Sashe 55
Tubali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Abba ya maganan aikina kuma Idan har abunda kake shiryawan ya tabbata, hakura zanyi da aikin nawa kenan?”
Kai Abba Kabir din ya girgiza mata, cikin tausasawa kuma yace.
“Karki damu Jannart, komai zai tafi dai-dai, Domin zanje na samu MD’n ku, duk wani abu daya dace nayi zanyi, tayanda aikinki bazai bar hannunki ba, koda kuwa bakyanan, kada kiji komai aranki Jannart, Insha Allah sauyi ne yake zuwawa rayuwarki.”
Ajiyar zuciya ta sauke saboda sai yanzu ne taji sanyi acikin zuciyarta.
Yayinda Abban kuwa abincin ya soma ci, tun aloman farko kuwa ya soma yin santi.
Tas kuwa ya cinye abincin, bayan ya kammala ne kuma ya yi musu sallaama ya tafi
Yana fita kai tsaye Mai-nasara Hospital ya nufa...
Jannart kuwa bayan ta kammala komai, jere musu abincin tayi akan dining table.
Koda sukayi breakfast din kuma daki ta koma ta kwanta, zuciyarta cike da sake sake kala kala, musamman yau din takejin bugun zuciya da faduwar gaba.
Saboda tsoro da takeyi na kada yamma tayi kuma mutumin da sukayi dashi akan zai kawo musu Dr. Rayyern Mai-nasara yaki zuwa.
Haka dai ta wuni cikin fargaba.
A hankali ya ɗago kanshi ya kalli ƙofar shigowa Office din nasa.
Wanda ake neman izinin shiga.
Idonshi ya ɗan lumshe tare da bada izinin shigowa.
Dr Sulaiman a gaba sai Barrister Kabir dake bayansa da alama jagora yayi masa.
Da sauri ya ida buɗe idansa.
Tare da gyara zamanshi.
Ido ya zuwa Dr Sulaiman dake nuna Barrister Kabir kujerar zama tare da ce mishi.
“Bismillah Barrister ga wurin zama.
Gaka ga Dr Rayyern Mai-nasara, ni bari in koma bakin aiki”.
Cikin jin daɗi Barrister Kabir ya zauna tare da cewa.
“Docta ngd matuƙa”.
Shi kuwa Dr Rayyern Mai-nasara wani irin kallon tuhuma yakeyiwa Dr Sulaiman shi kuwa Sulaiman murmushi yayi tare da cewa.
“Toh na tafi”.
Ya ƙare mgnar yana fita.
Wani nannauyan numfashin ya fesar kana a hankali ya kalli Barrister Kabir dake zaune cikin kamala da mutuntaka.
Cikin nitsuwa yace.
"Barka da zuwa”.
“Barka dai Rayyern, ya gida yasu Abbanka?”.
Barrister Kabir yayi mgnar cikin kulawa da mutuntakar da tasa jikin Rayyern yin sanyi, cikin girmamawa yace.
“Alhamdulillah. Ya mai jiki?”.
Ya ida mgnar a matuƙar gajarce.
Wanda mgnar kamar subutar bakine.
Cike da jin daɗin yace.
“Alhamdullih jiki da sauƙi”.
Uhum yace tare da gyara zamanshi.
Shima Abba gyara zamanshi yayi cikin nitsuwa yace.
“Yanzuma mgnar tane ya kawoni gareka in ba matsala dan Allah da Manzonsa mu tattauna!”.
Ya ƙare mgnar yana zubawa Dr Rayyern Mai-nasara idanu.
Shi kuwa Rayyern a hankali ya meda bayanshi ya jingine da jikin kujerar tasa.
Wani sassanyan numfashi ya fesar.
Tabbas Barrister yana karya mishi duk wani logonshi da yake haɗashi da Allah da Manzonsa.
Cikin yin ƙasa da murya yace.
“Bismillah”.
Jin hakane yasa Abba gyara zamanshi da kyau fuska cike da tsantsar gsky ya fara mgn a sanyaye.
Yayinda shi kuwa Dr Rayyern ya tsareshi da idanu dan son gano gskyr zuciyarsa.
A nitse ya fara mgn.
“Kayi haƙuri Dr Rayyern Mai-nasara, nasan dole kaga batun da nazo muku dashi a matsayin tatsuniya ko shirme.
Ko kuma zance mara dalili.”
Numfashi ya dan ja sai ga wasu irin hawaye masu zafi suka kwaranyo mishi wanda sukayi masifar karya zuciyar Dr Rayyern Mai-nasara da take mai tausayi.
Cikin raunin murya yaci gaba da cewa.
“Jannart yarinya ce mai rauni, da son taimako da samun tsayayyen jigon da zai zame mata GARKUWA'N da zai iya killaceta, sabida akwai masu bibiyar rayuwarta suna son kasheta!!!.”
Sosai Dr Rayyern ya rumtse idanunshi sabida hawayen mutumin na karya mishi zuciya.
A raunace yaci gaba da cewa.
“Haka yasa nake neman inda zan sata ta tsira da rayuwarta, ID card ɗinshi ya miƙa mishi tare da cewa.
“Ka gani ni Lawyer ne mai kare haƙin ɗan adam bisa umarnin kotu nake neman inda zan adanata ba wai haka nan gaba gad’i nakeyi ba.
Rayyern Jannart macece da takeda cikar sura, ba rashin mijin nema bane yasa na baka ita sai dai bisa dalilin gamayyar TUBALIn matsalar.
Please ka amince da auren Jannart bisa Kekkyawar niya, ita marainiyace, mahaifiyarta ta barmin amanarta da wasiyyar in aura mata miji na gari da zai riƙeta da amana”.
Wani irin taune lips ɗinshi yayi duka biyu.
Tare da jin wani irin masifeffen tausayi rauni da kuma shiga rud’un kalaman Barrister.
Cikin murya mai cike da kamala da yanayinsa na rashin iya ƙarya yace.
“Bana sonta batayi min ba ko kaɗan, sam bafa na sonta cikin raina. Koda dai-dai da kwayar zarra a haka zamuyi zaman auren?”.
Da sauri Barrister Kabir yace.
“Zaka sota Rayyern in ka zauna da Jannart zaka sota.
Sabida ita macece mai biyayya da amsar umarni tanada haƙuri”.
Da sauri ya girgiza kansa tare da cewa.
“Bazan sotaba wlh bazan sotaba har gaban abadan sabida in na tsani abu bani dawowa in soshi daga baya”.
Cikin tsananta hawaye Barrister Kabir ya mai-maita kalmar tsana a ransa.
A fili kuwa cewa yayi.
"Ya ilahi ya mujibadda'awati, ya Allah ka kawo min mafita, Allah ka gani ina son kare rai da lfy da martabar Jannart bani da nufin haɗata da wanda ya tsaneta”.
Sai kuma ga sabbin hawaye.
Hannunshi yasa ya kamo hannun Dr Rayyern cikin sanyi yace.
“Toh amman zaka iya riƙe min amanar kula da tsaronta da lfyarta da cinta da shanta bisa ƙarƙashin inuwar auren na wani ɗan lokacin da gsky zatayi halinta sai ka sakar min ita in bata mai sonta? Dan Allah da Manzonsa kamin wannan alfmafar”.
Wani irin nannauyan numfashin ya fesar jin yadda murmuyar Abba ke rawan kuka
Cikin rauni da tausayin mutumin yace.
“Har zuwa wannne lokacin kenan?”.
Da sauri Barrister Kabir yace.
“Wata takwas zuwa shekara ɗaya dan Allah”.
Cikin sanyi yace.
“Ba komai na amince zan kula da ita dai-dai iyawa ta.
Abba na yayi saurin aminta da kai, ya kuma nuna min dole in auri ɗiyarka, bayan kuma Bani da isasshen lokacin.
Toh zamuyi yarjejeniyar shekara ɗaya tana cika kacewa Abba in sakar maka ƴarka sabida bani da isasshen lokacin kainama bare na kula da ƴarka.
Kaga daga nan in na saketa Abba bazai sake min mgnar aureba tunda yaga rashin lokacin ya shafi auren”.
Cikin wani irin kallo Barrister Kabir yace.
“Zan amince da haka sai dai cikin yarjejeniyar tamu, ya zama Jannart ta tsira da budurcibta kada ka meda min ƴaƴan ƙaramar bazawara tunda har kasan baka sonta, ka tabbatar ta dawo hannuna a budurwa”.
Fuskarshi ya ɗan yamutsa tare da tura baki kana yace.
“Nayima al'ƙari, ni kuma mema haɗina da ita nifa RAYYERN babu mace a idanuna”.
Da sauri ya kalli Barrister Kabir da yace.
“Kada ka manta wannan tattaunawar tamu fa”.
Cikin yarda da kai yace.
“Ban cika mantuwa ba, kuma in nayi al'ƙawari nakan yi iya iyawa ta inga na cikashi”.
Cikin jan numfashi Barrister Kabir ya miƙa tare da cewa.
“Ngd matuka ni dai fatana. Ci da sha jinya muhalli nitsuwa nake buƙatar Jannart ta samu masu sata farin ciki”.
Hannu ya bashi ganin yana miƙa mishi hannu busaha sukayi kana yace.
“Uhum”.
Daga nan Barrister Kabir ya sallameshi ya tafi.
Shi kuwa Dr Rayyern Mai-nasara gyara zamanshi yayi yana mai cewa.
“Wai kada in taɓa masa ƴa jifa, sai kace ance masa ni irin jarabbun nanne marasa haƙuri da rashin iya sarrafa kai, ko zato yake ni mayen matane!?”
Chocolate ɗin dake gefenshi ya ɓare ya afa a baki.
Ya tauna ido ya lumshe tare da cewa.
“Ni ko kalloma wannan uwar ƙwaƙƙwazon ta isheni nema, me ma zai kaini kusa da ita tunda nafi kowa sanin karo da ita ba dama kamar anyi karo da doki.
Tana ƙasa ina sama”.
Ya ida mgnar yana shan Chocolate ɗinsa da yasa yaketa lumshe ido.
Shi kuwa Abba daga Mai-nasara Hospital kai tsaye gidansu Dr Rayyern ɗin yaje.
Suka tattauna da Abba kana ya koma gida bayan ya biya wurin Dr Sajo ma.
Ita kuwa Jannart 4:00 pm dai dai ta fito daga wanka, bayan ta gama tsane ruwan dake jikinta ne kuma, ta shafawa lallausan fatar jikinta body lotion, tare da fesawa kowani lungu dake jikinta turare mai dadin kamshi.
Kamar kullum kuma bata wani yi kwalliya akan fuskarta ba, powder ce kawai sai lipstick da kuma mascara da ta shafa.
Amma duk da hakan kuwa tayi kyau sosai.
Musamman kajol din da tasa sun kara bayyana hasken idanunta.
Wata had’add’iyar Turkish Abaya mai kalan Dark greeen ta ciro daga cikin drawer’nta, abayace mai tsananin kyaun gaske, da kuma tsada Domin kuwa ko adon duwatsun da aka kawata jikinsa dashi abun kallone.
Kimtsa cikin jikinta tayi, Domin kuwa yaudin harda bra ta saka domin sosai takejin nauyin da ƙirjinta keyi ya ragun mata tunda ta fara shan magungunan da aka bata a Mai-nasara Hospital, bayan ta kammala ne kuma ta Zura doguwar rigar ajikinta, tare da daukan mayafin rigar, bayan tayi parking dogon gashin kanta ne, kuma ta yafa vail din abayan, wanda ya rufe mata kai zuwa wuyanta.
Bayan ta saka wani dankunnen gold mai kalan dark green akunnenta ne kuma,
Anutse ta zura wani had’add’en hill shoe mai kalan dark green ak’afarta.
Yah Allah bak’aramin kyau Jannart din tayi yau ba, musamman yanda doguwar rigar yabi hadaddiyar Surar jikinta ya kwanta.
Koda ta kalli kanta amadubi murmushi tayi, Domin ita kanta tasan cewa rigar tayi masifar mata kyau sosai, musamman da dark green color din ya bayyana hasken fatarta.
Bayan ta sake shafa parfumed ajikinta ne kuma, ta d’auki Waya hadi da dan maidaidaicin dark green handbag dinta, wanda adon duwatsun jikinsa ke shige da na jikin rigarta.
Kyau iya kyau kam tasha shi.
Koda ta fito daga cikin dakinnata kuwa, haka take takawa Ahankali harta sauko kasa inda Momy ke zaune.
Idanu Momyn ta zuba mata, tare da bud’e baki tace.
“Masha Allah Kai gaskiya Jannart kinyi kyau kinganki kuwa saikace irin matan Egypt dinnan.”
Murmushin Jin dadi Jannart din tayi, tare kuma da yiwa Momyn godiya.
Kana cikin dan hanzari tace.
“Momy natafi saina dawo.”
Adawo lafiya Momyn tayi mata, Yayinda ita kuma kaitsaye ta fice daga cikin falon.
Koda ta fito compound din gidan, ta samu Baba Ado da guards dinta na jiranta.
Ad’an k’agauce haka ta shiga cikin mota suka bar gidan.
Kai Abba Kabir din ya girgiza mata, cikin tausasawa kuma yace.
“Karki damu Jannart, komai zai tafi dai-dai, Domin zanje na samu MD’n ku, duk wani abu daya dace nayi zanyi, tayanda aikinki bazai bar hannunki ba, koda kuwa bakyanan, kada kiji komai aranki Jannart, Insha Allah sauyi ne yake zuwawa rayuwarki.”
Ajiyar zuciya ta sauke saboda sai yanzu ne taji sanyi acikin zuciyarta.
Yayinda Abban kuwa abincin ya soma ci, tun aloman farko kuwa ya soma yin santi.
Tas kuwa ya cinye abincin, bayan ya kammala ne kuma ya yi musu sallaama ya tafi
Yana fita kai tsaye Mai-nasara Hospital ya nufa...
Jannart kuwa bayan ta kammala komai, jere musu abincin tayi akan dining table.
Koda sukayi breakfast din kuma daki ta koma ta kwanta, zuciyarta cike da sake sake kala kala, musamman yau din takejin bugun zuciya da faduwar gaba.
Saboda tsoro da takeyi na kada yamma tayi kuma mutumin da sukayi dashi akan zai kawo musu Dr. Rayyern Mai-nasara yaki zuwa.
Haka dai ta wuni cikin fargaba.
A hankali ya ɗago kanshi ya kalli ƙofar shigowa Office din nasa.
Wanda ake neman izinin shiga.
Idonshi ya ɗan lumshe tare da bada izinin shigowa.
Dr Sulaiman a gaba sai Barrister Kabir dake bayansa da alama jagora yayi masa.
Da sauri ya ida buɗe idansa.
Tare da gyara zamanshi.
Ido ya zuwa Dr Sulaiman dake nuna Barrister Kabir kujerar zama tare da ce mishi.
“Bismillah Barrister ga wurin zama.
Gaka ga Dr Rayyern Mai-nasara, ni bari in koma bakin aiki”.
Cikin jin daɗi Barrister Kabir ya zauna tare da cewa.
“Docta ngd matuƙa”.
Shi kuwa Dr Rayyern Mai-nasara wani irin kallon tuhuma yakeyiwa Dr Sulaiman shi kuwa Sulaiman murmushi yayi tare da cewa.
“Toh na tafi”.
Ya ƙare mgnar yana fita.
Wani nannauyan numfashin ya fesar kana a hankali ya kalli Barrister Kabir dake zaune cikin kamala da mutuntaka.
Cikin nitsuwa yace.
"Barka da zuwa”.
“Barka dai Rayyern, ya gida yasu Abbanka?”.
Barrister Kabir yayi mgnar cikin kulawa da mutuntakar da tasa jikin Rayyern yin sanyi, cikin girmamawa yace.
“Alhamdulillah. Ya mai jiki?”.
Ya ida mgnar a matuƙar gajarce.
Wanda mgnar kamar subutar bakine.
Cike da jin daɗin yace.
“Alhamdullih jiki da sauƙi”.
Uhum yace tare da gyara zamanshi.
Shima Abba gyara zamanshi yayi cikin nitsuwa yace.
“Yanzuma mgnar tane ya kawoni gareka in ba matsala dan Allah da Manzonsa mu tattauna!”.
Ya ƙare mgnar yana zubawa Dr Rayyern Mai-nasara idanu.
Shi kuwa Rayyern a hankali ya meda bayanshi ya jingine da jikin kujerar tasa.
Wani sassanyan numfashi ya fesar.
Tabbas Barrister yana karya mishi duk wani logonshi da yake haɗashi da Allah da Manzonsa.
Cikin yin ƙasa da murya yace.
“Bismillah”.
Jin hakane yasa Abba gyara zamanshi da kyau fuska cike da tsantsar gsky ya fara mgn a sanyaye.
Yayinda shi kuwa Dr Rayyern ya tsareshi da idanu dan son gano gskyr zuciyarsa.
A nitse ya fara mgn.
“Kayi haƙuri Dr Rayyern Mai-nasara, nasan dole kaga batun da nazo muku dashi a matsayin tatsuniya ko shirme.
Ko kuma zance mara dalili.”
Numfashi ya dan ja sai ga wasu irin hawaye masu zafi suka kwaranyo mishi wanda sukayi masifar karya zuciyar Dr Rayyern Mai-nasara da take mai tausayi.
Cikin raunin murya yaci gaba da cewa.
“Jannart yarinya ce mai rauni, da son taimako da samun tsayayyen jigon da zai zame mata GARKUWA'N da zai iya killaceta, sabida akwai masu bibiyar rayuwarta suna son kasheta!!!.”
Sosai Dr Rayyern ya rumtse idanunshi sabida hawayen mutumin na karya mishi zuciya.
A raunace yaci gaba da cewa.
“Haka yasa nake neman inda zan sata ta tsira da rayuwarta, ID card ɗinshi ya miƙa mishi tare da cewa.
“Ka gani ni Lawyer ne mai kare haƙin ɗan adam bisa umarnin kotu nake neman inda zan adanata ba wai haka nan gaba gad’i nakeyi ba.
Rayyern Jannart macece da takeda cikar sura, ba rashin mijin nema bane yasa na baka ita sai dai bisa dalilin gamayyar TUBALIn matsalar.
Please ka amince da auren Jannart bisa Kekkyawar niya, ita marainiyace, mahaifiyarta ta barmin amanarta da wasiyyar in aura mata miji na gari da zai riƙeta da amana”.
Wani irin taune lips ɗinshi yayi duka biyu.
Tare da jin wani irin masifeffen tausayi rauni da kuma shiga rud’un kalaman Barrister.
Cikin murya mai cike da kamala da yanayinsa na rashin iya ƙarya yace.
“Bana sonta batayi min ba ko kaɗan, sam bafa na sonta cikin raina. Koda dai-dai da kwayar zarra a haka zamuyi zaman auren?”.
Da sauri Barrister Kabir yace.
“Zaka sota Rayyern in ka zauna da Jannart zaka sota.
Sabida ita macece mai biyayya da amsar umarni tanada haƙuri”.
Da sauri ya girgiza kansa tare da cewa.
“Bazan sotaba wlh bazan sotaba har gaban abadan sabida in na tsani abu bani dawowa in soshi daga baya”.
Cikin tsananta hawaye Barrister Kabir ya mai-maita kalmar tsana a ransa.
A fili kuwa cewa yayi.
"Ya ilahi ya mujibadda'awati, ya Allah ka kawo min mafita, Allah ka gani ina son kare rai da lfy da martabar Jannart bani da nufin haɗata da wanda ya tsaneta”.
Sai kuma ga sabbin hawaye.
Hannunshi yasa ya kamo hannun Dr Rayyern cikin sanyi yace.
“Toh amman zaka iya riƙe min amanar kula da tsaronta da lfyarta da cinta da shanta bisa ƙarƙashin inuwar auren na wani ɗan lokacin da gsky zatayi halinta sai ka sakar min ita in bata mai sonta? Dan Allah da Manzonsa kamin wannan alfmafar”.
Wani irin nannauyan numfashin ya fesar jin yadda murmuyar Abba ke rawan kuka
Cikin rauni da tausayin mutumin yace.
“Har zuwa wannne lokacin kenan?”.
Da sauri Barrister Kabir yace.
“Wata takwas zuwa shekara ɗaya dan Allah”.
Cikin sanyi yace.
“Ba komai na amince zan kula da ita dai-dai iyawa ta.
Abba na yayi saurin aminta da kai, ya kuma nuna min dole in auri ɗiyarka, bayan kuma Bani da isasshen lokacin.
Toh zamuyi yarjejeniyar shekara ɗaya tana cika kacewa Abba in sakar maka ƴarka sabida bani da isasshen lokacin kainama bare na kula da ƴarka.
Kaga daga nan in na saketa Abba bazai sake min mgnar aureba tunda yaga rashin lokacin ya shafi auren”.
Cikin wani irin kallo Barrister Kabir yace.
“Zan amince da haka sai dai cikin yarjejeniyar tamu, ya zama Jannart ta tsira da budurcibta kada ka meda min ƴaƴan ƙaramar bazawara tunda har kasan baka sonta, ka tabbatar ta dawo hannuna a budurwa”.
Fuskarshi ya ɗan yamutsa tare da tura baki kana yace.
“Nayima al'ƙari, ni kuma mema haɗina da ita nifa RAYYERN babu mace a idanuna”.
Da sauri ya kalli Barrister Kabir da yace.
“Kada ka manta wannan tattaunawar tamu fa”.
Cikin yarda da kai yace.
“Ban cika mantuwa ba, kuma in nayi al'ƙawari nakan yi iya iyawa ta inga na cikashi”.
Cikin jan numfashi Barrister Kabir ya miƙa tare da cewa.
“Ngd matuka ni dai fatana. Ci da sha jinya muhalli nitsuwa nake buƙatar Jannart ta samu masu sata farin ciki”.
Hannu ya bashi ganin yana miƙa mishi hannu busaha sukayi kana yace.
“Uhum”.
Daga nan Barrister Kabir ya sallameshi ya tafi.
Shi kuwa Dr Rayyern Mai-nasara gyara zamanshi yayi yana mai cewa.
“Wai kada in taɓa masa ƴa jifa, sai kace ance masa ni irin jarabbun nanne marasa haƙuri da rashin iya sarrafa kai, ko zato yake ni mayen matane!?”
Chocolate ɗin dake gefenshi ya ɓare ya afa a baki.
Ya tauna ido ya lumshe tare da cewa.
“Ni ko kalloma wannan uwar ƙwaƙƙwazon ta isheni nema, me ma zai kaini kusa da ita tunda nafi kowa sanin karo da ita ba dama kamar anyi karo da doki.
Tana ƙasa ina sama”.
Ya ida mgnar yana shan Chocolate ɗinsa da yasa yaketa lumshe ido.
Shi kuwa Abba daga Mai-nasara Hospital kai tsaye gidansu Dr Rayyern ɗin yaje.
Suka tattauna da Abba kana ya koma gida bayan ya biya wurin Dr Sajo ma.
Ita kuwa Jannart 4:00 pm dai dai ta fito daga wanka, bayan ta gama tsane ruwan dake jikinta ne kuma, ta shafawa lallausan fatar jikinta body lotion, tare da fesawa kowani lungu dake jikinta turare mai dadin kamshi.
Kamar kullum kuma bata wani yi kwalliya akan fuskarta ba, powder ce kawai sai lipstick da kuma mascara da ta shafa.
Amma duk da hakan kuwa tayi kyau sosai.
Musamman kajol din da tasa sun kara bayyana hasken idanunta.
Wata had’add’iyar Turkish Abaya mai kalan Dark greeen ta ciro daga cikin drawer’nta, abayace mai tsananin kyaun gaske, da kuma tsada Domin kuwa ko adon duwatsun da aka kawata jikinsa dashi abun kallone.
Kimtsa cikin jikinta tayi, Domin kuwa yaudin harda bra ta saka domin sosai takejin nauyin da ƙirjinta keyi ya ragun mata tunda ta fara shan magungunan da aka bata a Mai-nasara Hospital, bayan ta kammala ne kuma ta Zura doguwar rigar ajikinta, tare da daukan mayafin rigar, bayan tayi parking dogon gashin kanta ne, kuma ta yafa vail din abayan, wanda ya rufe mata kai zuwa wuyanta.
Bayan ta saka wani dankunnen gold mai kalan dark green akunnenta ne kuma,
Anutse ta zura wani had’add’en hill shoe mai kalan dark green ak’afarta.
Yah Allah bak’aramin kyau Jannart din tayi yau ba, musamman yanda doguwar rigar yabi hadaddiyar Surar jikinta ya kwanta.
Koda ta kalli kanta amadubi murmushi tayi, Domin ita kanta tasan cewa rigar tayi masifar mata kyau sosai, musamman da dark green color din ya bayyana hasken fatarta.
Bayan ta sake shafa parfumed ajikinta ne kuma, ta d’auki Waya hadi da dan maidaidaicin dark green handbag dinta, wanda adon duwatsun jikinsa ke shige da na jikin rigarta.
Kyau iya kyau kam tasha shi.
Koda ta fito daga cikin dakinnata kuwa, haka take takawa Ahankali harta sauko kasa inda Momy ke zaune.
Idanu Momyn ta zuba mata, tare da bud’e baki tace.
“Masha Allah Kai gaskiya Jannart kinyi kyau kinganki kuwa saikace irin matan Egypt dinnan.”
Murmushin Jin dadi Jannart din tayi, tare kuma da yiwa Momyn godiya.
Kana cikin dan hanzari tace.
“Momy natafi saina dawo.”
Adawo lafiya Momyn tayi mata, Yayinda ita kuma kaitsaye ta fice daga cikin falon.
Koda ta fito compound din gidan, ta samu Baba Ado da guards dinta na jiranta.
Ad’an k’agauce haka ta shiga cikin mota suka bar gidan.