← Book details Tubali Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 14 OF 81

Sashe 14

Tubali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ganin shigowarsu ne kuma yasa Mamy dake, tsaye agaban had’add’en dining table d’insu wanda aka k’awatasa da wasu fitinannun royal chairs, ta saki sassanyar murmushin dake bayyana tsananin k’aunarta ga ahalin nata, murya asake tace.
“Masha Allah! Our dinner is ready.”

Jin hakan da sukayi dinne kuma yasa kasu sakin murmushi, tare da wuce wa dining area din kai tsaye.

Ramadan kuwa kulolin da Mamy ta miƙo kishi ya amsa dasu plate and spoos da gorunan ruwa mai sanyi.
Kana ya juya ya fita, dan kaiwa su Baba Mauɗo nasu abincin cikin kamala da mutuntaka ya kai musu kana ya dawo.

Shikuwa Rayyern da tun fitowarsu daga masallaci, yake tasbihi acikin zuciyarsa, kaitsaye gaban had’add’en fridge’n mai kaman show glass d’in dake dining area din ya nufa, yana isa kuwa ya bud’e murfin fridge’n, tare da d’ansa kansa ya zaro babban ledan chocolate na diary milk , wanda ya d’au sanyi sosai.

Maida murfin fridge’n yayi ya rufe, tare da juyowa ya zauna akan d’aya daga cikin kujerun dining table d’in, wanda aka cika saman babban table d’in, da kayan cima kala kala, more especially fruits.

Ahankali ya b’are ledan, tare da kai chocolate d’in bakinsa.
Fitinannun idanunsa masu d’auke da long eye lashes ya lumshe, adaidai lokacin da yaji d’and’ano da kuma zak’in chocolate din ya mamaye harshen sa, wanda hakan yasa shi sake tura chocolate din abakinsa, tare da soma taunawa ahankali, yana maijin wani irin sanyi aransa, Tabbas aduk sanda yake cin abunda yakeso, yakanji wani irin gamsuwa na musamman, musamman madai duk wani abu mai zak’i, kwarai yanason zak’i sosai da sosai.

Abba da Mamy dake zaune kuwa idanunsu kawai suka zuba masa, musamman ma Abba da bayajin dad’in, yawan shan zak’in da Rayyern d’in keyi, always shan zak’i sai kace karamin yaro.

Shikuwa Rayyern da har yanzu idanunsa ke lumshe, hakanan yaji ajikinsa cewa akwai k’wayoyin idanun dake kansa, wanda hakan yasa ahankali yad’an ware oily eyes d’insa, masu matuk’ar kyau da daukar hankali.

Karab sukayi ido hudu da Abba, hakanne kuwa yasa shi d’an gyara zamansa, tare kuma da yin k’asa da kansa, saboda acikin 2 second din ya fahimci wani irin kallo Abban, nasa keyi masa.
Zare chocolate din dake bakinnasa yayi, tare da ajiyewa agefe.

Ganin hakanne kuma yasa Mamy da Ramadan yin murmushi, shikuwa Abba plate d’in dake dauke da crispy microwave Patatoe chips, and salad, da kuma onion sauce ya turowa Rayyern d’in gabansa.
Tare da cewa.
“Maza kacinye wannan.”

Plate din da Abban nasa ya turo masa ya kalla, tare da d’an zaro idanunsa, kana lokaci guda kuma ya sanja mood dinsa izuwa shagwab’a, akasalance cikin kuma muryarsa da bakowa kejinta ba yace.

“Abba duka wannan zan ci?.”

“Eh duka kuma yanzu nakeson kaci.” Abba ya fad’a cikin tsare gida.

Ahankali ya saukar da idanunsa k’asa, saboda yanda yaji tone din Abban nasu, yasan abun is seriously.
D’aukan plate d’in abincin yayi tare da fork ahankali, yakai abincin bakinsa bayan yayi bismillah.

Bai kuwa wani ci abincin sosai ba, ya d’ago kansa ya kalli Mamy dake cin abincinta itama.
Cikin muryarsa dake bayyana rashin sabonsa dayin magana mai yawa yace.

“Please Mamy na k’oshi da abincin nan ki bani tea.”

D’agowa Abba yayi ya kalleshi, still kuma cikin tsare gida yace.

“A’a fa yau sai kacinye abincin nan tas, saboda haka babu wani tea din da za’a baka.”

Maraitattun idanunsa yad’an lumshe, cikin kuma yanayin dake bayyana tsananin biyayyarsa ga mahaifinnasa yace.

“To Abba amma dan Allah abani tea sai in had’a, na tabbata abincin zaifi shiga...”

Yanayin yanda ya k’are maganar yana karyar da wuyansa gefe ne, yasa Abban sakin murmushi, cike da k’aunar d’an nasa yace.

“Shikenan to na yarda ka had’a da tea d’in.”

Jin haka yasa Mamy tashi ta soma kokarin had’a masa tea, kamar yanda ya buk’ata.

Shikuwa Murmushin jin dad’i yayi, saboda dama shi yafison ko yaya idan zaici abinci, ya zamana yana mixing abincin da abu mai zak’i, gashi kuma dama shi.
Sam baya da yawan cin abinci, sometimes idan yaci chocolate d’insa ya d’aura da bootle water, yakanji sa dai-dai.

Had’a masa tea d’in acikin mug Mamy tayi ta mik’o masa, koda ya karb’a bai wuce 3 sipping yayi ba, ya d’ago kansa ahankali ya kalleta.

Cikin yanayi da salon maganarsa yace.
“Ayyah Mamyna sugar baiji ba dai, please ki karamin.”

Idanu Mamy tad’an zaro cikin yanayin mamaki tace.
“Rayyern Shugar 3spoon amma kace baiyi maka ba, kai dai kam shan zak’i ya zama maka jiki.”
Ta kare maganar tana mai k’ara masa Shugar one spoon acikin tea d’in.

Murmushi kawai yayi, batare daya kuma cewa komai ba, ya maida kansa ya cigaba da sipping tea din, sai time to time yake daukan patatoe daya yakai bakinsa, nan ma kuma gudun kada Abba yayi masa fad’a ne.

Saida yasha kusan rabin tea d’in, kafin ya d’ago da kansa ahankali ya kalli Ramadan dake cin abinci.

“Ramadan ya hospital d’in, ina fatan komai yana tafiya dai-dai ko?.”

Ramadan kuwa Jin abunda Hamman nashi ya tambaya ne, yasa shi dakatawa da cin abincin, tare da cewa.

“Alhamdulillah Hamma Rayyern komai yana tafiya yanda ya kamata, bayan wannan tafiyar taka ma Ya Sulaiman yana zuwa, tare mukeyin duk wasu abubuwan da suka dace.”

Idanunsa ya d’an lumshe ahankali tare da jinjina kansa, Tabbas dama yasan koda bayanan, Sulaiman da Ramadan zasu gudanar da komai yanda ya kamata kana ga sauran Doctor's ɗin, kasancewar dukansu Doctors ne way’anda suka san aikinsu, kuma kowannensu da irin k’warewarsa.

Hiran hospital d’in da kuma irin manya manyan ayyukan da sukayi, alokacin da bayanan Ramadan d’in ya shiga yi masa.
Yayinda shi kuwa ahankali yake d’an jinjina kansa, alaman gamsuwa, saboda zuwa yanzu bakinsa ya dan fara gajiya da motsawa.

Abba da tun d’azun ya kafesu da idanu baya ko k’yaftawa, murmushi ne kawai ke bayyane akan fuskarsa.
Yayinda yake yiwa yaran nasa, wani irin kallo mai d’auke da tsananin k’auna had’i da soyayya, Tabbas yanaji aransa cewa yaransa GARKUWA ne, sannan koda bayan ransa da izinin Ubangiji,
Zasu ƙarasa ginin TUBALI’n da aka fara ginasa zasu karasa ida ginasa da yardar Allah, akullum a kuma koda yaushe yana alfahari dasu, Tabbas ako ina zaiyi al'faharin cewa.
Yay’an nasa jajirtattune kuma masu k’wazo, Lallai watarana Tabbas zasu cimmawa abunda suke so yana jin gamsuwa mai tarin yawa na riƙo da amarsu da Allah ya bashi da basu gamsasshiyar tarbiya.

Jin da yayi hirar tasu ta tsaya ne kuma, yasashi Kallon Rayyern tare da cewa.
“Rayyan ya tafiyar taka? Ina fata ansamu abunda akeso ko!?.”

Kai Rayyern d’in ya jinjina tare da bud’e bakinsa anutse yace.

“Alhamdulillah Abba, duk wani abu da muke nema na samu, dama kayan amfanin companies dinmu ne naje sayawo, to kuma ba abunda ban samu ba, nayi ordering Insha Allah kuma soon zasu sauk’a nan Nigeria.”

Kai Abban ya jinjina cike da gamsuwa, kana yace.

“To kaida kaje US kuma sai gaka a ethiopia’n harda karb’an wani kambun karramawa.”

Murmushin daya bayyana fararen haƙoransa yayi, cikin kuma sakewa da mahaifinnasa yace.

“To Abba ai acikin Airport na hadu da yarannasu harna taimaka musu, shine fahimtar likitane Ni yasa dole aka wuce dani k’asarsu,
Jin dadin ceton ahlin masu muƙamin ƙasar ne yasa sukamin wannan karramawar.”

“Masha Allah Allah Ubangiji yaci gaba da taimakawa.”
Abba da Mamy suka had’a baki wajen fad’ar hakan.

Ramadan kuwa daya kammala cin abincinsa, mik’ewa tsaye yayi tare da d’aukan wayarsa dake kan table d’in, cikin kuma yanayin nuna kulawa ga Hamman nasa yace.

“Yauwa Hamma Rayyern bari na amso maka maganin rage zogin ciwo acikin pharmacy d’inmu.”

Kai kawai Rayyern din ya jinjina, Yayinda shi kuma Ramadan yasa kai ya fice daga cikin falon.
Koda ya fito daga cikin gidan nasu direct Mai-Nasara’s Pharmacy Nig LTD ya nufa, kasancewar kuma pharmacy din bashi da wani nisa da gidansu, hakan yasa bai wani b’ata lokaci ba ya dawo.

Shida kansa ya d’auko bottle water marar sanyi, tare da b’are maganin ya bawa Hamman nasa yasha.

Bayan Rayyern din yasha maganin ne kuma, ya mik’e tsaye ahankali tare da kallon su Abban nasa, aladabce yace .
“Abba ni zanje na kwanta, dan inajin gajiya sosai ajikina.”

Kai Abba ya jinjina masa tare da cewa.
“To Allah ya tashemu lafiya.”

Da “Ameen.” Ya amsa kafun yayiwa Mamy da Ramadan saida safe, kana kaitsaye ya nufi sashinsa, da k’ofar shiga cikinta ke Cikin babban falon a nitse yake tattaki bisa steps ɗin haurawa saman.

Ahankali ya murd’a handle d’in had’add’Iyar k’ofar, tare da tura kansa ciki.
Wani irin sassanyan k’amshin room freshener daya shak’ane kuma yasashi lumshe idanunsa, wanda suke d’auke da wani yanayi na musamman.
Tabbas shi mutum ne maitsanin son k’amshi, wannan yasa aduk sanda yaji k’amshi sai zuciyarsa tayi sanyi.

Ahankali ya bud’e idanun nasa, tare da soma bin kekyawan falon da kyawunsa ya zarce tunanin mutum da kallo.
Duk da kuwa cewar babu yawan tarkace acikin falon, amma yanayin tsarin falon da kuma kayan dake cikinsa, na millions din kud’i ne ya ƙawatashi.

Domin kuwa acikin falon wasu irin had’add’un Roma complete sofa’s ne masu masifar kyau da tsada, wanda sukayiwa tsakiyar falon k’awanya, Yayinda aka cika samansu da wasu irin trow pillows new design, babban abu mafi d’aukar hankali ajikin sofas din kuwa shine, yanda aka k’awata su da wani irin abu mai kaman royal glasses, da kuma ado na musamman, kasantuwar design din Golding ash ne kuma, yasa har wani d’auke ido adon sofas d’in keyi.
Yayinda daga k’asan sofas din kuwa aka shumfud’e wani had’add’en Ash colour Austin carpet, mai tsananin taushi da laushi, domin kuwa saboda tsabar laushin carpet d’in, har k’afan mutum kan iya nutsewa idan ya taka.

Yayinda aka d’aura wani had’add’en glass Roma table akan tsakiyar carpet d’in, wanda kuma shine ya k’ara k’awata kyau da had’uwar falon, musamman wasu beautiful roses masu kalan gold da aka d’aura asamansa.
Chapter 14 · 0% Book details