Sashe 60
Tubali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Assalamu Alaikum.”
Dr Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara din ya fad’a atausashe, saboda yasan izuwa yanzu duk su Abbansa suna kallonsa.
Jannart kuwa juyowa tayi ta fuskanci Camera hadi da cewa.
“To masu kallonmu duka duka anan muka kawo k’arshen shirin namu, tare da babban bak’onmu”.
Ta ƙare mgnar da juyowa tana kallon Dr Rayyern.
Numfashi ya ɗan fesar tare da cewa.
“Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara”.
Gyara zamanta tayi tare da cewa.
“Sai kuma ni dana shirya na kuma gabatar JANNART IDI SALE DAKATA. Nake, mana fatan mu hade awani sati Idan Allah ya kaimu a huta gajiya.”
Cuttt haka masu d’aukan shirin suka katse tare da kashe cameras dinsu.
Dai-dai lokacin ne Kuma anan gidansu Rayyern din Zuciyar Abba tayi wani irin bugawa, saboda sunan Yarinyar da yaji acikin kunnuwansa.
“Jannart Idi Sale Dakata!!”.
Abba ya maimaita sunan acikin zuciyarsa, cikin sauri kuma ya d’ago da kansa ya kalli Mamy, wacce ita dinma shi take kallo, fuskarta dauke da tsananin mamaki.
Atare kuma suka sake maida kallonsu ga tv,n.
“Idan har sunan da yarinyar ta fad’a shine sunanta na gaskiya, To Lallai kuwa, wannan itace yarinyar da Barrister Kabir yazo musu da maganarta.”
Abban ya fad’i haka azuciyarsa, fuskarsa cike da tsananin mamaki, hadi da tu’ajjudin faruwar hakan.
Tuno wani abu da yayi ne kuma yasa Lokaci daya ya saki wani irin murmushi, mai dauke da tsananin jin dadi, hadi da cin nasara.
Tabbas ayanzu ya sake gaskatawa, cewar Nesa tazo ta kusa.
Acan TV station din kuwa Zumbur haka Dr Rayyern din ya mik’e tsaye, wanda hakan yasa cikin sauri MD da kuma sauran assistance managing director hadi da manyan masu muk’amai na tashan suka nufo wajen Rayyern din kaitsaye, hannayensu suka dinga mik’a masa daya bayan daya suna gaisawa cikin mutuntaka.
Inda MD da farinciki yasa bakinsa kasa rufuwa yace.
“Mungode Kwarai Dr. Rayyern, Allah Ubangiji yasa kafi haka, nida sauran ma’aikatan wannan tasha, muna godiya agareka, daka samu daman zuwa wannan tasha.
Tabbas zuwanka ya sake daga darajar tasharmu.”
Yar sauk’ak’ekk’iyar Murmushi kawai yayiwa MD’n, Yayinda MD kuwa yasa a daukowa Dr. Rayyern din kyauta ta musamman, wanda sukayi dan nuna godiyarsu agaresa.
Salman, Aysha Lawal da kuma Aunty Fauziy D Sulaiman dake gefe kuwa, hannayensu suka d’agawa Jannart alaman jinjina, kowannensu fuskarsa cike da farincikin, irin nasaran da Jannart din ta samu, Domin kuwa ta kafa tarihin da akab gidan television’s din dake Nigeria babu wanda ya tab’a kafawa.
Ta kawo musu babban hazikin Dan kasuwa kuma Doctor, mutumin da kowa yake fatan ganinsa, yau gashi Jannart din ta kawosa ta kuma bayyanawa duniya fuskarsa, daya jima yana b’oyeta.
Murmushi Jannart din tayi musu, tare kuma da k’arasowa ta kalli Salman, wanda azahirance yana cikin tsananin farinciki, akasin hakan kuwa, shine Sam bayajin dadin zuciyarsa, saboda tun zaman Jannart da kuma Dr. Rayyern din daya gani awaje daya, yaji zuciyarsa ta karye, badan komai ba kuwa saidan tsananin matching din da yaga sunyi, sosai suka haska tamkar wasu taurari, sai kuma ayanzun ya sake tabbatarwa da kansa, cewar kwata-kwata ma Jannart Dakata ba sa’ar sa bace, Jannart matar manyan mutane ce.
Kana kuma Jannart zara ce acikin taurari, furta wani abu daya shafi so agareta, kuwa tamkar karambani ne, saboda ya sani bashi da wannan matsayin.
Haka dai jikinsa adan sanyaye ya juya suka rufawa su MD din baya, wanda tuni sun nufi hanyar waje, Dan raka Dr. Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara mota.
Cikin masu rakiyan kuwa harda Asiya, wacce takejin kamar ta fashe da kuka, ko tasa ihu.
Badan komai ba kuwa, saidan ta samu ko kallo daya ne Dr. Rayyern din yayi mata.
Jannart kuwa kaitsaye Office dinsu ta wuce, batare da tabi yan rakiyar ba, Sam ita rakasa ma baya gabanta, hasalima mamaki take akan yanda taga, y’an Office din nasu suna karramasa, Tabbas Koda ga wahalan da tasha wajen nemansa, tasan cewar shidin babban mutum ne.
D’an tab’e bakinta tayi alokaci da ta samu waje ta zauna.
Hakanan takejin zuciyarta wasai, tamkar an zare mata wani mashi dake sukanta.
“Alhamdulillah Allah, Kai katsaramin komai, yanzu bazan rasa aikina ba, bana kuma da wata fargaba, Thanks for everything Allah.”
Ta fad’i hakan abayyane Cikin kuma tsananin farinciki, dajin dadi.
Saboda duk wata fargabanta yanzu ya yaye.
Acan compound din tv station din kuwa, har wajen mota su MD suka rako Dr. Rayyern, bayan sun bashi kyautar karramawa.
Kasancewar kuma tun kafun su isa, Hadi'nsa ya bud’e masa murfin motar tasa ne, hakan yasa yana zuwa batare da wani b’ata lokaci ba ya shiga ya zauna.
Still harya rufe murfin motar kuma godiya su MD sukeyi masa, tare dayi masa fatan sauk’a lafiya.
Anutse kuwa Hadi yaja motar suka fice daga cikin gidan tv’n.
Fuska Asiya ta had’e tamkar zata had’iyi zuciyarta haka takeji.
Lallai tayi takaicin wannan ranan, saboda ko kallo daya bata samu daga wajen Dr. Rayyern din ba, hasali mai irin halittarta ma baisan tana wajen ba.
Dan Kallon kanta tayi, can cikin zuciyarta kuma taja tsaki, tare da cewa.
“Tayaya ma zai kalleni, tunda akwai irin waccar mayyar aduniya, natsaneki wallahi Jannart natsani ma Koda ganinki, saboda ke ne zaman office dinnan ya fara yimin kunci, kinzo kin hanani sakat, wai kawai saboda kina da kyau, mcheewww.”
Tak’are maganar nata da jan tsaki tare da juyawa ta koma Cikin office din, dan zuwa yanzu ita kad’ai aka bari awajen.
Acan cikin Office din kuwa, MD dakansa ya shigo cikin Office din su Jannart din, tare da bud’e hannayensa ya soma tafa mata.
Aikuwa Ganin haka yasa duk sauran ma’aikatan suma bud’e hannayensu suka soma tafa mata.
Cike da jinjina hadi da yaba k’wazonta MD yace.
“Congratulation Jannart, Lallai kin cika hazikar yar jarida, na kuma jinjinawa kwazonki, Tabbas samun irinki acikin aikin jarida abune mai kyau, ayau ta sanadiyarki tasharmu ta sake daukaka, kin shammace mu Kwarai, dole ne mu baki lambar yabo, zaku ma muyi miki karramawa ta musamman.”
“Kwarai kuwa Jannart hakika kinyi Namijin kokari, Tabbas kin cika hazikar Mace mai kishi da kuma son aikinta congratulations.”
Cewar Aunty Fauziya D Sulaiman.
Jannart din kuwa murmushin daya bayyana kyawawan hakwaranta tayi, cikin tsananin jin dadi tace.
“Congratulations to you all my colleagues, Domin duk wannan nasaran nasa meta ne da k’arfafawar guiwanku, musamman Salman, Thank you so much Salman.”
Murmushin Jin dadi duk sukayi, Yayinda Salman kuwa ya sunkuyar da kansa kasa yana murmushi.
Asiya dake gefe kuwa ji take kaman tayi hauka, tsabar k’unci takaici da kuma bak’in Cikin daya cika zuciyarta.
Haka dai suka ci gaba da tattaunawa atsakaninsu, Yayinda fuskar kowannensu ke dauke da tsananin farin ciki.
Amma banda na Asiya da har hawayen takaici saida suka tara.
MD kuwa yau din da kansa yasa akayi musu order’n delicious food, tare da kayan drinks.
Anan cikin babban falon da suke ajiye baki, suka gudanar da d’an kwarya kwaryan party.
Inda kuma sukayiwa Jannart din tanadin Karin matsa yi na musamman.
Bayan sun gama yar kwarya kwaryan Partyn nasu ne kuma ta dau Jakarta Kai tsaye ta wuce, gida zuciyarta cike da tsananin farinciki.
Yayinda daga can b’angaren Dr Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara kuwa, daga tv station din kaitsaye gidansu ya nufa.
Suna isa bakin gate din kuwa Baba Hadi ya danna horn, cikin sauri da kuma azama Baba Maud’o ya karaso ya bude musu gate din, direct Baba Hadi ya tura motar cikin gida, tare da dai-dai-ta parking dinta a parking space.
Ahankali Rayyern din ya bud’e motar ya fito,
Kana ya juya ya nufi wurin da Baba Maud’o yake tare da ɗan longoɓar da kai alaman gaisuwa.
Murmushi Baba Mauɗo yayi tare da mishi sannu. kafun kaitsaye ya nufi babban falon gidan.
Inda Mamy da Abba dasu Ramadan ke zaune.
Shigowarsa cikin falonne kuma yasa duk suka d’ago Kai suka kalleshi, Riyyam-nsra ne ya taso da d’an hanzari ya rungumeshi, tare da cewa.
“Gaskiya ko Hamma Rayyern kaina musamman ne, ka iya amsa duk wata tambaya da akayi Ma.”
Kansa kawai ya Dan jinjina saboda duk ji yakeyi kansa a gajiye, karasa shigowa cikin falon yayi, tare da yiwa Abba da Mamy sannu da gida.
“Yauwa Rayyern sannu da dawowa.”
Mamy ta amsa masa, Yayinda Abba kuwa Da Kai ya amsa masa.
“Hamma Rayyern congratulation.” Ramadan ya fad’a k’asa k’asa yayinda yake Dan danne dariyarsa, badon komai ba kuma saidan sanin halin Yayan nasa da yayi, kwata-kwata baya son yawan magana amma kuma yau gashi wata tasashi yayi ta magantuwa.
Da kai kawai Rayyern din ya amsa masa, batare daya zauna acikinsu ba kuma kaitsaye ya wuce part d’insa.
Wanka yayi tare da dauro alwalan sallan magriba, bayan ya kimtsa kansa acikin wasu kaya marar nauyi ne kuma, ya fito inda dukansu suka had’a hanya wajen zuwa masallaci.
Koda sukaje masallacin kuwa kamar Koda yaushe basu dawo ba saida aka Sallame sallan Isha.
Suna dawowa gidan kuwa suka samu Mamy ta had’e musu lafiyayyen dinner, hakan yasa duk suka k’arasa kan dining table din suka zazzauna.
Yau din kuma Riyyam-nsra ne da kansa ya amshi Mamy wajen yin saving dinsu, shida kansa ya zubawa kowa abincin banda Abba da Mamy ta zuba mishi nashi, sannan da kansa ya had’awa Hamma Rayyern din tea.
Bayan ya kammala had’a musu ne kuma, kowa ya soma cin abincinsa, anutse Abba ya d’ago da kansa ya kalli Rayyern cikin jinjina da kuma ya bawa yace.
“Tabbas hirar da akayi da kai yau, tayi armashi da kuma ma’ana, sannan shawarwarin daka bayar shawara ne masu kyau, gaskiya na jinjina maka,”.
Sai kuma ya ɗan tsagaita kana ya ɗan kalleshi tare daci gaba da cewa. “Amma da kashawarce ni kafun hakan, To fa da bazakaje ba.”
Zazzafan tea din dake bakinsa ya had’iya, kana cikin yin kasa dakai yace.
“Kayi hakuri Abba nima banaje Dan son raina bane, naje ne kawai saboda nayi musu alk’awari, sannan banason wanda aka bawa kwangilar nema na din ya rasa aikinsa, kamar yanda manyansa suka bashi zab’i.”
Kai Abban ya jinjina, batare kuma daya ja zancen yayi tsawo ba yace.
“Shikenan To Rayyern Allah ya taimaka ya tsare min kai.”
Da Ameen duk suka amsa.
Bayan sun kammala cin abincinne kuma, kaitsaye Rayyern din ya wuce daki’n sa.
Dr Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara din ya fad’a atausashe, saboda yasan izuwa yanzu duk su Abbansa suna kallonsa.
Jannart kuwa juyowa tayi ta fuskanci Camera hadi da cewa.
“To masu kallonmu duka duka anan muka kawo k’arshen shirin namu, tare da babban bak’onmu”.
Ta ƙare mgnar da juyowa tana kallon Dr Rayyern.
Numfashi ya ɗan fesar tare da cewa.
“Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara”.
Gyara zamanta tayi tare da cewa.
“Sai kuma ni dana shirya na kuma gabatar JANNART IDI SALE DAKATA. Nake, mana fatan mu hade awani sati Idan Allah ya kaimu a huta gajiya.”
Cuttt haka masu d’aukan shirin suka katse tare da kashe cameras dinsu.
Dai-dai lokacin ne Kuma anan gidansu Rayyern din Zuciyar Abba tayi wani irin bugawa, saboda sunan Yarinyar da yaji acikin kunnuwansa.
“Jannart Idi Sale Dakata!!”.
Abba ya maimaita sunan acikin zuciyarsa, cikin sauri kuma ya d’ago da kansa ya kalli Mamy, wacce ita dinma shi take kallo, fuskarta dauke da tsananin mamaki.
Atare kuma suka sake maida kallonsu ga tv,n.
“Idan har sunan da yarinyar ta fad’a shine sunanta na gaskiya, To Lallai kuwa, wannan itace yarinyar da Barrister Kabir yazo musu da maganarta.”
Abban ya fad’i haka azuciyarsa, fuskarsa cike da tsananin mamaki, hadi da tu’ajjudin faruwar hakan.
Tuno wani abu da yayi ne kuma yasa Lokaci daya ya saki wani irin murmushi, mai dauke da tsananin jin dadi, hadi da cin nasara.
Tabbas ayanzu ya sake gaskatawa, cewar Nesa tazo ta kusa.
Acan TV station din kuwa Zumbur haka Dr Rayyern din ya mik’e tsaye, wanda hakan yasa cikin sauri MD da kuma sauran assistance managing director hadi da manyan masu muk’amai na tashan suka nufo wajen Rayyern din kaitsaye, hannayensu suka dinga mik’a masa daya bayan daya suna gaisawa cikin mutuntaka.
Inda MD da farinciki yasa bakinsa kasa rufuwa yace.
“Mungode Kwarai Dr. Rayyern, Allah Ubangiji yasa kafi haka, nida sauran ma’aikatan wannan tasha, muna godiya agareka, daka samu daman zuwa wannan tasha.
Tabbas zuwanka ya sake daga darajar tasharmu.”
Yar sauk’ak’ekk’iyar Murmushi kawai yayiwa MD’n, Yayinda MD kuwa yasa a daukowa Dr. Rayyern din kyauta ta musamman, wanda sukayi dan nuna godiyarsu agaresa.
Salman, Aysha Lawal da kuma Aunty Fauziy D Sulaiman dake gefe kuwa, hannayensu suka d’agawa Jannart alaman jinjina, kowannensu fuskarsa cike da farincikin, irin nasaran da Jannart din ta samu, Domin kuwa ta kafa tarihin da akab gidan television’s din dake Nigeria babu wanda ya tab’a kafawa.
Ta kawo musu babban hazikin Dan kasuwa kuma Doctor, mutumin da kowa yake fatan ganinsa, yau gashi Jannart din ta kawosa ta kuma bayyanawa duniya fuskarsa, daya jima yana b’oyeta.
Murmushi Jannart din tayi musu, tare kuma da k’arasowa ta kalli Salman, wanda azahirance yana cikin tsananin farinciki, akasin hakan kuwa, shine Sam bayajin dadin zuciyarsa, saboda tun zaman Jannart da kuma Dr. Rayyern din daya gani awaje daya, yaji zuciyarsa ta karye, badan komai ba kuwa saidan tsananin matching din da yaga sunyi, sosai suka haska tamkar wasu taurari, sai kuma ayanzun ya sake tabbatarwa da kansa, cewar kwata-kwata ma Jannart Dakata ba sa’ar sa bace, Jannart matar manyan mutane ce.
Kana kuma Jannart zara ce acikin taurari, furta wani abu daya shafi so agareta, kuwa tamkar karambani ne, saboda ya sani bashi da wannan matsayin.
Haka dai jikinsa adan sanyaye ya juya suka rufawa su MD din baya, wanda tuni sun nufi hanyar waje, Dan raka Dr. Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara mota.
Cikin masu rakiyan kuwa harda Asiya, wacce takejin kamar ta fashe da kuka, ko tasa ihu.
Badan komai ba kuwa, saidan ta samu ko kallo daya ne Dr. Rayyern din yayi mata.
Jannart kuwa kaitsaye Office dinsu ta wuce, batare da tabi yan rakiyar ba, Sam ita rakasa ma baya gabanta, hasalima mamaki take akan yanda taga, y’an Office din nasu suna karramasa, Tabbas Koda ga wahalan da tasha wajen nemansa, tasan cewar shidin babban mutum ne.
D’an tab’e bakinta tayi alokaci da ta samu waje ta zauna.
Hakanan takejin zuciyarta wasai, tamkar an zare mata wani mashi dake sukanta.
“Alhamdulillah Allah, Kai katsaramin komai, yanzu bazan rasa aikina ba, bana kuma da wata fargaba, Thanks for everything Allah.”
Ta fad’i hakan abayyane Cikin kuma tsananin farinciki, dajin dadi.
Saboda duk wata fargabanta yanzu ya yaye.
Acan compound din tv station din kuwa, har wajen mota su MD suka rako Dr. Rayyern, bayan sun bashi kyautar karramawa.
Kasancewar kuma tun kafun su isa, Hadi'nsa ya bud’e masa murfin motar tasa ne, hakan yasa yana zuwa batare da wani b’ata lokaci ba ya shiga ya zauna.
Still harya rufe murfin motar kuma godiya su MD sukeyi masa, tare dayi masa fatan sauk’a lafiya.
Anutse kuwa Hadi yaja motar suka fice daga cikin gidan tv’n.
Fuska Asiya ta had’e tamkar zata had’iyi zuciyarta haka takeji.
Lallai tayi takaicin wannan ranan, saboda ko kallo daya bata samu daga wajen Dr. Rayyern din ba, hasali mai irin halittarta ma baisan tana wajen ba.
Dan Kallon kanta tayi, can cikin zuciyarta kuma taja tsaki, tare da cewa.
“Tayaya ma zai kalleni, tunda akwai irin waccar mayyar aduniya, natsaneki wallahi Jannart natsani ma Koda ganinki, saboda ke ne zaman office dinnan ya fara yimin kunci, kinzo kin hanani sakat, wai kawai saboda kina da kyau, mcheewww.”
Tak’are maganar nata da jan tsaki tare da juyawa ta koma Cikin office din, dan zuwa yanzu ita kad’ai aka bari awajen.
Acan cikin Office din kuwa, MD dakansa ya shigo cikin Office din su Jannart din, tare da bud’e hannayensa ya soma tafa mata.
Aikuwa Ganin haka yasa duk sauran ma’aikatan suma bud’e hannayensu suka soma tafa mata.
Cike da jinjina hadi da yaba k’wazonta MD yace.
“Congratulation Jannart, Lallai kin cika hazikar yar jarida, na kuma jinjinawa kwazonki, Tabbas samun irinki acikin aikin jarida abune mai kyau, ayau ta sanadiyarki tasharmu ta sake daukaka, kin shammace mu Kwarai, dole ne mu baki lambar yabo, zaku ma muyi miki karramawa ta musamman.”
“Kwarai kuwa Jannart hakika kinyi Namijin kokari, Tabbas kin cika hazikar Mace mai kishi da kuma son aikinta congratulations.”
Cewar Aunty Fauziya D Sulaiman.
Jannart din kuwa murmushin daya bayyana kyawawan hakwaranta tayi, cikin tsananin jin dadi tace.
“Congratulations to you all my colleagues, Domin duk wannan nasaran nasa meta ne da k’arfafawar guiwanku, musamman Salman, Thank you so much Salman.”
Murmushin Jin dadi duk sukayi, Yayinda Salman kuwa ya sunkuyar da kansa kasa yana murmushi.
Asiya dake gefe kuwa ji take kaman tayi hauka, tsabar k’unci takaici da kuma bak’in Cikin daya cika zuciyarta.
Haka dai suka ci gaba da tattaunawa atsakaninsu, Yayinda fuskar kowannensu ke dauke da tsananin farin ciki.
Amma banda na Asiya da har hawayen takaici saida suka tara.
MD kuwa yau din da kansa yasa akayi musu order’n delicious food, tare da kayan drinks.
Anan cikin babban falon da suke ajiye baki, suka gudanar da d’an kwarya kwaryan party.
Inda kuma sukayiwa Jannart din tanadin Karin matsa yi na musamman.
Bayan sun gama yar kwarya kwaryan Partyn nasu ne kuma ta dau Jakarta Kai tsaye ta wuce, gida zuciyarta cike da tsananin farinciki.
Yayinda daga can b’angaren Dr Rayyern Bashir Muhammad Mai-nasara kuwa, daga tv station din kaitsaye gidansu ya nufa.
Suna isa bakin gate din kuwa Baba Hadi ya danna horn, cikin sauri da kuma azama Baba Maud’o ya karaso ya bude musu gate din, direct Baba Hadi ya tura motar cikin gida, tare da dai-dai-ta parking dinta a parking space.
Ahankali Rayyern din ya bud’e motar ya fito,
Kana ya juya ya nufi wurin da Baba Maud’o yake tare da ɗan longoɓar da kai alaman gaisuwa.
Murmushi Baba Mauɗo yayi tare da mishi sannu. kafun kaitsaye ya nufi babban falon gidan.
Inda Mamy da Abba dasu Ramadan ke zaune.
Shigowarsa cikin falonne kuma yasa duk suka d’ago Kai suka kalleshi, Riyyam-nsra ne ya taso da d’an hanzari ya rungumeshi, tare da cewa.
“Gaskiya ko Hamma Rayyern kaina musamman ne, ka iya amsa duk wata tambaya da akayi Ma.”
Kansa kawai ya Dan jinjina saboda duk ji yakeyi kansa a gajiye, karasa shigowa cikin falon yayi, tare da yiwa Abba da Mamy sannu da gida.
“Yauwa Rayyern sannu da dawowa.”
Mamy ta amsa masa, Yayinda Abba kuwa Da Kai ya amsa masa.
“Hamma Rayyern congratulation.” Ramadan ya fad’a k’asa k’asa yayinda yake Dan danne dariyarsa, badon komai ba kuma saidan sanin halin Yayan nasa da yayi, kwata-kwata baya son yawan magana amma kuma yau gashi wata tasashi yayi ta magantuwa.
Da kai kawai Rayyern din ya amsa masa, batare daya zauna acikinsu ba kuma kaitsaye ya wuce part d’insa.
Wanka yayi tare da dauro alwalan sallan magriba, bayan ya kimtsa kansa acikin wasu kaya marar nauyi ne kuma, ya fito inda dukansu suka had’a hanya wajen zuwa masallaci.
Koda sukaje masallacin kuwa kamar Koda yaushe basu dawo ba saida aka Sallame sallan Isha.
Suna dawowa gidan kuwa suka samu Mamy ta had’e musu lafiyayyen dinner, hakan yasa duk suka k’arasa kan dining table din suka zazzauna.
Yau din kuma Riyyam-nsra ne da kansa ya amshi Mamy wajen yin saving dinsu, shida kansa ya zubawa kowa abincin banda Abba da Mamy ta zuba mishi nashi, sannan da kansa ya had’awa Hamma Rayyern din tea.
Bayan ya kammala had’a musu ne kuma, kowa ya soma cin abincinsa, anutse Abba ya d’ago da kansa ya kalli Rayyern cikin jinjina da kuma ya bawa yace.
“Tabbas hirar da akayi da kai yau, tayi armashi da kuma ma’ana, sannan shawarwarin daka bayar shawara ne masu kyau, gaskiya na jinjina maka,”.
Sai kuma ya ɗan tsagaita kana ya ɗan kalleshi tare daci gaba da cewa. “Amma da kashawarce ni kafun hakan, To fa da bazakaje ba.”
Zazzafan tea din dake bakinsa ya had’iya, kana cikin yin kasa dakai yace.
“Kayi hakuri Abba nima banaje Dan son raina bane, naje ne kawai saboda nayi musu alk’awari, sannan banason wanda aka bawa kwangilar nema na din ya rasa aikinsa, kamar yanda manyansa suka bashi zab’i.”
Kai Abban ya jinjina, batare kuma daya ja zancen yayi tsawo ba yace.
“Shikenan To Rayyern Allah ya taimaka ya tsare min kai.”
Da Ameen duk suka amsa.
Bayan sun kammala cin abincinne kuma, kaitsaye Rayyern din ya wuce daki’n sa.