Sashe 67
Tubali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Ka kwantar da hankalinka Barrister, Domin kamar yanda ka aminta damu, ka d’auko Jannart ka kawo mana ita cikin gidannan Insha Allah, bazamu bari hawayenta su zuba ak’asa ba, zamu zame mata iyaye na gari, idan tayi rayuwar maraici abaya Ina mai tabbatar maka da ayanzu Jannart bazata sakeyin rayuwar maraici ba, Zamu zame mata Garkuwa da yardar Allah, ka bamu amana kuma zamu rik’e, Jannart ba zata sakeyin kukan kadaici da maraici ba, zamu bata duk wani farinciki.”
Kai Barrister Kabir din ya jinjina, tare da kamo hannun Abban yace.
“Nagode kwarai Alhaji Bashir, Lallai Tabbas yanzu na sake gamsuwa da cewar, na kawo Jannart inda ya dace, na kawota inda za’a bata kulawa, inda bakuma za’a bari tayi kunci ba, Alhamdulillah Allah ya tayaku rik’o”.
“Ameen.”
Abba da Baba Maud’o suka amsa.
Hannu Barrister Kabir din ya mik’awa, Abba da Baba Maud’o suka sakeyin musabaha.
Bayan yayi musu sallama ne kuma ya bud’e motarsa ya shiga, Ari ne kuma ya bud’e masa gate din gidan ya fice.
Har acikin ransa yana mejin gamsuwa na abunda ya aikata, Domin yasani acikin abunda ya aikatan Kwata-kwata babu kuskure, Allah yaga zuciyarsa da kuma kyakkyawan nufinsa.
Burinsa shine fito da gaskiyar da azzalumai suka b’oye, wanda kuma yake da tabbacin Allah zai bashi sa’a, akan dukkan komai, Domin Allah ba azzalumin kowa ba ne, saidai wanda ya zalunci kansa.
Su Abba kuwa ganin tafiyarsa ne, yasa Baba Maud’o wucewa makwancinsa kaitsaye, inda shi kuwa Abba juyawa yayi ya koma cikin gidan.
Barrister Kabir kuwa kaitsaye gidansa ya nufa.
Koda ya isa cikin gidannsa karfe 12:40 na dare.
Kaitsaye dakinsa ya wuce, bayan yayi wanka ne kuma Aunty Dijat ta kawo masa Coffee.
Sai-dai ganin yanda gaba daya jikin mijin nata ke sanyaye ne yasa, ta gyara zama tare da kamo hannunsa, cike dason basa kwarin guiwa tace.
“Ka kwantar da hankalinka Abban Hafeez, Domin nasan duk wani abunda ke damunka, ayanzu bai wuce akan Jannart, meyasa zaka damu Abban Hafeez, bayan kasan cewar wannan auren shine abunda zai kawo sauyi da farinciki acikin rayuwar Jannart, wannan auren shi zaisa Jannart tasan wacece ita, shi ne kuma zai warware mata duk wani k’ulli dake cikin rayuwarta, Tabbas wannan auren al'khairi ne, kuma Insha Allah akwai lokacin da Jannart zatayi al'fahari da wannan Auren, musamman alokacin da ta gano cewar ka zab’a mata miji, mai nagarta irin wanda bashida saukin samu, sannan ka ceci rayuwarta daga sharrin mak’iyan dake kewaye da ita, way’anda take kwana acikinsu, take tashi batare da ta sani ba.”
Kai Barrister Kabir din ya jinjina, Cikin samun karfin guiwa kuma yace.
“Insha Allah Jannart zatayi farinciki, komai kuma zai yaye, ayanzu duniyarta zatayi sanyi, Domin tafita daga cikin magauta, hakika ko ayau na mutu, nasan na mik’a Jannart ga inda za’a tsaya mata, inda babu wani maitsaurin ido daya isa zuwa yaci mutumcin ta, saboda Rayyern ba kanwar lasa bane ba kuma mutum bane kamar kowaba, shi na musamman ne domin naga tsoronshi cikin idanun Magautan nasa da Jannart.
Tun ran forko kuma dana ganshi ya tunomin wani ma irin zarrarsa a tsakiyar su Yaya idi wanda sukayi nasarar kaudashi a duniya.
Sai naketa kamar Allah ya turo Rayyern garesune dan ya tono jiyansu ya tsaida yau ɗinsu ya birkita gobensu yadda yake musu mgna kamar ɗan fansa ne, Insha Allah kuma watarana Jannart sai ta zamo wani sashi na jikinsa.”
Murmushi Aunty Dijat tayi, saboda ta fahimci kalaman da mijinnata ke nufi.
Acan gidan su Rayyern kuwa, Koda Abba ya dawo cikin falon, anan ya sameta zaune ita da Jannart din, da har yanzu ta kasa daina zubda hawaye.
Zama Abban yayi
Tare da tausasa muryarsa cikin aminci yace.
“Jannart”.
Wani irin sanyi taji muryar Abba ya sakar mata.
Shi kuwa a mutunce yace.
“Jannart d’ago kanki ki kalleni.”
Jannart dake sakin shesshekan kuka, sake Jin Muryar Babban mutum acikin kunnuwanta ne yasa ta d’ago kanta Ahankali, da kuma Idanunta wanda sukayi luhu-luhu ta kalleshi.
Kai Abban ya girgiza, kana cikin lallashi da ban baki yace.
“Kada kiyi mini wani kallo na daban Jannart, inaso ki kalleni amatsayin mahaifinki, ni Babanki ne, kada ki ajiyeni amatsayin suruki kawai, saboda na daukeki ne amatsayin y’a, wanda har abada kuma bazan tab’a bari kunci yayi tasiri acikin zuciyarki ba, wannan gidan kada ki daukeshi amatsayin gidan aurenki kawai, ki daukeshi amatsayin gidanku, kafun yanzu bamu sanki ba, amma ayanzu kedin tamuce, kin zama daya daga cikin iyalinmu, munzama iyayenki ke kuma kinzama y’armu, Ramadan ya zama shak’ik’in d’an uwa agareki, dama kuma duk wani wanda yake tare damu, duk wani damuwa da ya dameki kuwa ki sanar mana.
Insha Allah zamu magance miki ita, saboda haka ki daina kuka kinji, kisa aranki cewa muna tare dake, kuma Allah Ma yana tare dake.”
Kanta ta d’an jinjina, saboda yanda kalaman Abban sukayi tasiri a zuciyarta, duk da cewar ta kasa tsaida hawayen dake zuba acikin Idanunta.
Cikin sanyi hadi da muryarta wacce bata fita sosai tace.
“Nagode Abba, nagode da karamcin da kukayi min Allah ya kara girma.”
Murmushi Abban yayi, kana cikin jin dadin biyayyar yarinyar yace.
“Ba komai Jannart, Insha Allah zamu zame miki iyaye na gari, Mamyn Rayyern Ina Rayyern din kuma ya tafi.”
Ya ƙare mgnar yana kallon Mamy.
“Rayyern ya haura sama.” Mamy ta fad’a tana murmushi.
Kai Abban ya jinjina, kana cikin kulawa yace.
“To dare na tayi, ki Kai Jannart masaukinta ta kwanta.”
Ya ƙare mgnar yana nuna mata side din da zata kai Jannart ɗin.
To Mamyn tace, tare kuma da kama Hannun Jannart din suka nufi, wata had’add’Iyar k’ofa dake nan cikin falon, kusa da side din kitchine da kuma dining area.
Ahankali Mamy ta tura k’ofar d’akin.
“Ki shigo da bismillah.”
Mamyn ta fad’awa Jannart Cikin kulawa, hakan kuwa akayi da bismillah Jannart ta jefa k’afarta ta dama acikin falon.
Falo ne mai kyaun gaske wanda aka k’awata cikinsa, da wasu had’add’un royal cushions masu kyau, sai kuma labulayen da aka k’awata jikin window dana bedroom door dashi, atsakiyar falon kuwa, wani lallausan carpet ne maikyau da girma, sai kuma babban tv’ plasma’n da aka daurasa akan wani babban tv stand.
Sosai falon yayi kyau, duk da cewar babu wasu tarkace masu yawa acikinsa, amma komai da komai mai tsada ne.
Sanyin AC da kuma daddad’an kamshin room freshener dake tashi acikin falonne yasa Jannart lumshe Idanunta.
Inda Mamy kuwa kaitsaye ta wuce jin wata kofa dake cikin falon, still kuma tana rik’e da hannun Jannart ta bud’e kofar suka kutsa ciki.
Bedroom ne madaidaici wanda aka zuba masa furnitures na alfarma, bed, drawer, and dressing mirror with bedside drawer then shoe rug.
Komai dake cikin d’akin kalan pink and white ne, shiyasa haduwarsa yake dajan hankali, kamar dai falon, Domin shima cushions da labulayen cikinsa duk pink and white ne.
K’arasa shigowa cikin dakin sukayi, Yayinda Mamyn ta zaunar da ita bakin gadon daya sha bedsheet na alfarma.
Kallonta Mamyn tayi, kana cikin tausasawa tace.
“Jannart Nan shine masaukinki, zaki zauna ne kuma kafun agama gyara miki asalin inda zaki zauna.
Dan Allah Jannart ki saki jikinki, babu wani wanda zai takura miki, akwai komai na amfani da zaki buk’ata, duk abunda kikeso kuma kiyi min magana, banason kiyi kuka kinji ko Jannart”.
Cikin sharce hawayen ta gyaɗa kai alamun.
Eh taji.
Cikin jin daɗi Mamy tace.
“Kinga ke amanace agaremu, zubar hawayenki kuma zai zamo damuwa azuciyoyin mu, duk wani abunda ya dameki ki sanar dani, kada kiji shakka ko kuma nauyi na.
Domin bana daukanki amatsayin suruka, sannan kada ki bari damuwa tayi nasarar tank’wasar da zuciyarki, kowani bawa yana d’auke da irin salon k’addararsa, saboda haka ki kwantar da hankalinki, ke taki k’addarar ahaka tazo, Insha Allah kuma watarana komai zai wuce, babu wani damuwa dake tabbata, kiyi farinciki aduk wani yanayin da kika samu kanki kinji Jannart.”
Kai Jannart din ta jinjina, tare kuma da kama y’an yatsun hannunta cikin sanyi tace.
“Insha Allahu Mamy zanyi duk abinda kikace.”
Murmushi Mamyn tayi, cikin tsananin jin dadi da farinciki tace.
“Yauwa Jannart, Allah Yayi miki albarka, naji dadin biyayyarki.
Domin duk wani wanda yake daukar maganan na sama dashi, har abada bazai tab’ayin dana sani ba.”
Ta ƙare mgnar tana nufar Bathroom.
Ruwan wanka mai dumi Mamyn ta had’awa Jannart acikin bath, tare kuma dasa mata turaren wanka mai dadin k’amshi.
Koda ta fito daga toilet din, hannun Jannart din ta kamo ta miƙar da ita, tare da cewa.
“Yauwa Jannart kije kiyi wanka ko nasan..”
Sauran maganan Mamyn ne ya mak’ale, saboda yanda taji duk jikin Jannart din ya dau zafi.
“Subahanallah Jannart gashi duk jikinki zafi, nasan kuma hakan bai rasa na saba, da kukan da kikayi, kije kiyi wanka, akwai sabin towels acikin toilet din saikiyi amfani dasu, akwai kuma ruwan dumi dana had’a miki a bathtub.”
“Nagode Mamy.”
Jannart din ta fad’a, Ahankali tare kuma da zare dogon hijab din dake jikinta.
Mamy kuwa murmushi tayi, kana ta juya ta fice daga cikin d’akin.
Koda ta fito nan cikin falon nasu, kaitsaye kitchine ta wuce.
Yar ƙaramar tukunya tasa akan gas, cikin abunda baiwuce.
15mn ba kuwa ta kammala had’a indomie’n da ta dafawa Jannart din, wanda yaji kayan hadi da kifi, bayan ta juye indomie’n a plate ne kuma, ta had’a tea mai kauri acikin mug.
Bayan ta gama kimtsa komai ne kuma, kaitsaye ta haura sama zuwa dakin Rayyern.
Zaune yake akan gadonsa, inda ya sanja shigar jikinsa, zuwa kayan bacci masu taushi.
Yanayin yanda yayi zaman duka k’afafunsa na k’asa, sannan kuma ya dafe kansa da hannayensa duka biyu.
Idanunsa arumtse suke, kana kuma time to time yake fesar da wani irin numfashi mai kama da ajiyan zuciya.
Mamy kuwa isowarta jikin kofar ne yasa ta d’an soma knocking.
Sai-dai har tsawon mintuna 2 tana knocking amma bataji a bud’e k’ofar ko kuma bata izinin shigowa ba.
Hakan kuwa shi yasa ta murd’a handle din kofar a zayonta ko yana bacci ne, ga mamakinta kuwa sai taga kofar ta bud’u.
Ahankali ta tura kanta cikin dakin tare dayin sallama.
Anan zaune ta hangosa, ya dafe Kai, da dukkan alama kuma yayi nisa acikin duniyar tunanin da yakeyi.
Kai Barrister Kabir din ya jinjina, tare da kamo hannun Abban yace.
“Nagode kwarai Alhaji Bashir, Lallai Tabbas yanzu na sake gamsuwa da cewar, na kawo Jannart inda ya dace, na kawota inda za’a bata kulawa, inda bakuma za’a bari tayi kunci ba, Alhamdulillah Allah ya tayaku rik’o”.
“Ameen.”
Abba da Baba Maud’o suka amsa.
Hannu Barrister Kabir din ya mik’awa, Abba da Baba Maud’o suka sakeyin musabaha.
Bayan yayi musu sallama ne kuma ya bud’e motarsa ya shiga, Ari ne kuma ya bud’e masa gate din gidan ya fice.
Har acikin ransa yana mejin gamsuwa na abunda ya aikata, Domin yasani acikin abunda ya aikatan Kwata-kwata babu kuskure, Allah yaga zuciyarsa da kuma kyakkyawan nufinsa.
Burinsa shine fito da gaskiyar da azzalumai suka b’oye, wanda kuma yake da tabbacin Allah zai bashi sa’a, akan dukkan komai, Domin Allah ba azzalumin kowa ba ne, saidai wanda ya zalunci kansa.
Su Abba kuwa ganin tafiyarsa ne, yasa Baba Maud’o wucewa makwancinsa kaitsaye, inda shi kuwa Abba juyawa yayi ya koma cikin gidan.
Barrister Kabir kuwa kaitsaye gidansa ya nufa.
Koda ya isa cikin gidannsa karfe 12:40 na dare.
Kaitsaye dakinsa ya wuce, bayan yayi wanka ne kuma Aunty Dijat ta kawo masa Coffee.
Sai-dai ganin yanda gaba daya jikin mijin nata ke sanyaye ne yasa, ta gyara zama tare da kamo hannunsa, cike dason basa kwarin guiwa tace.
“Ka kwantar da hankalinka Abban Hafeez, Domin nasan duk wani abunda ke damunka, ayanzu bai wuce akan Jannart, meyasa zaka damu Abban Hafeez, bayan kasan cewar wannan auren shine abunda zai kawo sauyi da farinciki acikin rayuwar Jannart, wannan auren shi zaisa Jannart tasan wacece ita, shi ne kuma zai warware mata duk wani k’ulli dake cikin rayuwarta, Tabbas wannan auren al'khairi ne, kuma Insha Allah akwai lokacin da Jannart zatayi al'fahari da wannan Auren, musamman alokacin da ta gano cewar ka zab’a mata miji, mai nagarta irin wanda bashida saukin samu, sannan ka ceci rayuwarta daga sharrin mak’iyan dake kewaye da ita, way’anda take kwana acikinsu, take tashi batare da ta sani ba.”
Kai Barrister Kabir din ya jinjina, Cikin samun karfin guiwa kuma yace.
“Insha Allah Jannart zatayi farinciki, komai kuma zai yaye, ayanzu duniyarta zatayi sanyi, Domin tafita daga cikin magauta, hakika ko ayau na mutu, nasan na mik’a Jannart ga inda za’a tsaya mata, inda babu wani maitsaurin ido daya isa zuwa yaci mutumcin ta, saboda Rayyern ba kanwar lasa bane ba kuma mutum bane kamar kowaba, shi na musamman ne domin naga tsoronshi cikin idanun Magautan nasa da Jannart.
Tun ran forko kuma dana ganshi ya tunomin wani ma irin zarrarsa a tsakiyar su Yaya idi wanda sukayi nasarar kaudashi a duniya.
Sai naketa kamar Allah ya turo Rayyern garesune dan ya tono jiyansu ya tsaida yau ɗinsu ya birkita gobensu yadda yake musu mgna kamar ɗan fansa ne, Insha Allah kuma watarana Jannart sai ta zamo wani sashi na jikinsa.”
Murmushi Aunty Dijat tayi, saboda ta fahimci kalaman da mijinnata ke nufi.
Acan gidan su Rayyern kuwa, Koda Abba ya dawo cikin falon, anan ya sameta zaune ita da Jannart din, da har yanzu ta kasa daina zubda hawaye.
Zama Abban yayi
Tare da tausasa muryarsa cikin aminci yace.
“Jannart”.
Wani irin sanyi taji muryar Abba ya sakar mata.
Shi kuwa a mutunce yace.
“Jannart d’ago kanki ki kalleni.”
Jannart dake sakin shesshekan kuka, sake Jin Muryar Babban mutum acikin kunnuwanta ne yasa ta d’ago kanta Ahankali, da kuma Idanunta wanda sukayi luhu-luhu ta kalleshi.
Kai Abban ya girgiza, kana cikin lallashi da ban baki yace.
“Kada kiyi mini wani kallo na daban Jannart, inaso ki kalleni amatsayin mahaifinki, ni Babanki ne, kada ki ajiyeni amatsayin suruki kawai, saboda na daukeki ne amatsayin y’a, wanda har abada kuma bazan tab’a bari kunci yayi tasiri acikin zuciyarki ba, wannan gidan kada ki daukeshi amatsayin gidan aurenki kawai, ki daukeshi amatsayin gidanku, kafun yanzu bamu sanki ba, amma ayanzu kedin tamuce, kin zama daya daga cikin iyalinmu, munzama iyayenki ke kuma kinzama y’armu, Ramadan ya zama shak’ik’in d’an uwa agareki, dama kuma duk wani wanda yake tare damu, duk wani damuwa da ya dameki kuwa ki sanar mana.
Insha Allah zamu magance miki ita, saboda haka ki daina kuka kinji, kisa aranki cewa muna tare dake, kuma Allah Ma yana tare dake.”
Kanta ta d’an jinjina, saboda yanda kalaman Abban sukayi tasiri a zuciyarta, duk da cewar ta kasa tsaida hawayen dake zuba acikin Idanunta.
Cikin sanyi hadi da muryarta wacce bata fita sosai tace.
“Nagode Abba, nagode da karamcin da kukayi min Allah ya kara girma.”
Murmushi Abban yayi, kana cikin jin dadin biyayyar yarinyar yace.
“Ba komai Jannart, Insha Allah zamu zame miki iyaye na gari, Mamyn Rayyern Ina Rayyern din kuma ya tafi.”
Ya ƙare mgnar yana kallon Mamy.
“Rayyern ya haura sama.” Mamy ta fad’a tana murmushi.
Kai Abban ya jinjina, kana cikin kulawa yace.
“To dare na tayi, ki Kai Jannart masaukinta ta kwanta.”
Ya ƙare mgnar yana nuna mata side din da zata kai Jannart ɗin.
To Mamyn tace, tare kuma da kama Hannun Jannart din suka nufi, wata had’add’Iyar k’ofa dake nan cikin falon, kusa da side din kitchine da kuma dining area.
Ahankali Mamy ta tura k’ofar d’akin.
“Ki shigo da bismillah.”
Mamyn ta fad’awa Jannart Cikin kulawa, hakan kuwa akayi da bismillah Jannart ta jefa k’afarta ta dama acikin falon.
Falo ne mai kyaun gaske wanda aka k’awata cikinsa, da wasu had’add’un royal cushions masu kyau, sai kuma labulayen da aka k’awata jikin window dana bedroom door dashi, atsakiyar falon kuwa, wani lallausan carpet ne maikyau da girma, sai kuma babban tv’ plasma’n da aka daurasa akan wani babban tv stand.
Sosai falon yayi kyau, duk da cewar babu wasu tarkace masu yawa acikinsa, amma komai da komai mai tsada ne.
Sanyin AC da kuma daddad’an kamshin room freshener dake tashi acikin falonne yasa Jannart lumshe Idanunta.
Inda Mamy kuwa kaitsaye ta wuce jin wata kofa dake cikin falon, still kuma tana rik’e da hannun Jannart ta bud’e kofar suka kutsa ciki.
Bedroom ne madaidaici wanda aka zuba masa furnitures na alfarma, bed, drawer, and dressing mirror with bedside drawer then shoe rug.
Komai dake cikin d’akin kalan pink and white ne, shiyasa haduwarsa yake dajan hankali, kamar dai falon, Domin shima cushions da labulayen cikinsa duk pink and white ne.
K’arasa shigowa cikin dakin sukayi, Yayinda Mamyn ta zaunar da ita bakin gadon daya sha bedsheet na alfarma.
Kallonta Mamyn tayi, kana cikin tausasawa tace.
“Jannart Nan shine masaukinki, zaki zauna ne kuma kafun agama gyara miki asalin inda zaki zauna.
Dan Allah Jannart ki saki jikinki, babu wani wanda zai takura miki, akwai komai na amfani da zaki buk’ata, duk abunda kikeso kuma kiyi min magana, banason kiyi kuka kinji ko Jannart”.
Cikin sharce hawayen ta gyaɗa kai alamun.
Eh taji.
Cikin jin daɗi Mamy tace.
“Kinga ke amanace agaremu, zubar hawayenki kuma zai zamo damuwa azuciyoyin mu, duk wani abunda ya dameki ki sanar dani, kada kiji shakka ko kuma nauyi na.
Domin bana daukanki amatsayin suruka, sannan kada ki bari damuwa tayi nasarar tank’wasar da zuciyarki, kowani bawa yana d’auke da irin salon k’addararsa, saboda haka ki kwantar da hankalinki, ke taki k’addarar ahaka tazo, Insha Allah kuma watarana komai zai wuce, babu wani damuwa dake tabbata, kiyi farinciki aduk wani yanayin da kika samu kanki kinji Jannart.”
Kai Jannart din ta jinjina, tare kuma da kama y’an yatsun hannunta cikin sanyi tace.
“Insha Allahu Mamy zanyi duk abinda kikace.”
Murmushi Mamyn tayi, cikin tsananin jin dadi da farinciki tace.
“Yauwa Jannart, Allah Yayi miki albarka, naji dadin biyayyarki.
Domin duk wani wanda yake daukar maganan na sama dashi, har abada bazai tab’ayin dana sani ba.”
Ta ƙare mgnar tana nufar Bathroom.
Ruwan wanka mai dumi Mamyn ta had’awa Jannart acikin bath, tare kuma dasa mata turaren wanka mai dadin k’amshi.
Koda ta fito daga toilet din, hannun Jannart din ta kamo ta miƙar da ita, tare da cewa.
“Yauwa Jannart kije kiyi wanka ko nasan..”
Sauran maganan Mamyn ne ya mak’ale, saboda yanda taji duk jikin Jannart din ya dau zafi.
“Subahanallah Jannart gashi duk jikinki zafi, nasan kuma hakan bai rasa na saba, da kukan da kikayi, kije kiyi wanka, akwai sabin towels acikin toilet din saikiyi amfani dasu, akwai kuma ruwan dumi dana had’a miki a bathtub.”
“Nagode Mamy.”
Jannart din ta fad’a, Ahankali tare kuma da zare dogon hijab din dake jikinta.
Mamy kuwa murmushi tayi, kana ta juya ta fice daga cikin d’akin.
Koda ta fito nan cikin falon nasu, kaitsaye kitchine ta wuce.
Yar ƙaramar tukunya tasa akan gas, cikin abunda baiwuce.
15mn ba kuwa ta kammala had’a indomie’n da ta dafawa Jannart din, wanda yaji kayan hadi da kifi, bayan ta juye indomie’n a plate ne kuma, ta had’a tea mai kauri acikin mug.
Bayan ta gama kimtsa komai ne kuma, kaitsaye ta haura sama zuwa dakin Rayyern.
Zaune yake akan gadonsa, inda ya sanja shigar jikinsa, zuwa kayan bacci masu taushi.
Yanayin yanda yayi zaman duka k’afafunsa na k’asa, sannan kuma ya dafe kansa da hannayensa duka biyu.
Idanunsa arumtse suke, kana kuma time to time yake fesar da wani irin numfashi mai kama da ajiyan zuciya.
Mamy kuwa isowarta jikin kofar ne yasa ta d’an soma knocking.
Sai-dai har tsawon mintuna 2 tana knocking amma bataji a bud’e k’ofar ko kuma bata izinin shigowa ba.
Hakan kuwa shi yasa ta murd’a handle din kofar a zayonta ko yana bacci ne, ga mamakinta kuwa sai taga kofar ta bud’u.
Ahankali ta tura kanta cikin dakin tare dayin sallama.
Anan zaune ta hangosa, ya dafe Kai, da dukkan alama kuma yayi nisa acikin duniyar tunanin da yakeyi.