Sashe 85
Asanadin Makwabtaka Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ki kawo cups ko" Haisam ya ya fad'a, tana juyawa ya mik'e ya fara kokarin matsar masu da c-table don a hannun kujerun ta d'aura ma kowa, gwaggo na ganin hakan ta mik'e tace ba sai ya wahala ba tafiya zasu yi ma hakan yasashi dakatawa, Fatuu na ganin sun miken ta dawo ba tare da ta dauko kofunan ba, ganin duk basu d'auki lemun da ruwan ba yasa tace" Gwaggo kin bar lemunki da ruwa fa" banza tayi mata ta fice Haisam yace ta d'aukar masu,
tace "to nima in d'aukko" yana niyyar fita yace "wani ya hanaki ne" daga haka yabi bayansu, daukowa tayi itama ta zubasu acikin hijabin jikinta daga haka itama tabi bayansu niki niki da abu rungume, bayan sun fito gwaggo tace mashi don Allah ya koma don part d'in hajiya zasu je, sallama yay masu suka shiga k'ara yi mashi godiya ya juya kawae Fatuu na cewa "saida safe Ya Handsome" ya d'aga mata hannu daga haka ya shige, itama dai hajiyar godiya sukai mata tace ita batama san anyi ba ai, sosae gwaggo ta shiga mamakin hali irin na haisam wannan shine kyauta da dama ba tare da hagu ta sani ba, masu yi don Allah kenan, yar hira suka ta6a kafin suka yi sallama da ita suka koma gida, bayan sun koma ne suka shiga kiciniyar bud'e sabuwar freezer din don su had'a ta, a cikin d'an ginin d'akin da ba'a k'arasa ba dake gefen na gwaggo suka yanke shawarar ajeta don ta rinka samun isashshiyar iska amman sai anyi mata yar baranda asama saboda rana wannan kuma duk sai gobe in Allah ya kaimu suka yanke shawarar za'ai hakan.
Ana saura kwana ukku a fara Azumi ranar laraba kwatsam sai ga Mahaifin Fatuu yayi masu zuwan bazata, wannan ne zuwanshi na biyu tun bayan da ta dawo nan ba kuma don baison zuwa ba sai don kunya da kawaici irin na Fulani, da farko lokacin data dawo ya fara turo masu kudi akai akai gwaggo ta dakatar dashi tace bata d'auki Fatuu don yaci gaba da kula da ita ba, d'aukar d'awainiyarta bazai gagareta ba in sha Allah, sosae yaji dad'i amman duk da hakan lokaci bayan lokaci yana masu aike ta hanyar yan garinsu dake zuwa manyan kasuwannin yankin Katsina tunda shi yanzu ya daina zuwa sai dae k'annanshi da y'ay'an yan'uwanshi, haka kuma yana yawan yin waya da fatun don ko bai kiraba ita tasa gwaggo ko kawu Amadu wani ya kira mata shi, Mahaifi mai dadi (Allah ka jikan namu da suka rasu, Amin), Jama'a kuzo kuga Murna agun Fatuu duk tabi ta kankameshi shidae sai dariya yake, fari dashi mai kyau har yafi Fatuu fari saidai daka kalli fuskarshi zaka ga kamanninshi da Fatun yayi shigar dogayen kayan yadi mai kyau kanshi sanye da hula tsaf tsaf dashi kaman ba daga k'auye yake ba, amman daka ganshi kaga cikakken bafullatani, A d'akin Amadu aka sauke shi fatuu sai faman tambayoyi take mashi tana tambayar yan'uwanta yana bata amsa da muryarshi mai sanyi daga ji baida hayaniya kuma ya iya hausa sosae don Fatun da hausa take mashi Magana koda yayi mata da fullanci amman sam basuyi hausa ba da gwaggo da ta shigo don su k'ara gaisawa, sam Fatuu tak'i barinshi ya huta yaci abinci sosae, tunda ta kawo mashi ta tasashi gaba tana ta bashi labarin Ya Handsome da duk Alkhairan da yake masu kuma har labarin yadda akai suka saba dashi saida ta bashi wanda ko gwaggo batasani ba har yake cewa ashe har yanzu baki daina rashin ji ba inna wuro (sunan da yake kiranta dashi kenan wato uwar masu gida don sunan Mahaifiyarshi ne aka sanya mata), rantsuwa ta hau yi mashi kan ta daina rashin ji kuma ma ya tambayi gwaggo, atare suka ci abincin gwanin burgewa har abaki take bashi, bayan sun gama ya d'an kishingida don ya huta ita kuma tace mashi zataje ta dawo, kopar gida ta nufa wurin kawu Amadu don tunda yaje suka gaisa ya dawo shagon, rok'onshi tayi wai ya kira mata Ya Handsome yace bai kira, Magiya ta fara yi mashi ta hanashi sakat har saida ya kira mata shi, cikin murna ko gaidashi bata yi ba ta sanar dashi Babanta yazo tana ta faman dariya, cemata yay yana tayata murna in ya dawo zaizo su gaisa tace mashi to,
Bayan sallar la'asar yazo gidan yana sanye cikin jeans da t-shirt gaba dayansu navy blue ne, hannunshi sanye da agogo bak'a hakama takalmanshi bakake ne sai sakin kayataccen kamshi yake, Amadu ya shigar dashi wurin Baban Fatun lokacin tana like dashi sai faman zuba take mashi ko islamiyya tace bata zuwa, bayan Amadu ya shigo ya sanar mashi cewa zasu gaisa da bako ya juya waje yace ma Haisam ya shigo, fatuu na jin muryarshi yayi yar sallama ta wani zabura ta tashi zaune, ganin shine da gaske yasa ta washe baki tace ma babanta to ga Ya Handsome d'in da take bashi labari nan, ganin ba abun zama yasa Amadu cewa bari ya d'aukko mashi kujera acikin gida haisam yace ya barshi, d'an duk'awa yayi suka gaisa cike da mutuntawa anan yake mashi godiya yace inna wuro ta fad'i mashi abun arzikin da yake masu, to shi d'inma dai cemashi yay ba wani abu, daga haka shiru ta biyo baya don gaba d'ayansu ba gwanayen Magana bane kai kace bashi ne Mahaifin Fatuu ba ta wannan fannin, muryarta kawai ake ji sai zuba take tana zuba uwar shagwa6a da shirme kala kala kanta na akan kafafunshi,
" Baffa na gaya maka Ya Handsome dinnan yana da motoci, in kana so sai ya kaika kaga garin nan" Fatuu ta fad'a,shiru baice mata komai ba hakan yasa ta d'aga idanunta tana kallonshi tace "ko baka son ganin garinne?",
fuskarshi da fara'a yana kallonta cikin harshen fulatanci yace mata ai ba dad'ewa zaiyi ba gobe da safe zai tafi, tana jin hakan ta fara bori tana tittirza k'afa akan katifar cike da shagwa6a tace " kai da ka dad'e baka zo ba kuma sai kace wai gobe zaka tafi, ni dai ban yarda ba Allah kwan",
Still Haisam yay yana kallonsu fuskarshi a sake shi kuma mahaifin nata sai murmushi yake da gani dai yana da fara'a sosae, ganin yadda take ta zuba shagwa6a ne yasashi cemata yaso zuwa tuni Ardo ne yay jinya shiyasa bai zo ba kuma har yanzu bai idasa warwarewa ba shiyasa bazai zauna ba don shi ke kula da harkokinshi da yawa acan, da bud'ar bakinta sai cewa tayi " Allah yasa ma ciwon mutuwa ne yakeyi kowa ya huta da masifa " tana yin Maganar suka had'a ido da haisam ya d'an harareta shi kuma baban nata kama kunnanta guda yay ya d'an ja ta saki yar k'ara tana fad'in " wad' muyal baffa, ba ya tsufa ba",
murmushi Haisam ya danyi kafin ya mik'e yay mashi sallama ganin yana kokarin tashi shima yace yay zaman shi da mota yake zai wuce ne, mik'ewa Fatuu tayi tana sanye da riga da skirt na shadda kanta ba kallabi tace ma babanta bari ita ta raka shi waje yanzu zata dawo,
Haisam da har ya nufi mota ya juyo sakamakon kiran sunanshi da tayi, tsayawa yayi ta k'araso tana ta dariya ta kasa ce mashi komae,
" U'r Happy Dad yazo ko" jinjina mashi kai tayi sai kuma ta kwa6e fuska tace " bacin ma wai gobe da safe zai tafi",
" yana da uzuri ne" ya fad'a yana kokarin juyawa,
" gida zaka koma?" ta tambayeshi, kai ya girgiza alamar a'a,
" To ina zaka?"
"Gym" ya bata amsa yana nufar mota,
" ko in zo in raka ka?" sai lokacin ya tsaya yay mata wani kallo ta kyalkyace da dariya,
" ina Aunty Anah?" ta tambayeshi bayan ta daina dariyar,
" tana tambayarki" ya bata amsa a takaice,
" wayyo, don Allah zaka k'ara kaini in ganta, wllh tana da kirki",
girgiza mata kai yay alamar a'a aikuwa ta fara d'an bubbuga kafa tana jujjuya kai, kai kawai ya d'an girgiza ya kai hannu ya bud'e motar ya shiga kafarshi guda awaje, ganin tak'i daina abunda take yasa yay mata alamar tazo da hannunshi, sealed Popcorn da tuwon madara ya mik'o mata ta amsa sai kuma cewa tayi "Ya Handsome na gane wayonka, ina yi maka rigima shine kaban wad'annan abubuwan don inyi shiru ka maida ni karamar yarinya ko",
d'an cije peach lip dinsa na kasa yay da alama ta kashe shi da mamaki, murya can kasa ya furta "kinsan ma rigima ne kike man ko Zarah?" jin haka yasa ta 6oye a gefen motar tana dariya, d'an leko da kanshi yay ya kalleta aikuwa da sauri ta kife fuskar, girgiza kai yay yace "ki koma kin bar dad shi kadae" yana fad'in hakan ya maida kafarshi ciki ta lek'a kanta tana kallonshi yay mata alamar taje da hannu, har saida ya tashi motar ya tafi tana ta d'aga mashi hannu, lokacin data koma cikin d'akin kawu Amadu Babanta har yayi bacci, bawan Allah tun karfe hudu na asuba ya taho ya sauka a Kano kafin ya hau motar Katsina, ya kwaso gajiya don akwae nisa tsakanin Katsina da Yola kusan fin awa goma yana hanya yazo kuma ta hanashi hutawa, Allah yaso yan hankali sunzo mata ta kyaleshi ta nufi cikin gida, tare suka ci abunda haisam ya bata da gwaggo amman fa sai da ta rage ma Baffanta, da daddare aka aiketa gidan hajiya ta kai mata tsaraba ananne tasan baban nata yazo tace ta tayata murna in Allah ya kaimu sa gaisa dashi, bayan ta dawo rigima tasa wai awurinshi zata kwana dole saidai Amadu ya tafi dakinta ya kwana,
tace "to nima in d'aukko" yana niyyar fita yace "wani ya hanaki ne" daga haka yabi bayansu, daukowa tayi itama ta zubasu acikin hijabin jikinta daga haka itama tabi bayansu niki niki da abu rungume, bayan sun fito gwaggo tace mashi don Allah ya koma don part d'in hajiya zasu je, sallama yay masu suka shiga k'ara yi mashi godiya ya juya kawae Fatuu na cewa "saida safe Ya Handsome" ya d'aga mata hannu daga haka ya shige, itama dai hajiyar godiya sukai mata tace ita batama san anyi ba ai, sosae gwaggo ta shiga mamakin hali irin na haisam wannan shine kyauta da dama ba tare da hagu ta sani ba, masu yi don Allah kenan, yar hira suka ta6a kafin suka yi sallama da ita suka koma gida, bayan sun koma ne suka shiga kiciniyar bud'e sabuwar freezer din don su had'a ta, a cikin d'an ginin d'akin da ba'a k'arasa ba dake gefen na gwaggo suka yanke shawarar ajeta don ta rinka samun isashshiyar iska amman sai anyi mata yar baranda asama saboda rana wannan kuma duk sai gobe in Allah ya kaimu suka yanke shawarar za'ai hakan.
Ana saura kwana ukku a fara Azumi ranar laraba kwatsam sai ga Mahaifin Fatuu yayi masu zuwan bazata, wannan ne zuwanshi na biyu tun bayan da ta dawo nan ba kuma don baison zuwa ba sai don kunya da kawaici irin na Fulani, da farko lokacin data dawo ya fara turo masu kudi akai akai gwaggo ta dakatar dashi tace bata d'auki Fatuu don yaci gaba da kula da ita ba, d'aukar d'awainiyarta bazai gagareta ba in sha Allah, sosae yaji dad'i amman duk da hakan lokaci bayan lokaci yana masu aike ta hanyar yan garinsu dake zuwa manyan kasuwannin yankin Katsina tunda shi yanzu ya daina zuwa sai dae k'annanshi da y'ay'an yan'uwanshi, haka kuma yana yawan yin waya da fatun don ko bai kiraba ita tasa gwaggo ko kawu Amadu wani ya kira mata shi, Mahaifi mai dadi (Allah ka jikan namu da suka rasu, Amin), Jama'a kuzo kuga Murna agun Fatuu duk tabi ta kankameshi shidae sai dariya yake, fari dashi mai kyau har yafi Fatuu fari saidai daka kalli fuskarshi zaka ga kamanninshi da Fatun yayi shigar dogayen kayan yadi mai kyau kanshi sanye da hula tsaf tsaf dashi kaman ba daga k'auye yake ba, amman daka ganshi kaga cikakken bafullatani, A d'akin Amadu aka sauke shi fatuu sai faman tambayoyi take mashi tana tambayar yan'uwanta yana bata amsa da muryarshi mai sanyi daga ji baida hayaniya kuma ya iya hausa sosae don Fatun da hausa take mashi Magana koda yayi mata da fullanci amman sam basuyi hausa ba da gwaggo da ta shigo don su k'ara gaisawa, sam Fatuu tak'i barinshi ya huta yaci abinci sosae, tunda ta kawo mashi ta tasashi gaba tana ta bashi labarin Ya Handsome da duk Alkhairan da yake masu kuma har labarin yadda akai suka saba dashi saida ta bashi wanda ko gwaggo batasani ba har yake cewa ashe har yanzu baki daina rashin ji ba inna wuro (sunan da yake kiranta dashi kenan wato uwar masu gida don sunan Mahaifiyarshi ne aka sanya mata), rantsuwa ta hau yi mashi kan ta daina rashin ji kuma ma ya tambayi gwaggo, atare suka ci abincin gwanin burgewa har abaki take bashi, bayan sun gama ya d'an kishingida don ya huta ita kuma tace mashi zataje ta dawo, kopar gida ta nufa wurin kawu Amadu don tunda yaje suka gaisa ya dawo shagon, rok'onshi tayi wai ya kira mata Ya Handsome yace bai kira, Magiya ta fara yi mashi ta hanashi sakat har saida ya kira mata shi, cikin murna ko gaidashi bata yi ba ta sanar dashi Babanta yazo tana ta faman dariya, cemata yay yana tayata murna in ya dawo zaizo su gaisa tace mashi to,
Bayan sallar la'asar yazo gidan yana sanye cikin jeans da t-shirt gaba dayansu navy blue ne, hannunshi sanye da agogo bak'a hakama takalmanshi bakake ne sai sakin kayataccen kamshi yake, Amadu ya shigar dashi wurin Baban Fatun lokacin tana like dashi sai faman zuba take mashi ko islamiyya tace bata zuwa, bayan Amadu ya shigo ya sanar mashi cewa zasu gaisa da bako ya juya waje yace ma Haisam ya shigo, fatuu na jin muryarshi yayi yar sallama ta wani zabura ta tashi zaune, ganin shine da gaske yasa ta washe baki tace ma babanta to ga Ya Handsome d'in da take bashi labari nan, ganin ba abun zama yasa Amadu cewa bari ya d'aukko mashi kujera acikin gida haisam yace ya barshi, d'an duk'awa yayi suka gaisa cike da mutuntawa anan yake mashi godiya yace inna wuro ta fad'i mashi abun arzikin da yake masu, to shi d'inma dai cemashi yay ba wani abu, daga haka shiru ta biyo baya don gaba d'ayansu ba gwanayen Magana bane kai kace bashi ne Mahaifin Fatuu ba ta wannan fannin, muryarta kawai ake ji sai zuba take tana zuba uwar shagwa6a da shirme kala kala kanta na akan kafafunshi,
" Baffa na gaya maka Ya Handsome dinnan yana da motoci, in kana so sai ya kaika kaga garin nan" Fatuu ta fad'a,shiru baice mata komai ba hakan yasa ta d'aga idanunta tana kallonshi tace "ko baka son ganin garinne?",
fuskarshi da fara'a yana kallonta cikin harshen fulatanci yace mata ai ba dad'ewa zaiyi ba gobe da safe zai tafi, tana jin hakan ta fara bori tana tittirza k'afa akan katifar cike da shagwa6a tace " kai da ka dad'e baka zo ba kuma sai kace wai gobe zaka tafi, ni dai ban yarda ba Allah kwan",
Still Haisam yay yana kallonsu fuskarshi a sake shi kuma mahaifin nata sai murmushi yake da gani dai yana da fara'a sosae, ganin yadda take ta zuba shagwa6a ne yasashi cemata yaso zuwa tuni Ardo ne yay jinya shiyasa bai zo ba kuma har yanzu bai idasa warwarewa ba shiyasa bazai zauna ba don shi ke kula da harkokinshi da yawa acan, da bud'ar bakinta sai cewa tayi " Allah yasa ma ciwon mutuwa ne yakeyi kowa ya huta da masifa " tana yin Maganar suka had'a ido da haisam ya d'an harareta shi kuma baban nata kama kunnanta guda yay ya d'an ja ta saki yar k'ara tana fad'in " wad' muyal baffa, ba ya tsufa ba",
murmushi Haisam ya danyi kafin ya mik'e yay mashi sallama ganin yana kokarin tashi shima yace yay zaman shi da mota yake zai wuce ne, mik'ewa Fatuu tayi tana sanye da riga da skirt na shadda kanta ba kallabi tace ma babanta bari ita ta raka shi waje yanzu zata dawo,
Haisam da har ya nufi mota ya juyo sakamakon kiran sunanshi da tayi, tsayawa yayi ta k'araso tana ta dariya ta kasa ce mashi komae,
" U'r Happy Dad yazo ko" jinjina mashi kai tayi sai kuma ta kwa6e fuska tace " bacin ma wai gobe da safe zai tafi",
" yana da uzuri ne" ya fad'a yana kokarin juyawa,
" gida zaka koma?" ta tambayeshi, kai ya girgiza alamar a'a,
" To ina zaka?"
"Gym" ya bata amsa yana nufar mota,
" ko in zo in raka ka?" sai lokacin ya tsaya yay mata wani kallo ta kyalkyace da dariya,
" ina Aunty Anah?" ta tambayeshi bayan ta daina dariyar,
" tana tambayarki" ya bata amsa a takaice,
" wayyo, don Allah zaka k'ara kaini in ganta, wllh tana da kirki",
girgiza mata kai yay alamar a'a aikuwa ta fara d'an bubbuga kafa tana jujjuya kai, kai kawai ya d'an girgiza ya kai hannu ya bud'e motar ya shiga kafarshi guda awaje, ganin tak'i daina abunda take yasa yay mata alamar tazo da hannunshi, sealed Popcorn da tuwon madara ya mik'o mata ta amsa sai kuma cewa tayi "Ya Handsome na gane wayonka, ina yi maka rigima shine kaban wad'annan abubuwan don inyi shiru ka maida ni karamar yarinya ko",
d'an cije peach lip dinsa na kasa yay da alama ta kashe shi da mamaki, murya can kasa ya furta "kinsan ma rigima ne kike man ko Zarah?" jin haka yasa ta 6oye a gefen motar tana dariya, d'an leko da kanshi yay ya kalleta aikuwa da sauri ta kife fuskar, girgiza kai yay yace "ki koma kin bar dad shi kadae" yana fad'in hakan ya maida kafarshi ciki ta lek'a kanta tana kallonshi yay mata alamar taje da hannu, har saida ya tashi motar ya tafi tana ta d'aga mashi hannu, lokacin data koma cikin d'akin kawu Amadu Babanta har yayi bacci, bawan Allah tun karfe hudu na asuba ya taho ya sauka a Kano kafin ya hau motar Katsina, ya kwaso gajiya don akwae nisa tsakanin Katsina da Yola kusan fin awa goma yana hanya yazo kuma ta hanashi hutawa, Allah yaso yan hankali sunzo mata ta kyaleshi ta nufi cikin gida, tare suka ci abunda haisam ya bata da gwaggo amman fa sai da ta rage ma Baffanta, da daddare aka aiketa gidan hajiya ta kai mata tsaraba ananne tasan baban nata yazo tace ta tayata murna in Allah ya kaimu sa gaisa dashi, bayan ta dawo rigima tasa wai awurinshi zata kwana dole saidai Amadu ya tafi dakinta ya kwana,