Sashe 9
Kaunar Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hamida kan ta a kasa tana auna irin tsabar kiyayyar da ake mata a cikin ahalin ta kamar ba zama tare suka yi da Mufidar cikin cikin mahaifiyar su sannan aka haifo tare har suke rayuwa yau atare ba,ita ce ta zamo bare da ba a san tana raye ba?ko dai ta mace ne da har ba'a lura ba,8 calls daddyn su ya ma fifi ita tana nan tana ta jiran ganin kiran sa sau daya bai kira ba
even after seeing her 3 missed calls bai bi kiran ba sai fifi da ya kira ta har sau takwas..abun yanacin mata rai matuka
Waya ta ji a kunnen ta kuma shine ya ankarar da ita cewa a take muryar daddyn su ta ji yana ce mata
"Hamida ta yaya kuke?kina lura da yar uwanki kuwa? na ga kiran ki har uku amma bana kusa kuma da na dawo na gani sai nayi tunanin tare kuke da yar uwar ki dan haka na kira ta in ya so ita sai ta baki mu gaisa kawai,hamida tace hmmm.yace da fatar kema kina jin dadin gidan su Ammyn naku?murmushi mai ciwo tayi jin wai ashe ya ga missed calls din nata ma, amma bai biyo ta ba sai ya kira wacce ta fiye mai soyuwa a zuciyar sa sannan sai yanzu ne zaina tambayar ta akan jin dadin zaman gidan wanda in da zata sami dama da mutumin da ya cancanta toh da zata samar da shi irin rayuwar da ta fara ginawa a yan awannin da ta tsinci kan ta a ciki a cikin gidan da take ganin tana iya bugun kirji tayi alfahari da shi..
"Daddy komai alhamdulillah"iya kalmar da ya iya fitowa daga bakin ta kenan sai tayi shiru,ko me ya kuma ce mata sai ta mikowa fifi wayar tana tashi daga wurin dan bata muradin jin cigaban hirar tasu..
Sai da ta tabbatar sun gama sannan ta fito da fake face ta fuskanci fifin tana fadin
"So,ya outing din naku ya kasance"?ita kadai ta san karfin halin da tayi kafin tayi tambayar nan,tunanin ta kamar kullum fifi zata hau zayyano mata komai da ya faru ne dalla dalla sai dai yau ta ga akasin hakan
Dan fifi yi tayi kamar bata ji tambayar ba ita ta aiko mata da nata tambayar..
"Hameda meye ne wai ni kam, me ke faruwa da ke ne tun zuwar mu kasar nan?duk yanayin ki ya sauya kamar baki ji dadin tahowar mu ko dan nan kasar batamu bane ko?duk fah fara'ar ki ta dauke baki walwala hamida, baki sakin jikin ki dani na rasa gane maki Hamee
Please dan Allah ki sanar da ni damuwar ki kin ga duk duniyar nan baki da wata wacce zaki iya bayyanawa damuwar ki sama da ni,hamida ta a tare muka taho duniya, duk da ni din ba mai cikakkiyar lafiya ba ce kuma ina iya barin duniyar ma ako wani lokaci,
toh in baki fada min damuwar ki ba ta yaya kike so in taya ki saka farinciki a rayuwar ki, da fuskar ki wanda ba zaki taba mantawa da shi ba ko bayan na bar duniyar uhum?..fifi kamar zata yi kuka haka ta karasa maganar..
Kallon ta Hamida tayi tana jin maganganun yar uwar nata tsanake har yana son yin tasiri a zuciyar ta dan ta san bayan matsalar ciwon nan dake damin ta,inba don aan ware ta ba to da rayuwar su ba a haka zai ginu ba
dan sarai ta san Mufida bata da son kai bata da kyashi,amma wasu lokutan abubuwan dake faruwan be sai take ganin kamar fifin na da son kan ta da yawa wajen janye komai da kowa..
Matsowa fifi tayi ta riko hannuwar ta biyu cikin nata tana kallon cikin idanun ta hade da kuma yi mata tambayar
"Ko dai nan dakin bai maki bane mu yi musayar daki ke ki koma wancan nawa ni in dawo nan"?
kallon ta Hamida ta cigaba da yi kafin ta cire hannun ta cikin na Mufida ta mike tsaye tana fadin
"A'a fifi na,ko daya cikin tambayoyin ki babu wanda ke dami na,yanzu ki zo mu je mu ci abinci dan kin ga sai da daddy ya kuma min gargadin kar in rinka barin ki da yunwa in kular masa da ke,so mis Khadijah Mufida Mande can we go for our dinner now"?
sunan da ta kira ta da shi ne ya saka ta murmusawa dan da sigar tsokana ta fadi sunan..
Fifi Tana son sanar da mufida sirrin zuciyar ta game da Khalid amma sai ta ga kamar lokaci baiyi ba,gani take zai fi in ta bari abin ya kara karfi sai ta fadawa yar uwar nata...
Tare suka fito suna dan hira kadan kadan har suka karaso main parlor suka nufi dinning table..
Hajja ce ta fara ankara da Hamida sai ta dafe kai cikin jimami tana fadin
"Hamida kina gidan nan amma aka yi ta sha'ani amma baki fito an yi da ke ba kuma baki aiko kowa ya kawo maki abincin rana ba?ni dai bani son irin wannan dabi'ar taki da kika dauko ta turawa a ce mutum na cikin ahalin sa amma yana jan jiki da su kamar ba shine nasu ba"?kasa karasa zaman Hamida tayi ta tsaya a tsaye tana kallon Hajja har ta gama maganar ta sannan Ammy ta dora nata..
"Hajja ni wallahi mantawa nayi da ita da na aika mata da nata dazu, kin san sam yaran nan na zamani ba cika son takurawa rayuwar su suke son ana yi ba kin ga bai dace ana yawan shiga harkar su ba"!
kamewa Hamida tayi a tsaye tana nazarin zantukar nasu,da kamar ta juya ta koma amma sai ta ji hannun fifi a kan hannun ta da ta saka ta janyo kujera da niyar zama amma ta kasa...
Kallon ta tayi sai ta ga ita murmushi ma take yi dan haka sai ta fasa komawar kawai ta zauna ba tare da ta ce kala ma maganganun su ba..
Serving din su abincin Ammy tayi suka zazzauna har sun fara ci sannan Khalid ya zo shima yayi joining din su saidai duk hankalin sa akan fifi ita kdai yake,bayan ita kuma Hamida hankalin ta akan shi yake tana mai ambaton kaunar sa a ran ta..
Abubuwa kala kala sun faru a gun cin abincin sai dai duk ba a sako Hamida ciki ba sai ita fifi,dannewa Hamida ta rinka yi har aka kammala cin abincin ta mike tana masu sai da safe,bata jira amsar su ba tayi gaba dan ta san kara mata damuwa zasu yi..
Ammy ce ta bi ta da kallo kamar ta so dago wani abu game da hamida karar da fifi ta saki ne ya sa tayi saurin maida hankalin ta ga tana tambayar ta lafiya..
Ashe spoon Khalid ya saka cikin abincin ta ya dauke mata last sliced of cucumber din dake cikin abincin shine ta sake kara dan har ya kai baki zai saka..
Fada Ammy ta mai akan yana babba amma madadin ya faranta mata a matsayin ta na kanwar sa shine yake kuma tsokanarta...
Hajja kuwa ta kasa hakura da dabi'ar Hamida dan tayi ma abun bahaguwar fahimta gani take hamida miskila ce marar saurin sabo..
Tace "Wannan yarinya dai dabi'ar ta daban take,ana zaune ana hira amma ta tashi ta wuce ciki anya bata da wata damuwa kuwa?karasa tambayar tayi tana kallon Ammy..
Dage kafada Ammyn tayi alamar oho bata sani ba,daga haka suka maida hankalin su ga shirmen Mufida da Khalid har suna tambayar ta ina take son zuwa gobe dan bude ido..
Kasancewar bata san ko ina ba sai Khalid ya rinka zayyano mata wuraren bude ido da daukar hankali,daga nan ta rinka zabar inda zata kai ziyarar a washegarin..
A haka dai suka karasa hirar ta sallame su akan zata koma ta kwanta dan kan ta ya fara ciwo,ai jin kalmar ciwon nan ya sa suka daga hankulan su har abin ya ba fifi tausayi dan ta san duk son da suke mata da kaunar da suke mata dole watan wata rana haka zata mutu ta bar masu duniyar..
Rungume su tayi tana furta masu kalaman so da kauna hade da godiyar kulawar su akan ta,sannan ta wuce su suma suka wuce zuwa makwamcin su..
Anan ma Bata tafi dakin direct ba sai da ta fara duba dkin Hamida ta zauna tare da ita ta rinka jan ta da hira mai ban dariya sannan ta bata sassanyar runguma dacewa kar ta manta in tana da damuwa ko tana jin tana bukatar shawara kar tayi kasa a gwiwa wurin sanar da ita ita kuma ta mata alkawarin bata dukkan lokacin ta da hankalin ta dan ganin ta taya ta magance damuwar ta..
Da haka suka rabu Hamida na ta nazarin kalaman yar uwar nata,taji dama dama sosai kamar dai ta dauka tayi amfani da shi,can sai kuma ta fasa dan karfin kiyayyar da take ma yar uwar nata kamar ya fara rinjayar karfin soyayyar da take mata..
kuma ko ba dan haka ba tasan ita ba zata taba zuba ido ta rasa Khalid ba,tace makanta enough is enough fifi,fifi,fifi,kowa fifi toh abin ya isa haka
Anan ko da ace mutum daya ne zai saurare ta tasaka aranta Khalid ne.
Da Hakan zai fiye mata kallon su da saurarar irin kalar son da suke ma Mufida..
A fannin fifi kuwa kasa runtsawa tayi har sai da ta karema hotunan da suka yi tare da Khalid kallo,ta kalli hotunan nan sun fi a kirga sannan daga bisani ta kashe bed side lamp din dakin ta runtse idanun ta tana me sa kan ta baccin dole dan ba baccin take ji ba ta fi jin kamar begen Khalid ne ya fi dacewa da ta yi a daren ba bacci ba shi ya sa ta runtse idanun dan dole koda bacci zai sace ta in ya so ko a mafarki ne ta lazumci begen sa..
#Mamuh*_Mamuhgee_*
Da sassafe Hamida ta tashi ta bar sashen ta ta nufi
sashen Mufida dan aiwatar da wata kudiri da zuciyar ta tayi ta ayyana mata akan ta aiwatar da zarar ta farka daga bacci..
even after seeing her 3 missed calls bai bi kiran ba sai fifi da ya kira ta har sau takwas..abun yanacin mata rai matuka
Waya ta ji a kunnen ta kuma shine ya ankarar da ita cewa a take muryar daddyn su ta ji yana ce mata
"Hamida ta yaya kuke?kina lura da yar uwanki kuwa? na ga kiran ki har uku amma bana kusa kuma da na dawo na gani sai nayi tunanin tare kuke da yar uwar ki dan haka na kira ta in ya so ita sai ta baki mu gaisa kawai,hamida tace hmmm.yace da fatar kema kina jin dadin gidan su Ammyn naku?murmushi mai ciwo tayi jin wai ashe ya ga missed calls din nata ma, amma bai biyo ta ba sai ya kira wacce ta fiye mai soyuwa a zuciyar sa sannan sai yanzu ne zaina tambayar ta akan jin dadin zaman gidan wanda in da zata sami dama da mutumin da ya cancanta toh da zata samar da shi irin rayuwar da ta fara ginawa a yan awannin da ta tsinci kan ta a ciki a cikin gidan da take ganin tana iya bugun kirji tayi alfahari da shi..
"Daddy komai alhamdulillah"iya kalmar da ya iya fitowa daga bakin ta kenan sai tayi shiru,ko me ya kuma ce mata sai ta mikowa fifi wayar tana tashi daga wurin dan bata muradin jin cigaban hirar tasu..
Sai da ta tabbatar sun gama sannan ta fito da fake face ta fuskanci fifin tana fadin
"So,ya outing din naku ya kasance"?ita kadai ta san karfin halin da tayi kafin tayi tambayar nan,tunanin ta kamar kullum fifi zata hau zayyano mata komai da ya faru ne dalla dalla sai dai yau ta ga akasin hakan
Dan fifi yi tayi kamar bata ji tambayar ba ita ta aiko mata da nata tambayar..
"Hameda meye ne wai ni kam, me ke faruwa da ke ne tun zuwar mu kasar nan?duk yanayin ki ya sauya kamar baki ji dadin tahowar mu ko dan nan kasar batamu bane ko?duk fah fara'ar ki ta dauke baki walwala hamida, baki sakin jikin ki dani na rasa gane maki Hamee
Please dan Allah ki sanar da ni damuwar ki kin ga duk duniyar nan baki da wata wacce zaki iya bayyanawa damuwar ki sama da ni,hamida ta a tare muka taho duniya, duk da ni din ba mai cikakkiyar lafiya ba ce kuma ina iya barin duniyar ma ako wani lokaci,
toh in baki fada min damuwar ki ba ta yaya kike so in taya ki saka farinciki a rayuwar ki, da fuskar ki wanda ba zaki taba mantawa da shi ba ko bayan na bar duniyar uhum?..fifi kamar zata yi kuka haka ta karasa maganar..
Kallon ta Hamida tayi tana jin maganganun yar uwar nata tsanake har yana son yin tasiri a zuciyar ta dan ta san bayan matsalar ciwon nan dake damin ta,inba don aan ware ta ba to da rayuwar su ba a haka zai ginu ba
dan sarai ta san Mufida bata da son kai bata da kyashi,amma wasu lokutan abubuwan dake faruwan be sai take ganin kamar fifin na da son kan ta da yawa wajen janye komai da kowa..
Matsowa fifi tayi ta riko hannuwar ta biyu cikin nata tana kallon cikin idanun ta hade da kuma yi mata tambayar
"Ko dai nan dakin bai maki bane mu yi musayar daki ke ki koma wancan nawa ni in dawo nan"?
kallon ta Hamida ta cigaba da yi kafin ta cire hannun ta cikin na Mufida ta mike tsaye tana fadin
"A'a fifi na,ko daya cikin tambayoyin ki babu wanda ke dami na,yanzu ki zo mu je mu ci abinci dan kin ga sai da daddy ya kuma min gargadin kar in rinka barin ki da yunwa in kular masa da ke,so mis Khadijah Mufida Mande can we go for our dinner now"?
sunan da ta kira ta da shi ne ya saka ta murmusawa dan da sigar tsokana ta fadi sunan..
Fifi Tana son sanar da mufida sirrin zuciyar ta game da Khalid amma sai ta ga kamar lokaci baiyi ba,gani take zai fi in ta bari abin ya kara karfi sai ta fadawa yar uwar nata...
Tare suka fito suna dan hira kadan kadan har suka karaso main parlor suka nufi dinning table..
Hajja ce ta fara ankara da Hamida sai ta dafe kai cikin jimami tana fadin
"Hamida kina gidan nan amma aka yi ta sha'ani amma baki fito an yi da ke ba kuma baki aiko kowa ya kawo maki abincin rana ba?ni dai bani son irin wannan dabi'ar taki da kika dauko ta turawa a ce mutum na cikin ahalin sa amma yana jan jiki da su kamar ba shine nasu ba"?kasa karasa zaman Hamida tayi ta tsaya a tsaye tana kallon Hajja har ta gama maganar ta sannan Ammy ta dora nata..
"Hajja ni wallahi mantawa nayi da ita da na aika mata da nata dazu, kin san sam yaran nan na zamani ba cika son takurawa rayuwar su suke son ana yi ba kin ga bai dace ana yawan shiga harkar su ba"!
kamewa Hamida tayi a tsaye tana nazarin zantukar nasu,da kamar ta juya ta koma amma sai ta ji hannun fifi a kan hannun ta da ta saka ta janyo kujera da niyar zama amma ta kasa...
Kallon ta tayi sai ta ga ita murmushi ma take yi dan haka sai ta fasa komawar kawai ta zauna ba tare da ta ce kala ma maganganun su ba..
Serving din su abincin Ammy tayi suka zazzauna har sun fara ci sannan Khalid ya zo shima yayi joining din su saidai duk hankalin sa akan fifi ita kdai yake,bayan ita kuma Hamida hankalin ta akan shi yake tana mai ambaton kaunar sa a ran ta..
Abubuwa kala kala sun faru a gun cin abincin sai dai duk ba a sako Hamida ciki ba sai ita fifi,dannewa Hamida ta rinka yi har aka kammala cin abincin ta mike tana masu sai da safe,bata jira amsar su ba tayi gaba dan ta san kara mata damuwa zasu yi..
Ammy ce ta bi ta da kallo kamar ta so dago wani abu game da hamida karar da fifi ta saki ne ya sa tayi saurin maida hankalin ta ga tana tambayar ta lafiya..
Ashe spoon Khalid ya saka cikin abincin ta ya dauke mata last sliced of cucumber din dake cikin abincin shine ta sake kara dan har ya kai baki zai saka..
Fada Ammy ta mai akan yana babba amma madadin ya faranta mata a matsayin ta na kanwar sa shine yake kuma tsokanarta...
Hajja kuwa ta kasa hakura da dabi'ar Hamida dan tayi ma abun bahaguwar fahimta gani take hamida miskila ce marar saurin sabo..
Tace "Wannan yarinya dai dabi'ar ta daban take,ana zaune ana hira amma ta tashi ta wuce ciki anya bata da wata damuwa kuwa?karasa tambayar tayi tana kallon Ammy..
Dage kafada Ammyn tayi alamar oho bata sani ba,daga haka suka maida hankalin su ga shirmen Mufida da Khalid har suna tambayar ta ina take son zuwa gobe dan bude ido..
Kasancewar bata san ko ina ba sai Khalid ya rinka zayyano mata wuraren bude ido da daukar hankali,daga nan ta rinka zabar inda zata kai ziyarar a washegarin..
A haka dai suka karasa hirar ta sallame su akan zata koma ta kwanta dan kan ta ya fara ciwo,ai jin kalmar ciwon nan ya sa suka daga hankulan su har abin ya ba fifi tausayi dan ta san duk son da suke mata da kaunar da suke mata dole watan wata rana haka zata mutu ta bar masu duniyar..
Rungume su tayi tana furta masu kalaman so da kauna hade da godiyar kulawar su akan ta,sannan ta wuce su suma suka wuce zuwa makwamcin su..
Anan ma Bata tafi dakin direct ba sai da ta fara duba dkin Hamida ta zauna tare da ita ta rinka jan ta da hira mai ban dariya sannan ta bata sassanyar runguma dacewa kar ta manta in tana da damuwa ko tana jin tana bukatar shawara kar tayi kasa a gwiwa wurin sanar da ita ita kuma ta mata alkawarin bata dukkan lokacin ta da hankalin ta dan ganin ta taya ta magance damuwar ta..
Da haka suka rabu Hamida na ta nazarin kalaman yar uwar nata,taji dama dama sosai kamar dai ta dauka tayi amfani da shi,can sai kuma ta fasa dan karfin kiyayyar da take ma yar uwar nata kamar ya fara rinjayar karfin soyayyar da take mata..
kuma ko ba dan haka ba tasan ita ba zata taba zuba ido ta rasa Khalid ba,tace makanta enough is enough fifi,fifi,fifi,kowa fifi toh abin ya isa haka
Anan ko da ace mutum daya ne zai saurare ta tasaka aranta Khalid ne.
Da Hakan zai fiye mata kallon su da saurarar irin kalar son da suke ma Mufida..
A fannin fifi kuwa kasa runtsawa tayi har sai da ta karema hotunan da suka yi tare da Khalid kallo,ta kalli hotunan nan sun fi a kirga sannan daga bisani ta kashe bed side lamp din dakin ta runtse idanun ta tana me sa kan ta baccin dole dan ba baccin take ji ba ta fi jin kamar begen Khalid ne ya fi dacewa da ta yi a daren ba bacci ba shi ya sa ta runtse idanun dan dole koda bacci zai sace ta in ya so ko a mafarki ne ta lazumci begen sa..
#Mamuh*_Mamuhgee_*
Da sassafe Hamida ta tashi ta bar sashen ta ta nufi
sashen Mufida dan aiwatar da wata kudiri da zuciyar ta tayi ta ayyana mata akan ta aiwatar da zarar ta farka daga bacci..