Sashe 66
Tubali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Hajiya ga Jannart nan na kawo muku Amana, Dan Allah ki rikemin ita, ki dauketa tamkar yar da kika haifa acikin cikinki, Dan Allah ku killacemin Jannart, banason ko k’ofar gida ta l’eka, Idan kuma akwai buk’atar fitar ta wanda ya kama da dalili a gayamin, saboda banason idanun wasu su sauk’a akanta.
Domin fataucin rayuwarta sukeyi, tamkar wanda yaje farauta yagaji bai samu komai ba, haka suke ayanzu, da zaran lokaci ya cika akanta zasu dire, suna son su kasheta, suna tsananin son ganin bayanta,
Alhamdulillah yau inajin na sauke wani nauyi akaina...”
Kasa karasa maganan nasa yayi, saboda kukan da yakeji na tasar masa.
Yayinda Jannart kuwa tuni kuka yaci karfinta, ba abunda ke tashi kuwa face sautin kukan ta.
Wanda hakan yasa gaba daya su Abba, Mamy, da Baba Maud’o duk jikinsu yayi sanyi.
Shikuwa Rayyern zuwa yanzu ya tankwashe kafafunsa, tare kuma dayin shiru, ya sunkuyar da kansa k’asa.
Haka kuma yakejin kansa na.
Dan sarawa, Yayinda yakejin jijiyon dake cikin kannsa nayi masa ciwo.
Badon komai ba kuma saidan saboda yanda yakejin kukan yarinyar na hawa kanshi.
Barrister Kabir kuwa Hannun Rayyern din ya kamo.
Da sauri Rayyern ya ɗago kansa ya kalleshi.
Sai kuma yayi ƙasa da ida nunshi ganin yadda mutumin mai girma yana kuka.
Shi kuwa Barrister Kabir.
cikin sanyin da jikinsa yayi yace.
“Rayyern ga amanar diyata matarka”.
Ya ƙare mgnar yana mai ɗago hannun Jannart ya saka acikin tattausan tafin hannun Rayyern din tare dasa nashi hannun ya rumtse tafin hannun Rayyern dake riƙe dana Jannart ya rumtse ya haɗe su...!
*Littafin TUBALI na kuɗine special Group 1k ne ƙaramin group 500 yawan posting ne banbanci su, 0661110170 GTBank AISHA GARKUWA ALIYU sai ki turo min shaidar biyanki ta whatsApp number na 09097853276, in baki da halin turawa ta banki to ki sayi katin MTN ki copy number's din ki turo min ta WhatsApp na*
By
*GARKUWAR FULANI*
Wani irin raunataccen kuka ne ya kwabcewa Jannart cike da rauni shessheƙan kukan yake fitowa, yana ratsa kunnuwansu.
Banda kukan Jannart dake tashi, shiru gaba d’aya falon ya d’auka.
Yayinda Rayyern kuwa ya sunkuyar da kansa k’asa, tare kuma da rumtse idanunsa gam dan jin fatan saman idonsa nata karkarwa.
Domin kuwa adai-dai lokacin da hannun Jannart din ya sauk’a acikin nasa hannun, wani irin harbawa zuciyarshi tayi tare da buɗewa da azaban ƙarfi.
Duk da cewar kuwa ba wannan bane first time nasa daya fara tab’a jikin mace, musamman Idan akayi duba da irin yanayin aikinsa, saidai kuma a iya tsawon rayuwarsa, bai tab’a rik’e jikin mace, da sunan wai dan yaji wani abu ajikinsa ba, yana rikewa ne kawai idan takama dole, enfact ma shi baicika son duba mata ba, sai idan abun yayi worst ya kuma zama lallai dole shidin ake da buk’atar ya duba su.
Sam bai tab’ajin wani abu makamancin haka ba.
Tamkar kuma yanda zuciyar tasa ke bugawa haka ma Jannart, da itama takejin wani irin bugun zuciya, badon komai ba kuwa saidan samun hannunta da tayi acikin nasa, haka kuma Wannan shine karo na farko a rayuwar ta, da wani d’a Namiji wanda bata sani ba kuma ba Muharraminta ba ya tab’a jikinta, domin kuwa Bayan Yah Junaid, Daddy, Abba Kabir, Abdull, sai kuma Dr Lukman wanda ya kasance Dr dinta ne, babu wani wanda ya tab’a kama Koda farcenta ne, sai wannan ayanzu da hannunta yake cikin nasa.
Wanda kuma hakanne yasa taji zuciyarta tayi mata nauyi, Yayinda duk wani rauni dake narke acikin zuciyarta ya sake hauhuwa, lokaci daya taji tamkar wani mafakan kuka ta samu.
Dan tsabar kukan dake cinta har wani seizing numfashinta keyi.
Cikin muryarta da ta dashe sosai, ta saki Sabon kukan da sauti da amonsa ya zarce na baya mai cike da rauni.
Domin ayanzun kuka take da duka zuciya da gangar jikinta, kukan dake bayyana tsananin tarin damuwa da maraicin rayuwarta, kukan dake bayyana rauninta, haka kuma kukan da yasawa kowannensu matsanancin tausayinta.
Musamman Mamy da gaba daya k’walla ya cika mata idanu.
Rayyern kuwa har yanzu idanunsa a rumtse suke, saboda yanda sautin kukan nata ke ratsa cikin kunnuwansa, yasa gaba d’aya yaji kansa na juyawa, Sam bayason wani hayaniya ko kuma yawan koke-koke, kwakwalwarsa bata iya jure hakan.
Abba Kabir kuwa wasu irin hawaye masu zafi ne, suka gangaro daga kan fuskarsa, sake matse hannunsu awaje daya yayi, cikin kuma muryarsa da tayi rauni sosai yace.
“Rayyern ga amanar y’ata Jannart na kawo maka, ayanzu kaine Mijinta majiɓamcin lamuran rayuwata, kaine kuma wanda nakesa ran zaka zame mata Garkuwa, Rayyern Jannart marainiyace, wacce tataso acikin kad’aici da tarin damuwa, Jannart batasan wani farinciki ba Rayyern.
Domin ako da yaushe damuwa da kuma fargaba suke cika zuciyarta, Karikemin amanar Jannart Rayyern, Domin ayanzu duk wani motsinta yana karkashin kulawanka ne da ikonka, Jannart ta rayu akan wata turba ta daban, sannan an tarbiyantar da ita akan biyyya da kuma karb’an umarni akan duk wani abu da aka sata, ko kad’an bani da haufi akan Jannart, Domin kuwa Ina da tabbaci akanta, nasani Jannart bazata tab’a sab’amaka ba Rayyern idan kuma ta saɓa maka to ajizancin ne da yake halittar ɗan Adam.
Dan Allah ka kula da ita, Koda ace bazaka dauketa awani matsa yi na musamman ba, To Ina fatan ka karb’eta amatsayin k’anwarka, Jannart tana buk’atar kulawa Rayyern, tana kuma buk’atar farinciki, saboda ita din Marainiya ce...”
Ya Kai k’arshen maganan cikin muryarsa dake rawa, hadi da alhinin sark’ak’iyar dake cikin rayuwar Jannart din.
Ahankali kuma ya dawo da kallonsa ga Jannart din, cikin matukar sanyin murya da kuma son kwantar mata da hankali yace.
“Jannart ga Mijinki nan, kiyi masa biyayya kamar yanda kika saba, ki kuma gujewa duk wani abu dazai b’ata ransa, Dan Allah Jannart ki kiyaye kinji, Insha Allah watarana zaki samu ingantaccen farinciki, watarana duhu zaiyaye inda haske zai cika cikinsa, ako wani bayan kunci akwai farinciki,sannan ako wani bayan k’addara akwai sauki, komai da muke yi yanzu da kuma wanda zamuyi anan gaba, rubutacce kuma tsararrene, wanda Allah ya tsara mana, babu wata damuwa da zata Tabbata Jannart nasan kinyi imani da hakan.”
D’an tsagaitawa Abba Kabir din yayi, cikin kuma hawaye dake zuba a idanunsa, ya zare hannunsa dake saman nasu, tare da tallafo fuskarta, ya sumbaceta akan goshinta.
“Zan tafi Jannart, ki kula da kanki, kada ki sab’awa kowa dake cikin gidannan, Domin ayanzu sune y’an uwa kuma Garkuwarki.”
Abba Kabir din ya fad’a yana me kokarin mik’ewa tsaye.
Jannart da kuka ya riga daya ci karfinta, saurin rik’o k’afafunsa tayi, tare da sake fashewa da kuka.
Domin hakanan takejin kamar Idan ya tafi bazai dawo ba, tayaya zata iya jure zama amatsayin matar aure?
Hakan wani rayuwane da bata sanshi ba, batasan wacce irin kalubale ne zata fuskanta ba, Tabbas ta sani acikin rayuwarta gaba d’aya duhu ne, ita da batasan menene cikakken fari ciki ba, tayaya zata iya bawa wani?
Rayyern kuwa cikin takaicin kukan nata dake shirin fasa masa kwakwalwa ya zare hannunsa, tare da kawar da kansa gefe, yana mejin tamkar yasa hannayensa ya toshe kunnuwansa ko bakinta.
Abba Kabir kuwa kukan da Jannart din keyi ne ya matuk’ar karyar masa da zuciya.
Ahankali ya d’an sunkuyo, tare da kama kafad’un Jannart din cikin tausasawa hadi da rarrashi yace.
“Jannart din Abba ki daina kuka, tafiyar da zanyi ayanzu bawai yana nufin bazan dawo bane, Lallai Zan dawo Jannart, ki saki ranki ki dauka nan tamkar gidanku ne, kuma suma iyayenki ne, kamar yanda muke kulawa dake haka suma zasu kula dake, ako da yaushe Ina miki fatan al'khairi da nasara Jannart, Allah ya sanya al'barka acikin rayuwar aurenki.”
Cikin matsanancin kukan dake addabarta, ta Dan soma jujjuya Kai.
Ganin hakanne kuma yasa Mamy da ta kasa tsaida ruwan hawayen daya zubo daga cikin idanunta tace.
“Zo Jannart kema y’atace kamar yanda su Rayyern suke yayana, ki daina kuka kinji, Insha Allah zan zame miki mahaifiyar dake share kukan yayanta, ki sa aranki kuma cewar kina tare da mahaifiyarki ce, ki kalleni amatsayin wacce ta haifeki, bawai matsayin suruka ba, ni kuma har abada zan rikeki amatsayin y’a, Domin dama Allah baibani y’a Mace ba,.
To yanzu gashi ya turo min ke amatsayin kyauta biyu, y’ata kuma suruka ta, Insha Allah bazamu bari kiyi kuka ba.”
Mamyn ta fad’a tana me jawo Jannart din jikinta, tare da kwantar da kan Jannart din akan cinyarta.
Hakanne kuma yasa Jannart din, lafewa ajikin Mamyn tana sakin sheshshek’an kuka akai akai.
Abba kuwa da Baba Maud’o duk mik’ewa tsaye sukayi, saboda Ganin Barrister Kabir din da sukayi ya mik’e.
Koda ya soma tafiya, Mara masa baya sukayi, Dan yi masa rakiya.
Suna fita daga cikin falon, kuwa Rayyern da yake jinsa tamkar akan k’aya ya mik’e tsaye, ko kallon inda Jannart din take kuwa baiyi ba, kaitsaye ya haura sama, yana Jin tamkar shi dinma ya fashe da kuka suyi tayi a tare tsabar takaici, haka kawai an takura yarinya.
Tazo da wani shegen kukanta tazo ta saukar masa da ciwon Kai.
Mamy kuwa, hannu tasa ta soma sharewa Jannart din hawayen dake kan fuskarta, wanda kuma saboda tsabar kukan da tayi, har saida idanunta suka zama jajur.
“Kiyi hakuri Jannart, ki daina wannan kukan kinji, haka rayuwar kowacce ya mace yake, Aranar da aka rabata da gidan iyayen ta, saboda haka hakuri zakiyi, da sannu kuma zaki saba da zama damu,
ba amatsayin surukata kawai kike ba, ke y’ata ce.”
Mamyn ta fad’a tana me shafa bayan Jannart din alaman rarrashi.
Saidai kuma duk da haka Jannart din ta kasa tsaida hawayen dake kwaranya daga cikin idanunta, kukan ya riga dayaci karfinta, duk yanda taso tsaida kukan nata ita kanta ta gaza, amma saidai jin kanta da tayi ajikin Mamyn, ya d’ansa zuciyarta tayi sanyi ko yanzu tasan ta samu madadin Mom.
Yayinda Acan waje kuwa har bakin mota Abba da kuma Baba Maud’o suka rako Barrister Kabir.
Ganin yanda shi kansa damuwa ke bayyane akan fuskarsa ne kuma yasa Abba da kansa yace.
Domin fataucin rayuwarta sukeyi, tamkar wanda yaje farauta yagaji bai samu komai ba, haka suke ayanzu, da zaran lokaci ya cika akanta zasu dire, suna son su kasheta, suna tsananin son ganin bayanta,
Alhamdulillah yau inajin na sauke wani nauyi akaina...”
Kasa karasa maganan nasa yayi, saboda kukan da yakeji na tasar masa.
Yayinda Jannart kuwa tuni kuka yaci karfinta, ba abunda ke tashi kuwa face sautin kukan ta.
Wanda hakan yasa gaba daya su Abba, Mamy, da Baba Maud’o duk jikinsu yayi sanyi.
Shikuwa Rayyern zuwa yanzu ya tankwashe kafafunsa, tare kuma dayin shiru, ya sunkuyar da kansa k’asa.
Haka kuma yakejin kansa na.
Dan sarawa, Yayinda yakejin jijiyon dake cikin kannsa nayi masa ciwo.
Badon komai ba kuma saidan saboda yanda yakejin kukan yarinyar na hawa kanshi.
Barrister Kabir kuwa Hannun Rayyern din ya kamo.
Da sauri Rayyern ya ɗago kansa ya kalleshi.
Sai kuma yayi ƙasa da ida nunshi ganin yadda mutumin mai girma yana kuka.
Shi kuwa Barrister Kabir.
cikin sanyin da jikinsa yayi yace.
“Rayyern ga amanar diyata matarka”.
Ya ƙare mgnar yana mai ɗago hannun Jannart ya saka acikin tattausan tafin hannun Rayyern din tare dasa nashi hannun ya rumtse tafin hannun Rayyern dake riƙe dana Jannart ya rumtse ya haɗe su...!
*Littafin TUBALI na kuɗine special Group 1k ne ƙaramin group 500 yawan posting ne banbanci su, 0661110170 GTBank AISHA GARKUWA ALIYU sai ki turo min shaidar biyanki ta whatsApp number na 09097853276, in baki da halin turawa ta banki to ki sayi katin MTN ki copy number's din ki turo min ta WhatsApp na*
By
*GARKUWAR FULANI*
Wani irin raunataccen kuka ne ya kwabcewa Jannart cike da rauni shessheƙan kukan yake fitowa, yana ratsa kunnuwansu.
Banda kukan Jannart dake tashi, shiru gaba d’aya falon ya d’auka.
Yayinda Rayyern kuwa ya sunkuyar da kansa k’asa, tare kuma da rumtse idanunsa gam dan jin fatan saman idonsa nata karkarwa.
Domin kuwa adai-dai lokacin da hannun Jannart din ya sauk’a acikin nasa hannun, wani irin harbawa zuciyarshi tayi tare da buɗewa da azaban ƙarfi.
Duk da cewar kuwa ba wannan bane first time nasa daya fara tab’a jikin mace, musamman Idan akayi duba da irin yanayin aikinsa, saidai kuma a iya tsawon rayuwarsa, bai tab’a rik’e jikin mace, da sunan wai dan yaji wani abu ajikinsa ba, yana rikewa ne kawai idan takama dole, enfact ma shi baicika son duba mata ba, sai idan abun yayi worst ya kuma zama lallai dole shidin ake da buk’atar ya duba su.
Sam bai tab’ajin wani abu makamancin haka ba.
Tamkar kuma yanda zuciyar tasa ke bugawa haka ma Jannart, da itama takejin wani irin bugun zuciya, badon komai ba kuwa saidan samun hannunta da tayi acikin nasa, haka kuma Wannan shine karo na farko a rayuwar ta, da wani d’a Namiji wanda bata sani ba kuma ba Muharraminta ba ya tab’a jikinta, domin kuwa Bayan Yah Junaid, Daddy, Abba Kabir, Abdull, sai kuma Dr Lukman wanda ya kasance Dr dinta ne, babu wani wanda ya tab’a kama Koda farcenta ne, sai wannan ayanzu da hannunta yake cikin nasa.
Wanda kuma hakanne yasa taji zuciyarta tayi mata nauyi, Yayinda duk wani rauni dake narke acikin zuciyarta ya sake hauhuwa, lokaci daya taji tamkar wani mafakan kuka ta samu.
Dan tsabar kukan dake cinta har wani seizing numfashinta keyi.
Cikin muryarta da ta dashe sosai, ta saki Sabon kukan da sauti da amonsa ya zarce na baya mai cike da rauni.
Domin ayanzun kuka take da duka zuciya da gangar jikinta, kukan dake bayyana tsananin tarin damuwa da maraicin rayuwarta, kukan dake bayyana rauninta, haka kuma kukan da yasawa kowannensu matsanancin tausayinta.
Musamman Mamy da gaba daya k’walla ya cika mata idanu.
Rayyern kuwa har yanzu idanunsa a rumtse suke, saboda yanda sautin kukan nata ke ratsa cikin kunnuwansa, yasa gaba d’aya yaji kansa na juyawa, Sam bayason wani hayaniya ko kuma yawan koke-koke, kwakwalwarsa bata iya jure hakan.
Abba Kabir kuwa wasu irin hawaye masu zafi ne, suka gangaro daga kan fuskarsa, sake matse hannunsu awaje daya yayi, cikin kuma muryarsa da tayi rauni sosai yace.
“Rayyern ga amanar y’ata Jannart na kawo maka, ayanzu kaine Mijinta majiɓamcin lamuran rayuwata, kaine kuma wanda nakesa ran zaka zame mata Garkuwa, Rayyern Jannart marainiyace, wacce tataso acikin kad’aici da tarin damuwa, Jannart batasan wani farinciki ba Rayyern.
Domin ako da yaushe damuwa da kuma fargaba suke cika zuciyarta, Karikemin amanar Jannart Rayyern, Domin ayanzu duk wani motsinta yana karkashin kulawanka ne da ikonka, Jannart ta rayu akan wata turba ta daban, sannan an tarbiyantar da ita akan biyyya da kuma karb’an umarni akan duk wani abu da aka sata, ko kad’an bani da haufi akan Jannart, Domin kuwa Ina da tabbaci akanta, nasani Jannart bazata tab’a sab’amaka ba Rayyern idan kuma ta saɓa maka to ajizancin ne da yake halittar ɗan Adam.
Dan Allah ka kula da ita, Koda ace bazaka dauketa awani matsa yi na musamman ba, To Ina fatan ka karb’eta amatsayin k’anwarka, Jannart tana buk’atar kulawa Rayyern, tana kuma buk’atar farinciki, saboda ita din Marainiya ce...”
Ya Kai k’arshen maganan cikin muryarsa dake rawa, hadi da alhinin sark’ak’iyar dake cikin rayuwar Jannart din.
Ahankali kuma ya dawo da kallonsa ga Jannart din, cikin matukar sanyin murya da kuma son kwantar mata da hankali yace.
“Jannart ga Mijinki nan, kiyi masa biyayya kamar yanda kika saba, ki kuma gujewa duk wani abu dazai b’ata ransa, Dan Allah Jannart ki kiyaye kinji, Insha Allah watarana zaki samu ingantaccen farinciki, watarana duhu zaiyaye inda haske zai cika cikinsa, ako wani bayan kunci akwai farinciki,sannan ako wani bayan k’addara akwai sauki, komai da muke yi yanzu da kuma wanda zamuyi anan gaba, rubutacce kuma tsararrene, wanda Allah ya tsara mana, babu wata damuwa da zata Tabbata Jannart nasan kinyi imani da hakan.”
D’an tsagaitawa Abba Kabir din yayi, cikin kuma hawaye dake zuba a idanunsa, ya zare hannunsa dake saman nasu, tare da tallafo fuskarta, ya sumbaceta akan goshinta.
“Zan tafi Jannart, ki kula da kanki, kada ki sab’awa kowa dake cikin gidannan, Domin ayanzu sune y’an uwa kuma Garkuwarki.”
Abba Kabir din ya fad’a yana me kokarin mik’ewa tsaye.
Jannart da kuka ya riga daya ci karfinta, saurin rik’o k’afafunsa tayi, tare da sake fashewa da kuka.
Domin hakanan takejin kamar Idan ya tafi bazai dawo ba, tayaya zata iya jure zama amatsayin matar aure?
Hakan wani rayuwane da bata sanshi ba, batasan wacce irin kalubale ne zata fuskanta ba, Tabbas ta sani acikin rayuwarta gaba d’aya duhu ne, ita da batasan menene cikakken fari ciki ba, tayaya zata iya bawa wani?
Rayyern kuwa cikin takaicin kukan nata dake shirin fasa masa kwakwalwa ya zare hannunsa, tare da kawar da kansa gefe, yana mejin tamkar yasa hannayensa ya toshe kunnuwansa ko bakinta.
Abba Kabir kuwa kukan da Jannart din keyi ne ya matuk’ar karyar masa da zuciya.
Ahankali ya d’an sunkuyo, tare da kama kafad’un Jannart din cikin tausasawa hadi da rarrashi yace.
“Jannart din Abba ki daina kuka, tafiyar da zanyi ayanzu bawai yana nufin bazan dawo bane, Lallai Zan dawo Jannart, ki saki ranki ki dauka nan tamkar gidanku ne, kuma suma iyayenki ne, kamar yanda muke kulawa dake haka suma zasu kula dake, ako da yaushe Ina miki fatan al'khairi da nasara Jannart, Allah ya sanya al'barka acikin rayuwar aurenki.”
Cikin matsanancin kukan dake addabarta, ta Dan soma jujjuya Kai.
Ganin hakanne kuma yasa Mamy da ta kasa tsaida ruwan hawayen daya zubo daga cikin idanunta tace.
“Zo Jannart kema y’atace kamar yanda su Rayyern suke yayana, ki daina kuka kinji, Insha Allah zan zame miki mahaifiyar dake share kukan yayanta, ki sa aranki kuma cewar kina tare da mahaifiyarki ce, ki kalleni amatsayin wacce ta haifeki, bawai matsayin suruka ba, ni kuma har abada zan rikeki amatsayin y’a, Domin dama Allah baibani y’a Mace ba,.
To yanzu gashi ya turo min ke amatsayin kyauta biyu, y’ata kuma suruka ta, Insha Allah bazamu bari kiyi kuka ba.”
Mamyn ta fad’a tana me jawo Jannart din jikinta, tare da kwantar da kan Jannart din akan cinyarta.
Hakanne kuma yasa Jannart din, lafewa ajikin Mamyn tana sakin sheshshek’an kuka akai akai.
Abba kuwa da Baba Maud’o duk mik’ewa tsaye sukayi, saboda Ganin Barrister Kabir din da sukayi ya mik’e.
Koda ya soma tafiya, Mara masa baya sukayi, Dan yi masa rakiya.
Suna fita daga cikin falon, kuwa Rayyern da yake jinsa tamkar akan k’aya ya mik’e tsaye, ko kallon inda Jannart din take kuwa baiyi ba, kaitsaye ya haura sama, yana Jin tamkar shi dinma ya fashe da kuka suyi tayi a tare tsabar takaici, haka kawai an takura yarinya.
Tazo da wani shegen kukanta tazo ta saukar masa da ciwon Kai.
Mamy kuwa, hannu tasa ta soma sharewa Jannart din hawayen dake kan fuskarta, wanda kuma saboda tsabar kukan da tayi, har saida idanunta suka zama jajur.
“Kiyi hakuri Jannart, ki daina wannan kukan kinji, haka rayuwar kowacce ya mace yake, Aranar da aka rabata da gidan iyayen ta, saboda haka hakuri zakiyi, da sannu kuma zaki saba da zama damu,
ba amatsayin surukata kawai kike ba, ke y’ata ce.”
Mamyn ta fad’a tana me shafa bayan Jannart din alaman rarrashi.
Saidai kuma duk da haka Jannart din ta kasa tsaida hawayen dake kwaranya daga cikin idanunta, kukan ya riga dayaci karfinta, duk yanda taso tsaida kukan nata ita kanta ta gaza, amma saidai jin kanta da tayi ajikin Mamyn, ya d’ansa zuciyarta tayi sanyi ko yanzu tasan ta samu madadin Mom.
Yayinda Acan waje kuwa har bakin mota Abba da kuma Baba Maud’o suka rako Barrister Kabir.
Ganin yanda shi kansa damuwa ke bayyane akan fuskarsa ne kuma yasa Abba da kansa yace.