaye hanya”.
Amin Mamy kana ta daura da cewa.
“Yanzu ki fad’amin me dame kikeso asayo miki Idan munje.”
Kai Jannart din ta dan sunkuyar k’asa, cikin sanyin murya, had’i da tsantsar ladabinta ga Mamyn tace.
“Mamy duk abunda kika sayamin yayi.”
Kai Mamyn ta jinjina cike da gamsuwa kuma tace.
“Masha Allah! To bari muje saimun dawo ko. Idan zaman dakin ya isheki, zaki iya fitowa falonki kisha iska, ko kallo kiyi nasan zai d’ebe miki kewa kafin mu dawo”.
“To Mamy, amman sai yaushe zaku dawo ne?”.
Jannart din ta tambaya, cikin tausasa murya.
Murmushi Mamyn tayi, again kuma itama cikin kulawa tace.
“Jannart kinsan yanayin kasuwa, Idan ka shigesa sai abunda Allah yayi, kana lisssafin zaka dawo da wurwuri, kuma sai kaga ba haka abun yake ba.”
Kai Jannart din ta jinjina, inda Mamy kuwa ta cigaba da cewa.
“Ni kaina bansan yaushe zamu dawo ba, saboda iya yanayin cikowan jama’a,n da muka samu, iya jimawan mu, amma dai Ina da yakinin bazamu wuce azahar ba.”
“Mamy har azahar.”
Jannart din ta tambaya fuska a karye.
“Eh mana Jannart, domin ya danganta da irin abubuwan da zamu saya, kuma kinga yanzu ma ana neman wajen karfe sha d’aya bamu tafiba.”
Kai Jannart din ta jinjina tare da gyara zamanta, tace.
“To Mamy saikun dawo Allah ya tsare.”
Da “Ameen.”
Mamyn ta amsa, harta juya zata fitane kuma idanunta suka Sauk’a, akan breakfast din da ta kawowa Jannart din, wanda ko tab’ashi batayi ba.
Kallonta Mamyn tayi, kana cikin kulawa tace.
“Jannart Meyasa baki ci abincin dana kawo miki ba?.”
Kai Jannart din ta dan sunkuyar kasa, kana murya asanyaye tace.
“Mamy banajin yunwa sosai ne, amma zanci zuwa anjima.”
“A’akam, banyarda da hakan ba, sam ban lamunci zama da yunwa ba sauk’o maza kici abinci kinji.”
Mamyn ta fad’a tana me kamo hannunta, ta zaunar da ita akan sofa, tare da matso mata kwanon abincin gabanta, cikin kulawa kuma tace.
“Kici abinci kinji, kada ki zauna da yunwa, domin yunwa tana illatar da lafiya, ko ke dinma irin Mijin naki ne, baku damu da abinci ba sai kayan kwalama.”
Shiru Jannart din tayi, kana Cikin matukar kunya, ta sadda kanta kasa, domin aduk sanda taji ance mijinta, wani irin abu ne takeji mai nauyi ya tsaya akan kirjinta to waye mijin? Ya yake? Me halinsa?.
Wadanan sune tambayoyin da takewa kanta tun jiya.
Mamy kuwa zuba mata abincin acikin plate tayi, tare da cewa.
“Idan kina buk’atar wani abu kafun mudawo, akwai kitchine anan cikin falon mu.
Taso ma muje na nuna miki.”
Mamyn ta fad’a tana me kamo, hannunta babu musu kuwa Jannart din ta mik’e, tare dabin bayan Mamyn suka fito, har cikin babban falon.
“Kinga wannan shine kitchine dinmu, wacccan kofan kuma anan part dina dana Abbansu Rayyern yake akwai kofar shiga da fita ta cikin falonmu wanda ba sai anbi ta nan ba.”
Mamyn ta fad’a tana meyi mata nuni da kitchine da kuma sashin su ita da Abba.
Kai Jannart din ta jinjina cike da gamsuwa.
“Can kuma dakunan k’asane irin Part ɗin dake sama ne. sai kuma sama inda anan bedroom na Rayyern, da kuma Ramadan suke, sai kuma extra part guda d’aya da yake can ta woje.
Sai nasu Baba Mauɗo, sai wanda kike ciki.
A can saman Mai gidanki yake.”
Mamyn ta k’are maganan tana meyi mata nuni da saman.
Jannart kuwa, kanta tad’an sadda k’asa, tare kuma da soma wasa da y’an yatsun hannunta, kana cikin sanyin murya tace.
“Mamy To meza’a girka yau d’in, kafun kudawo zan girka tunda dama ina zaune ne kawai babu abunda nakeyi.”
Murmushi Mamy tayi, tare da girgiza Kanta, kana cikin tsananin kulawa tace.
“A'a ki huta kinji Januart, bana son ki shiga kitchine daga yanzu.
Idan na dawo, zan girka abincin karki damu, ai bazamu wani jima sosai ba”
Dan juya kanta, tayi, saboda zuwan su Ramadan da kuma Riyyam kallonsu ta ɗanyi kana ta juyo ta kalli Mamy, atsanake cikin yanayin dake nuna biyayyarta tace.
“Da gaske Allah Mamy zanyi girkin, kinga zaku dawo a gajiye.”
Riyyam-nsra da yake karasowa wajennasu ne yayi saurin cab’e zancen da cewa.
“Please mana Mamy kibar My Aunty tayi mana girki yau, nasan abincinta dole zaiyi dadi.”
Jin muryar Riyyam-nsra dinne kuma yasa Jannart ɗin.
Dan dago da kanta, ta kallesu dai dai lokacinne kuma Ramadan ma
Ya karaso wajen.
Fuskarsa dauke da murmushi kuma yake Kallon matar Hamman nasa.
Cikin sakin fuska da kuma walwala yace.
“Good morning my beautiful Aunty, ya kwanan bak’unta.”
Murmushi ta ɗanyi kana ta ɗan kalleshi.
Tare da cewa tace.
“Morning.”
Riyyam ne yayi saurin matsowa kusa da ita, tare da danyin kasa da muryarsa, cikin kulawa yace.
“Aha My Aunty kin tunani ko?”.
cikin ɗan sakin fuska ta gyaɗa mishi kai, alamun ta tunoshi haduwarsu a airport,
Cikin yanayin rawan kansa yace.
“Aunty Jannart ni sunana Riyyam-nsra, tiktokers nasan kinsani ko?”.
Murmushi tayi tare da gyaɗa kai, ganin yadda ya tsareta da ido.
Kuma tabbas ta tunoshi haɗuwarsu a airport.
Shima murmushi yayi tare da cewa.
“Yauwa shi kuma wannan Hamma Ramadan sunansa, kuma yaya nane, akwai kuma babban yayanmu Hamma Rayyern.”
“Please kiyi mana abinci maidadi kinji, wanda zaisa kunnuwanmu su motsa.”
Ba iya Mamy da Ramadan ba harta ita saida ta saki murmushi mai hade da dan dariya.
Mamy kuwa Ganin lokaci na k’ure musu ne yasa, tace.
“Jannart rabu da shirmen Riyyam, koma daki kije kici abincinki.
Maganan girki kuma tunda kin dage sai kinyi, ki dafa mana abu mai sauki kawai.”
Kai Jannart din ta jinjina, sannan cikin zazzakar muryarta tace.
“Mamy ku dawo lafiya.”
Da “Ameen” duk sauka amsa, inda Mamy ta had’a kan Ramadan da Riyyam sukayi waje.
Itakuwa Jannart d’akinta ta koma, duk da cewar bata wani jin yunwa amma haka ta zauna ta d’an ci abincin, bayan ta kammala ne kuma ta d’aura da, lemon strawberry da Mamyn ta had’o mata dashi.
Gyatsa mai sanyi tayi tare da cewa.
“Alhamdulillah”.
Kana ta yunƙura
A nitse ta mik’e tsaye tare da d’aukan plates din da taci abincin ta fita dashi.
A hankali ta buɗe ƙofar falon nata.
Kana ta sako kanta.
Cikin Babban falon.
Numfashi ta dan fesar sabida wani irin masifeffen sanyin AC'n da suke busowa duka biyu.
A hankali take takowa har ta iso tsakiyar falon.
“Masha Allah, Mamy ba dai tsabta ba”.
Ta faɗi haka tana jujjuya kai tana kallon komai doke cikin falon.
Tsab-tsab sai ƙamshi da sanyi daya wadaci falon.