Sashe 51
Tubali Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wanda hakan yasa Ramadan share masa hawayen, cike da tausayawa yace.
“Kayi hakuri kaji Riyyam, Allah yajikansa da Rahama, amma kadaina kuka, addu’a zaka nayi kaji.”
Kai Riyyam-nsra din ya jinjina, kana cikin sanyi yace.
“Insha Allah.”
Ad’an fakaice kuma ya kalli wayarsa da tun dazu take aiki, saboda kiransa da Mammy d’insa tayi, sai kuma ya d’aga ab’oye batare daya fad’awa kowa ba.
Daga can cikin wayar kuwa Mammy duk taji abunda yake faruwa.
Wanda hakan yasa hawayen dake cikin idanunta gangarowa kan fuskarta, haka ma Zaiton dake gefenta, hawayene kwance akan fuskar ta, saboda itama taji abunda akace, Dan Mammyn nasu a hands free ta saka wayar.
Shikuwa Abba har yanzu idanunsa akan Riyyam din yake.
Sake gyara zamansa yayi, tare kuma da duban Riyyam din.
Cikin sanyi da kuma dan bugun zuciyar da yakeji yace.
“Allah ya jiƙanshi da rahma?”
Idanu Riyyam din yadan lumshe, still cikin zubar da hawaye yace.
“Amin Amin. Ameeeeeeen ya rabbil izzati ngd matuƙa da addu'arga.”
Ayanzu kam gaba daya tsananin tausayi da kuma raunin yaronne ya rufe musu zuciya.
Hatta Abba kuwa saida yaji zuciyarsa ta raunana.
Nandai sukayiwa Baban Riyyam din addu’a, bayan sun kammala cin abincinne kuma kowannesu ya watse zuciyarsa cike da tausayin Riyyam-nsra.
To ayau din dai kam gaba daya Riyyam din tare da Ramadan suka wuni har dare kuma suna tare.
Inda washegari laraba ne kuma, Jannart taji saukin jikinta yasa ta shirya zuwa aiki, bayan ta gaya wa Daddyn nata cewa zata biya ta gidan Abba Kabeer.
Daddy kuwa Ganin cewa Jannart din bata da wani ishashshen lafiya sosai ne, yasa bai hana ta zuwa gidan Abba Kabeer dinba.
Jannart din kuwa Koda ta fito daga gidan nasu, kaitsaye gidan Abba Kabir ta nufa.
Koda ta isa gidan tarba maikyau ta samu daga wajen Aunty Dijat, bayan sun gaisa ne kuma.
Aunty Dijat din ta sanar mata cewa.
Abba Kabir din na kiranta.
Akaron farko kenan a iya tsawon rayuwarta, da taji wani abu mai kama da faduwar gaba, saboda Abba Kabir din ya kirata.
Sunan Allah ta soma ambato acikin zuciyarta.
Lokacin da ta isa bakin kofar bedroom din nasa ne kuma tayi knocking daga ciki aka bata izinin shigowa.
Ahankali ta tura kofar dakin ta shiga bakinta dauke da sallama.
Bayan Abba Kabir din ya amsa mata sallaman ne kuma yayi mata alama akan tazo ta zauna.
Babu musu kuwa ta karaso ta zauna agabansa, Yayinda shikuwa yake zaune akan gado.
Koda suka gaisa kuwa Almost 5 minutes haka suka zauna shiru.
Ahankali kuma Barrister Kabir din ya gyara zamansa.
Cikin kuma muryar dake bayyana iya gaskiyarsa, da kuma abunda ke cikin zuciyarsa da alamun umarni yace.
*”Jannart Aurenki ya kusa fa zanyi miki Aure!”*
Ya fadi mgnar cikin serious
Wanda hakan yasa Jannart cikin wani irin yanayi mai rauni.
Da harbawar zuciya cikin sauri Jannart din ta D.......
By
*GARKUWAR FULANI*
D'ago kanta ta kalleshi, da Idanunta wanda lokaci daya yanayin cikinsu ya sauya, musamman yadda maganar da taji ya fito daga bakin Abban ya daki zuciyarta matuka gaya.
Abba Kabir kuwa ganin ta d'ago kanta ne yasa shima ya zuba mata ido, fuskarsa sam babu alaman wasa.
Hakannne kuma yasa ta maida kanta k'asa, tare da d'an lumshe Idanunta, a hankali ta soma wasa da y'an yatsun hannunta.
Yayinda takejin zuciyarta na dan bugawa.
Dai-dai lokacinne kuma Aunty Dijat ta bud'e kofar d'akin ta shigo.
Yanayin yanda tagansuda dinne kuma ya sakata sakin murmushi, tare da karasowa ta zauna akusa da Jannart din.
Kallon Jannart din Aunty Dijat tayi, tare kuma da bud’e bakinta da niyar yin magana.
Ganin hakanne kuma yasa Abba Kabir saurin d’aga mata hannu alamun dakatarwa.
Kallonsa Aunty Dijat din tayi, lokaci guda kuma itama ta sauke kanta k’asa.
Hakanne kuma yasa gaba ki d’aya d’akin ya dauki shiru, babu abunda ke tashi sai sautin fitan numfashi, da kuma ajiyar zuciya da suke ta saukewa dukansu akai akai.
Almost 10mn kafun Abba Kabir din ya sake d’ago Kai ya kalli Jannart, cikin tausayawa da kuma danne abundake cikin zuciyarsa yace.
“Jannart kinji abunda nace, Ina fatan bazaki bijirewa umarnina ba kamar yadda kika al'ƙ’warta min.”
Kai Jannart din ta d’ago Ahankali ta kalli Abban nata.
Domin sai takejin maganganun nasa tamkar wani abu na daban, wanda bata tab’aji ko sanin akwai shiba.
Ita dai tasan kalmar Aure, amma batasan haka kalmar kan zuwarwa mace cikin zuciyarta ba, batasan ya rayuwar cikinsa yake ba.
Saidai koma meye ta sani bazata tab’a bijerewa umarnin Abban nata ba.
Idanunta tasake mayarwa k’asa, kana kuma Cikin sanyi ta jinjina masa Kai, alaman “Eh.”
Ajiyar zuciya mai k’arfi Abba Kabir din ya sauk’e, cikin kuma son sake tabbatarwa kansa amincewarta yace.
“Jannart duk da cewar bani nahaifeki ba, amma matsayin uba nake awajenki, haka kuma Kallon y’ata ta cikina nake miki, wannan yasa bazan tab’a yi miki dole ba, shin kin amince da hukuncin dana yanke akanki?”
Kanta ta sake jinjina masa, tare da bud’e Labb’an bakinta da takejin sun danyi mata nauyi a hankali tace.
“Eh Na amince Abba, duk hukuncin daka yanke akaina dai-dai ne.”
Numfashi Abba Kabir din ya fesar, tare da sake gyara zamansa.
Kana yace.
“Alhamdulillah naji dadi kwarai, Insha Allahu kuma yanzu akwai shirye shiryen da zamu fara, Domin banason lokaci ya ja da yawa.”
Kanta ta d’an langwabar gefe, kana cikin yanayin sanyi tace.
“To Abba, amma akwai abunda nake shiryawa, saboda ranan alhamis dinnan, zanyi wani program, Dan Allah Abba kabani dama, nasamu nayi shirin nan, Idan yaso daga baya komai ma sai ayi.”
D’an murmushi Abba Kabir din yayi, tare da cewa.
“Karki damu Jannart, shirin da nakeyi akannaki ma zaikai har bayan alhamis din, saboda haka kina da ishashshen dama na y’an wasu kwanaki.”
Ajiyar zuciya ta sauk’e, tare da d’an sakin murmushi, saboda yanzu ta danji sanyi acikin ranta, Yayinda ta kuma k’ara samun hope akan cewar Lallai lailai bazata rasa aikinta ba.
Aunty Dijat kuwa Kallon Jannart din tayi, Yayinda takejin tasananin tausayin yarinyar na ratsa zuciyarta.
Lallai Tabbas tasan cewa, Jannart din bata san komai ba, aharkar auratayya sai abunda ta karanta a musulunce, wanda hakan yasa dole tana buk’atar mai taimaka mata.
Sanin wasu abun a zahiriyar rayuwar duniya more Especially aure.
Tasan Jannart cikekkiyar janitalauce, sabida kan haka aka reneta aka bata tarbiya, bin umarnin na gaba da ita, ya zama komai na rayuwarta bata da zabin kanta ko ra'ayinta sai abinda manyan ta suka faɗa, shiyasa suke sarrafa ƙwaƙwalwarta sun hanata yancinta sun dakufeta bata da wani abu sai amsar umarni daga garesu.
Shiyasa ta kasance mai sauƙin kai da rauni kana ga tarin haƙuri.
Wanda suke tasirin hanata tsayuwa kan ra'ayinta.
Hannunta Aunty Dijat din ta rik’o, kana cikin tausasawa tace.
“Naji dadi da kika amincewa maganan auren nan Jannart, Domin kuwa aure shine cikar farinciki dajin dadin rayuwa, acikin aure akwai abubuwa da yawa, farinciki da kuma akasin haka, amma ni naji ajikina cewar auren da zakiyi shine zai zame miki Tubalin farin cikin ki, Rayuwa zata sauya miki Jannart, zaki zamanto Mace mai y’anci, k’uncinki zai gushe, Yayinda haske zai bayyana acikin rayuwarki Insha Allah, sannan kuma ako da yaushe kiyi riko da addu’a, Domin abubuwa sukanyiwa bawa tsanani ne Idan yana wasa da addu’a, Addu’a makamin mumini ne Jannart, musamman gake, da ace bakya sakaci da addu’o’i da ko Junaid da yake yawan musgana miki, bazai tab’a samun daman fuskantar ki ba, saboda Allah zaina baki kariyarsa akoda yaushe.”
Kai Jannart din ta jinjina, cike da gamsuwa da maganganun Aunty Dijat din kuma tace.
“Insha Allah zanna rik’o da addu’o’i, Nagode sosai Aunty Dijat.”
Murmushi Aunty Dijat din tayi, tare kuma da cewa.
“Ba komai Jannart, Allah Ubangiji ya kawo mana saukin damuwarmu.”
Da Ameen suka amsa dukansu, Yayinda Jannart din kuwa ta d’an kalli agogon dake daure a tsintsiyar hannunta, ganin lokaci yaja sosai ne kuma yasata, d’an mikewa tsaye.
Tare da Kallon Abban nata tace.
“Abba zan tafi wajen aiki kada nayi latti.”
Kai Abba Kabir din ya jinjina, had’e kuma da mik’ewa tsaye yace.
“Allah ya kiyaye hanya Jannart ya kuma Kareki aduk inda kike.”
Da Ameen ta amsa, tare kuma da daukar jakarta, ta juya ta fice daga cikin dakin.
Sam bata damu da maganan auren da Abban yace zaiyi mata ba, saboda batasan menene zata tsinta acikinsa ba, wannan yasa ko tambayan wanda sa’a aura mata din da kuma sunansa batayi ba, Ita dai ahar kullum tamkar rak’umi da akala take, duk inda aka jata zuwa zatayi.
Saidai kuma tana da tabbaci cewa Abban nata bazai yi abunda zai cutar da ita ba.
Koda ta fito compound din gidan, kaitsaye wajen motarta ta nufa.
Tana shiga cikin motar kuwa Drivern yaja suka tafi, Yayinda kattin guard dinta suka rufa musu baya.
Kaitsaye hanyar tashar tasu ta Arewa24 suka nufa.
Jin yanda suka mik’i titi ne kuma yasa ta, jingina bayanta da jikin kujerar motar, tare da lumshe Idanunta.
Ahankali ta sauk’e wani irin ajiyar zuciya, Yayinda kalaman Aunty Dijat kuwa suka shiga dawowa cikin kanta filla filla.
“Aure shine cikar farinciki dajin dadin rayuwa, Aure shi zai zame miki tubalin ginuwar farincikin ki.”
Abunda kwakwalwarta ke maimaita mata kenan, wanda kuma har yanzu ta kasa warware kalaman.
Meyasa Aunty Dijat din tace aure zai zame mata tubalin farin ciki? Menene acikinsa? Wacce kalan rayuwa ce zatayi, har kuma ta samu farinciki bayan zata zaune akarkashin wani ne wanda bata saniba bai santaba.
Ya yake irin Yah Junaid da Daddy ne ne ko irin Yah Azeez da Abba? Wai shin menene ma manufar auren nata da Abba bai gaya mataba?
Tayiwa kanta duka way’annan tambayoyin da ko kusa bata da amsarsu, ba kuma ta da mai amsa mata su yanzu.
Batasan komai akan hakan ba, ba ta kuma tab’a tunanin hakan acikin kwakwalwarta ba, shiyasa takejin duk wata kalma da ta shafi aure, amatsayin bak’on abu.
D’an numfasawa tayi, tare da watsar da duk wani tunani dake cikin ranta, dai-dai lokacin kuwa suka iso babban parking space dake cikin tv station din.
Bayan Baba Ado ya gama dai-dai-ta parking din motar ne kuma ta fito, kaitsaye ta nufi cikin gidan tv’ nasu.
“Kayi hakuri kaji Riyyam, Allah yajikansa da Rahama, amma kadaina kuka, addu’a zaka nayi kaji.”
Kai Riyyam-nsra din ya jinjina, kana cikin sanyi yace.
“Insha Allah.”
Ad’an fakaice kuma ya kalli wayarsa da tun dazu take aiki, saboda kiransa da Mammy d’insa tayi, sai kuma ya d’aga ab’oye batare daya fad’awa kowa ba.
Daga can cikin wayar kuwa Mammy duk taji abunda yake faruwa.
Wanda hakan yasa hawayen dake cikin idanunta gangarowa kan fuskarta, haka ma Zaiton dake gefenta, hawayene kwance akan fuskar ta, saboda itama taji abunda akace, Dan Mammyn nasu a hands free ta saka wayar.
Shikuwa Abba har yanzu idanunsa akan Riyyam din yake.
Sake gyara zamansa yayi, tare kuma da duban Riyyam din.
Cikin sanyi da kuma dan bugun zuciyar da yakeji yace.
“Allah ya jiƙanshi da rahma?”
Idanu Riyyam din yadan lumshe, still cikin zubar da hawaye yace.
“Amin Amin. Ameeeeeeen ya rabbil izzati ngd matuƙa da addu'arga.”
Ayanzu kam gaba daya tsananin tausayi da kuma raunin yaronne ya rufe musu zuciya.
Hatta Abba kuwa saida yaji zuciyarsa ta raunana.
Nandai sukayiwa Baban Riyyam din addu’a, bayan sun kammala cin abincinne kuma kowannesu ya watse zuciyarsa cike da tausayin Riyyam-nsra.
To ayau din dai kam gaba daya Riyyam din tare da Ramadan suka wuni har dare kuma suna tare.
Inda washegari laraba ne kuma, Jannart taji saukin jikinta yasa ta shirya zuwa aiki, bayan ta gaya wa Daddyn nata cewa zata biya ta gidan Abba Kabeer.
Daddy kuwa Ganin cewa Jannart din bata da wani ishashshen lafiya sosai ne, yasa bai hana ta zuwa gidan Abba Kabeer dinba.
Jannart din kuwa Koda ta fito daga gidan nasu, kaitsaye gidan Abba Kabir ta nufa.
Koda ta isa gidan tarba maikyau ta samu daga wajen Aunty Dijat, bayan sun gaisa ne kuma.
Aunty Dijat din ta sanar mata cewa.
Abba Kabir din na kiranta.
Akaron farko kenan a iya tsawon rayuwarta, da taji wani abu mai kama da faduwar gaba, saboda Abba Kabir din ya kirata.
Sunan Allah ta soma ambato acikin zuciyarta.
Lokacin da ta isa bakin kofar bedroom din nasa ne kuma tayi knocking daga ciki aka bata izinin shigowa.
Ahankali ta tura kofar dakin ta shiga bakinta dauke da sallama.
Bayan Abba Kabir din ya amsa mata sallaman ne kuma yayi mata alama akan tazo ta zauna.
Babu musu kuwa ta karaso ta zauna agabansa, Yayinda shikuwa yake zaune akan gado.
Koda suka gaisa kuwa Almost 5 minutes haka suka zauna shiru.
Ahankali kuma Barrister Kabir din ya gyara zamansa.
Cikin kuma muryar dake bayyana iya gaskiyarsa, da kuma abunda ke cikin zuciyarsa da alamun umarni yace.
*”Jannart Aurenki ya kusa fa zanyi miki Aure!”*
Ya fadi mgnar cikin serious
Wanda hakan yasa Jannart cikin wani irin yanayi mai rauni.
Da harbawar zuciya cikin sauri Jannart din ta D.......
By
*GARKUWAR FULANI*
D'ago kanta ta kalleshi, da Idanunta wanda lokaci daya yanayin cikinsu ya sauya, musamman yadda maganar da taji ya fito daga bakin Abban ya daki zuciyarta matuka gaya.
Abba Kabir kuwa ganin ta d'ago kanta ne yasa shima ya zuba mata ido, fuskarsa sam babu alaman wasa.
Hakannne kuma yasa ta maida kanta k'asa, tare da d'an lumshe Idanunta, a hankali ta soma wasa da y'an yatsun hannunta.
Yayinda takejin zuciyarta na dan bugawa.
Dai-dai lokacinne kuma Aunty Dijat ta bud'e kofar d'akin ta shigo.
Yanayin yanda tagansuda dinne kuma ya sakata sakin murmushi, tare da karasowa ta zauna akusa da Jannart din.
Kallon Jannart din Aunty Dijat tayi, tare kuma da bud’e bakinta da niyar yin magana.
Ganin hakanne kuma yasa Abba Kabir saurin d’aga mata hannu alamun dakatarwa.
Kallonsa Aunty Dijat din tayi, lokaci guda kuma itama ta sauke kanta k’asa.
Hakanne kuma yasa gaba ki d’aya d’akin ya dauki shiru, babu abunda ke tashi sai sautin fitan numfashi, da kuma ajiyar zuciya da suke ta saukewa dukansu akai akai.
Almost 10mn kafun Abba Kabir din ya sake d’ago Kai ya kalli Jannart, cikin tausayawa da kuma danne abundake cikin zuciyarsa yace.
“Jannart kinji abunda nace, Ina fatan bazaki bijirewa umarnina ba kamar yadda kika al'ƙ’warta min.”
Kai Jannart din ta d’ago Ahankali ta kalli Abban nata.
Domin sai takejin maganganun nasa tamkar wani abu na daban, wanda bata tab’aji ko sanin akwai shiba.
Ita dai tasan kalmar Aure, amma batasan haka kalmar kan zuwarwa mace cikin zuciyarta ba, batasan ya rayuwar cikinsa yake ba.
Saidai koma meye ta sani bazata tab’a bijerewa umarnin Abban nata ba.
Idanunta tasake mayarwa k’asa, kana kuma Cikin sanyi ta jinjina masa Kai, alaman “Eh.”
Ajiyar zuciya mai k’arfi Abba Kabir din ya sauk’e, cikin kuma son sake tabbatarwa kansa amincewarta yace.
“Jannart duk da cewar bani nahaifeki ba, amma matsayin uba nake awajenki, haka kuma Kallon y’ata ta cikina nake miki, wannan yasa bazan tab’a yi miki dole ba, shin kin amince da hukuncin dana yanke akanki?”
Kanta ta sake jinjina masa, tare da bud’e Labb’an bakinta da takejin sun danyi mata nauyi a hankali tace.
“Eh Na amince Abba, duk hukuncin daka yanke akaina dai-dai ne.”
Numfashi Abba Kabir din ya fesar, tare da sake gyara zamansa.
Kana yace.
“Alhamdulillah naji dadi kwarai, Insha Allahu kuma yanzu akwai shirye shiryen da zamu fara, Domin banason lokaci ya ja da yawa.”
Kanta ta d’an langwabar gefe, kana cikin yanayin sanyi tace.
“To Abba, amma akwai abunda nake shiryawa, saboda ranan alhamis dinnan, zanyi wani program, Dan Allah Abba kabani dama, nasamu nayi shirin nan, Idan yaso daga baya komai ma sai ayi.”
D’an murmushi Abba Kabir din yayi, tare da cewa.
“Karki damu Jannart, shirin da nakeyi akannaki ma zaikai har bayan alhamis din, saboda haka kina da ishashshen dama na y’an wasu kwanaki.”
Ajiyar zuciya ta sauk’e, tare da d’an sakin murmushi, saboda yanzu ta danji sanyi acikin ranta, Yayinda ta kuma k’ara samun hope akan cewar Lallai lailai bazata rasa aikinta ba.
Aunty Dijat kuwa Kallon Jannart din tayi, Yayinda takejin tasananin tausayin yarinyar na ratsa zuciyarta.
Lallai Tabbas tasan cewa, Jannart din bata san komai ba, aharkar auratayya sai abunda ta karanta a musulunce, wanda hakan yasa dole tana buk’atar mai taimaka mata.
Sanin wasu abun a zahiriyar rayuwar duniya more Especially aure.
Tasan Jannart cikekkiyar janitalauce, sabida kan haka aka reneta aka bata tarbiya, bin umarnin na gaba da ita, ya zama komai na rayuwarta bata da zabin kanta ko ra'ayinta sai abinda manyan ta suka faɗa, shiyasa suke sarrafa ƙwaƙwalwarta sun hanata yancinta sun dakufeta bata da wani abu sai amsar umarni daga garesu.
Shiyasa ta kasance mai sauƙin kai da rauni kana ga tarin haƙuri.
Wanda suke tasirin hanata tsayuwa kan ra'ayinta.
Hannunta Aunty Dijat din ta rik’o, kana cikin tausasawa tace.
“Naji dadi da kika amincewa maganan auren nan Jannart, Domin kuwa aure shine cikar farinciki dajin dadin rayuwa, acikin aure akwai abubuwa da yawa, farinciki da kuma akasin haka, amma ni naji ajikina cewar auren da zakiyi shine zai zame miki Tubalin farin cikin ki, Rayuwa zata sauya miki Jannart, zaki zamanto Mace mai y’anci, k’uncinki zai gushe, Yayinda haske zai bayyana acikin rayuwarki Insha Allah, sannan kuma ako da yaushe kiyi riko da addu’a, Domin abubuwa sukanyiwa bawa tsanani ne Idan yana wasa da addu’a, Addu’a makamin mumini ne Jannart, musamman gake, da ace bakya sakaci da addu’o’i da ko Junaid da yake yawan musgana miki, bazai tab’a samun daman fuskantar ki ba, saboda Allah zaina baki kariyarsa akoda yaushe.”
Kai Jannart din ta jinjina, cike da gamsuwa da maganganun Aunty Dijat din kuma tace.
“Insha Allah zanna rik’o da addu’o’i, Nagode sosai Aunty Dijat.”
Murmushi Aunty Dijat din tayi, tare kuma da cewa.
“Ba komai Jannart, Allah Ubangiji ya kawo mana saukin damuwarmu.”
Da Ameen suka amsa dukansu, Yayinda Jannart din kuwa ta d’an kalli agogon dake daure a tsintsiyar hannunta, ganin lokaci yaja sosai ne kuma yasata, d’an mikewa tsaye.
Tare da Kallon Abban nata tace.
“Abba zan tafi wajen aiki kada nayi latti.”
Kai Abba Kabir din ya jinjina, had’e kuma da mik’ewa tsaye yace.
“Allah ya kiyaye hanya Jannart ya kuma Kareki aduk inda kike.”
Da Ameen ta amsa, tare kuma da daukar jakarta, ta juya ta fice daga cikin dakin.
Sam bata damu da maganan auren da Abban yace zaiyi mata ba, saboda batasan menene zata tsinta acikinsa ba, wannan yasa ko tambayan wanda sa’a aura mata din da kuma sunansa batayi ba, Ita dai ahar kullum tamkar rak’umi da akala take, duk inda aka jata zuwa zatayi.
Saidai kuma tana da tabbaci cewa Abban nata bazai yi abunda zai cutar da ita ba.
Koda ta fito compound din gidan, kaitsaye wajen motarta ta nufa.
Tana shiga cikin motar kuwa Drivern yaja suka tafi, Yayinda kattin guard dinta suka rufa musu baya.
Kaitsaye hanyar tashar tasu ta Arewa24 suka nufa.
Jin yanda suka mik’i titi ne kuma yasa ta, jingina bayanta da jikin kujerar motar, tare da lumshe Idanunta.
Ahankali ta sauk’e wani irin ajiyar zuciya, Yayinda kalaman Aunty Dijat kuwa suka shiga dawowa cikin kanta filla filla.
“Aure shine cikar farinciki dajin dadin rayuwa, Aure shi zai zame miki tubalin ginuwar farincikin ki.”
Abunda kwakwalwarta ke maimaita mata kenan, wanda kuma har yanzu ta kasa warware kalaman.
Meyasa Aunty Dijat din tace aure zai zame mata tubalin farin ciki? Menene acikinsa? Wacce kalan rayuwa ce zatayi, har kuma ta samu farinciki bayan zata zaune akarkashin wani ne wanda bata saniba bai santaba.
Ya yake irin Yah Junaid da Daddy ne ne ko irin Yah Azeez da Abba? Wai shin menene ma manufar auren nata da Abba bai gaya mataba?
Tayiwa kanta duka way’annan tambayoyin da ko kusa bata da amsarsu, ba kuma ta da mai amsa mata su yanzu.
Batasan komai akan hakan ba, ba ta kuma tab’a tunanin hakan acikin kwakwalwarta ba, shiyasa takejin duk wata kalma da ta shafi aure, amatsayin bak’on abu.
D’an numfasawa tayi, tare da watsar da duk wani tunani dake cikin ranta, dai-dai lokacin kuwa suka iso babban parking space dake cikin tv station din.
Bayan Baba Ado ya gama dai-dai-ta parking din motar ne kuma ta fito, kaitsaye ta nufi cikin gidan tv’ nasu.