Sashe 22
Asanadin Makwabtaka Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Fatuu na fitowa harabar gidan aka bud'e ma Haisam gate ya shigo,parking space ya shige ya parker bike din,ya fito jakar shi rataye a 6arin hannunshi na hagu,hannunshi na dama rike da Bottle water ya d'aga yana d'an sha a hankali ya nufi part dinsa, Fatuu kuwa tsaye tayi a tsakiyan harabar ta rike k'ugunta da d'ayan hannunta da ba komae,a fili tace "Kai! waye wannan kuma da ya shigo a saman waccan dirkeken babur d'in dana gani rannan a ajiye? Ko bak'o akayi bansani ba" yadda tayi maganar kamar irin gidan ubantan nan.
Fatuu bata ta6a ganin haisam cikin gidan ba,don bai dade daya dawo ba weekend dinshi na biyu kenan,dama kuma tafi zuwa gidan ranakun da ba islamiyya Alhamis da juma'a saboda Working days ba lokaci da safe taje boko da yamma kuma islamiyya haka Weekends ma Safe da Yamma tana islamiyya sai dai ko da dare in an aikota kaman yanzu da aka aiko tan shima aiken akan kwana biyu ba'a aiko ta ba,Wani lokacin kuma tana cema gwaggon zata zo ta gaida Hajiar in dare bai yi ba sosae,kuma da tazo suka gaisa hajia zata ce ta tafi gida dare yayi.Ranar Alhamis da ta wuce tazo gidan da yamma kaman yadda tace ma Gwaggo bayan ta fito ne ta biyo Jamila suka yi fad'a har ta zubar mata da Awara a lokacin ne kuma ta fara ganin Haisam d'in.
Ganin haisam na niyyar shigewa corridor yasa ta bi bayanshi da sauri tana fad'in "Aikuwa sai naga ko waye" daidai lokacin da ta iso bakin fence door d'in shiga part d'inshi,shi kuma yana taka matattakalar hawa balcony,jin kaman motsi a bayansa yasa shi dan juyowa,da sauri Fatuu ta koma gefe ta la6e,a hankali ta lek'o da kanta lokacin ya kama handle din kofa zai bud'e ya sake waiwayowa nan take ta gane fuskarsa don gaba daya hasken fitilu ya haske wurin kaman da rana,da sauri tasa tafin hannunta ta rufe bakinta ta juya da d'an gudu gudu tabar wurin,ko amsa saida safe da Officer ke mata bata yi ba,ta yanki hanyar gida tana yi tana waiwayen bayanta,har tana yin tuntu6e,
tana zuwa daidai kiosk din kawu Amadu yace"Ke,daga ina ki ke? Cikin rawar murya tace "d..daga gidan h..hajiya tuwo na kai mata" Yace"miye a cikin kwanon nan" bata bashi amsa ba sai kawai ta bud'e masa kwanon,da yake akwae wuta nan take yaga abunda ke ciki yace "Ah nima kam zanci in kin shiga ki d'an zubo man a plate" tace "toh" daga haka ta shige gidan da sauri,har lokacin hijab d'in da ta d'aura jikin window na nan,tasa hannu ta ciro ta wuce ciki,a bakin kofar kicin ta aje kwanon ta shige d'aki,
fad'awa tayi saman Gado ta takure wuri d'aya sai faman zare ido take cike da fargabar Mutumin nan da ta gani,a ranta kuwa sai maimaita abu d'aya take "dama a gidan hajiya yake...!" a fili tace "Innalillahi,to ko ya gaya ma hajia..!!! Can kuma tace "to amman da ya gaya mata ai da tayi man magana" ta rik'e ha6a alamar tunani,
Ta ci gaba"to ai bai san ni ko wacece ba,kai kilan ma ya fad'a mata fa" ta shiga yarfa hannuwa tace"Aikuwa in hajia tasani ta kuma gane ni ce...." shiru tayi saboda wani bugu da kirjinta ke yi sai zaro ido take,
Gwaggo ce ta fito daga d'aki hannunta rik'e da buta zata band'aki,daidai kitchen ta tsaya tana kallon kwanon da Fatuu ta aje a ranta tace "Ah wannan ba kwanon dana aiki fatuu dashi bane,yaushe ta shigo gidan? hannu tasa ta bud'e kwanon k'amshin couscous din ya bugi hancinta,tace"tabbas fatuu ta aje shi" d'agowa tayi ta kalli bakin kofar d'akin Fatun bata ga takalmanta ba don dasu ta shige d'akin hakan yasa tayi tunanin ficewa ta sake yi kenan,kwafa tayi a fili tace "zata dawo ta same ni,saita fad'an inda taje a daran nan" daga haka ta wuce band'akin.
Shiru shiru gwaggo nata jira taji shigowar fatuu,har bayan wani lokaci bata ji ta shigo ba hakan yasa ta fito ta nufi kofar gida ta lek'a ta wawwaiga ko zata hange ta amman bata ganta ba,
wani yaro ta hango tsaye a bakin shagon Amadu tace "Kai yiman kiran Amadu don Allah" tunkan yaron yayi magana Amadu yace mashi "naji", bayan ya sallami yaron ya bud'e kofan kiosk din ya fito ya nufi inda Gwaggo take tun kafin yace wani abu gwaggo tace mashi "Fatuu fa? Da mamaki ya maimaita sunan fatu yace "ba tana a cikin gidan ba? tace "a'a bata nan" shiru yayi yana tunani can yace "gaskia nadai ga sanda ta dawo daga gidan Hajiyar Sanata tace ke kika aiketa,harma naganta ta dawo da abinci nace ta d'an zubo man"
Gwaggo tace "to ta kawo ma abincin? Yace "a'a,tunda ta shiga banga ta fito ba gaskia,kin duba d'akinta? Tace "ai ko takalmanta babu a kofar d'akin,shiyasa ma ban duba ciki ba,don nasan in tana nan zan gansu a bakin d'akin" Amadu yace"ki dae duba cikin kilan ta shiga dasu don dama kaman a firgice take ta shiga gidan",
Gwaggo ta ta6e baki tace " wannan daman ai koda yaushe ma a firgice take,bari in duba d'akin to" har ta nufi ciki ta juyo tace"ka shigo ga abincin can a kofan kicin sai ka d'iba ka rage mata" yace "toh" daga haka ta nufi d'akin Fatuu,tsayawa gwaggo tayi cike da mamakin ganin fatuu kwance saman gado ta duk'unkune wuri guda,ta nufeta ta d'an leka fuskarta sai taga bacci take,gwaggo tace "bacci kuma.." hannu tasa ta d'an bubbuga k'afafunta aikuwa nan da nan ta farka firgigit sai zare ido take tana kallon gwaggon,
Gwaggo ta mik'e tana k'are mata kallo tace"yaushe kika shigo gidan? Kuma lafiya kike yin bacci haka? Saukko da k'afafunta tayi k'asa tace "tun d'azun na shigo"tasa hannu tana goge idanunta,
"amman ba ke kika zo da abincin da na gani a kofan kitchen ba" tace "ni nazo da shi,hajiya ta bani" Gwaggo tace to "bazaki ci bane kika aje kika zo kina bacci,kuma ma nasan ko salla baki yi ba" ita dai fatuu sai faman zare ido take hakan yasa gwaggo tace"wai mike damunki ne kike ta faman zaro idanu,da gani baki da gaskia,halan wata rigimar kika jawo,don nasan wannan baccin dama ba na Allah bane,da gani na rashin gaskiya ne" gaban fatuu ya fadi rass cike da tsoro take kallon gwaggon, tasan in har gwaggon taji abunda ta aikata kashinta ya bushe balle kuma taji mutumin dan gidan hajia ne tabb......,tsawa taji gwaggo ta daka mata "ba dake nike bane fatuu,mi ya faru ki ka zo kika kwanta haka? A daburce tace "da..dama kare ne ya biyo ni" sam bata san ta ambaci karen ba,
Gwaggo ta harareta tace"kece ke tsoron wani kare,sau nawa kike zuwa kina tono karen,ina kwanan nan kika je kika kinkimo d'an karya ta biyo ki har kofar gida,shine zaki wani ce man kare ne ya biyo ki...." da sauri ta katse gwaggon ganin zata gano k'arya take tace "ai ba irin shi bane fa,wannan fa irin mai gashi buzu buzu ne mai kaman zaki" ta kai maganar tana ta zare idanu tana hadiyar yawu,
gwaggon tace "to ke miya had'a ki da irin wannan karen, ina ki ka ganshi da zai biyo ki? tace "ina fitowa daga gidan hajia wani mutumi yazo zai wuce dashi shine yaji kamshin abincin hannuna yayo kaina shine na rugo" gwaggo ta girgiza kai don ta yarda da abunda fatun ta fad'a,tace "Allah ya kyauta to" da sauri fatuu tace "Amin,ganin ta yarda da k'aryar da ta gandara,
Gwaggo ta juya tana fadin "ki fito kici abincin,kiyi sallah sai kiyi baccin da kyau..."daga haka ta fice,fatuu ta dafe kirjinta alamar tasha,ta mik'e tabi bayan Gwaggon.
Amadu na gab da fita hannunshi rik'e da plate din daya d'ibi abinci yaji gwaggo ta fito daga dakin fatuu tana magana,ya juya yana tambayarta fatun na ciki? Gwaggo ta ta6e baki tace "tana nan,wai kare ne ya biyo ta shine ta tsorata,harda su baccin dole" dariya Amadu yayi yace "Ashe akwae karen da zai iya firgita ta haka"ya girgixa kai daga haka ya fice.
Fatuu bata ta6a ganin haisam cikin gidan ba,don bai dade daya dawo ba weekend dinshi na biyu kenan,dama kuma tafi zuwa gidan ranakun da ba islamiyya Alhamis da juma'a saboda Working days ba lokaci da safe taje boko da yamma kuma islamiyya haka Weekends ma Safe da Yamma tana islamiyya sai dai ko da dare in an aikota kaman yanzu da aka aiko tan shima aiken akan kwana biyu ba'a aiko ta ba,Wani lokacin kuma tana cema gwaggon zata zo ta gaida Hajiar in dare bai yi ba sosae,kuma da tazo suka gaisa hajia zata ce ta tafi gida dare yayi.Ranar Alhamis da ta wuce tazo gidan da yamma kaman yadda tace ma Gwaggo bayan ta fito ne ta biyo Jamila suka yi fad'a har ta zubar mata da Awara a lokacin ne kuma ta fara ganin Haisam d'in.
Ganin haisam na niyyar shigewa corridor yasa ta bi bayanshi da sauri tana fad'in "Aikuwa sai naga ko waye" daidai lokacin da ta iso bakin fence door d'in shiga part d'inshi,shi kuma yana taka matattakalar hawa balcony,jin kaman motsi a bayansa yasa shi dan juyowa,da sauri Fatuu ta koma gefe ta la6e,a hankali ta lek'o da kanta lokacin ya kama handle din kofa zai bud'e ya sake waiwayowa nan take ta gane fuskarsa don gaba daya hasken fitilu ya haske wurin kaman da rana,da sauri tasa tafin hannunta ta rufe bakinta ta juya da d'an gudu gudu tabar wurin,ko amsa saida safe da Officer ke mata bata yi ba,ta yanki hanyar gida tana yi tana waiwayen bayanta,har tana yin tuntu6e,
tana zuwa daidai kiosk din kawu Amadu yace"Ke,daga ina ki ke? Cikin rawar murya tace "d..daga gidan h..hajiya tuwo na kai mata" Yace"miye a cikin kwanon nan" bata bashi amsa ba sai kawai ta bud'e masa kwanon,da yake akwae wuta nan take yaga abunda ke ciki yace "Ah nima kam zanci in kin shiga ki d'an zubo man a plate" tace "toh" daga haka ta shige gidan da sauri,har lokacin hijab d'in da ta d'aura jikin window na nan,tasa hannu ta ciro ta wuce ciki,a bakin kofar kicin ta aje kwanon ta shige d'aki,
fad'awa tayi saman Gado ta takure wuri d'aya sai faman zare ido take cike da fargabar Mutumin nan da ta gani,a ranta kuwa sai maimaita abu d'aya take "dama a gidan hajiya yake...!" a fili tace "Innalillahi,to ko ya gaya ma hajia..!!! Can kuma tace "to amman da ya gaya mata ai da tayi man magana" ta rik'e ha6a alamar tunani,
Ta ci gaba"to ai bai san ni ko wacece ba,kai kilan ma ya fad'a mata fa" ta shiga yarfa hannuwa tace"Aikuwa in hajia tasani ta kuma gane ni ce...." shiru tayi saboda wani bugu da kirjinta ke yi sai zaro ido take,
Gwaggo ce ta fito daga d'aki hannunta rik'e da buta zata band'aki,daidai kitchen ta tsaya tana kallon kwanon da Fatuu ta aje a ranta tace "Ah wannan ba kwanon dana aiki fatuu dashi bane,yaushe ta shigo gidan? hannu tasa ta bud'e kwanon k'amshin couscous din ya bugi hancinta,tace"tabbas fatuu ta aje shi" d'agowa tayi ta kalli bakin kofar d'akin Fatun bata ga takalmanta ba don dasu ta shige d'akin hakan yasa tayi tunanin ficewa ta sake yi kenan,kwafa tayi a fili tace "zata dawo ta same ni,saita fad'an inda taje a daran nan" daga haka ta wuce band'akin.
Shiru shiru gwaggo nata jira taji shigowar fatuu,har bayan wani lokaci bata ji ta shigo ba hakan yasa ta fito ta nufi kofar gida ta lek'a ta wawwaiga ko zata hange ta amman bata ganta ba,
wani yaro ta hango tsaye a bakin shagon Amadu tace "Kai yiman kiran Amadu don Allah" tunkan yaron yayi magana Amadu yace mashi "naji", bayan ya sallami yaron ya bud'e kofan kiosk din ya fito ya nufi inda Gwaggo take tun kafin yace wani abu gwaggo tace mashi "Fatuu fa? Da mamaki ya maimaita sunan fatu yace "ba tana a cikin gidan ba? tace "a'a bata nan" shiru yayi yana tunani can yace "gaskia nadai ga sanda ta dawo daga gidan Hajiyar Sanata tace ke kika aiketa,harma naganta ta dawo da abinci nace ta d'an zubo man"
Gwaggo tace "to ta kawo ma abincin? Yace "a'a,tunda ta shiga banga ta fito ba gaskia,kin duba d'akinta? Tace "ai ko takalmanta babu a kofar d'akin,shiyasa ma ban duba ciki ba,don nasan in tana nan zan gansu a bakin d'akin" Amadu yace"ki dae duba cikin kilan ta shiga dasu don dama kaman a firgice take ta shiga gidan",
Gwaggo ta ta6e baki tace " wannan daman ai koda yaushe ma a firgice take,bari in duba d'akin to" har ta nufi ciki ta juyo tace"ka shigo ga abincin can a kofan kicin sai ka d'iba ka rage mata" yace "toh" daga haka ta nufi d'akin Fatuu,tsayawa gwaggo tayi cike da mamakin ganin fatuu kwance saman gado ta duk'unkune wuri guda,ta nufeta ta d'an leka fuskarta sai taga bacci take,gwaggo tace "bacci kuma.." hannu tasa ta d'an bubbuga k'afafunta aikuwa nan da nan ta farka firgigit sai zare ido take tana kallon gwaggon,
Gwaggo ta mik'e tana k'are mata kallo tace"yaushe kika shigo gidan? Kuma lafiya kike yin bacci haka? Saukko da k'afafunta tayi k'asa tace "tun d'azun na shigo"tasa hannu tana goge idanunta,
"amman ba ke kika zo da abincin da na gani a kofan kitchen ba" tace "ni nazo da shi,hajiya ta bani" Gwaggo tace to "bazaki ci bane kika aje kika zo kina bacci,kuma ma nasan ko salla baki yi ba" ita dai fatuu sai faman zare ido take hakan yasa gwaggo tace"wai mike damunki ne kike ta faman zaro idanu,da gani baki da gaskia,halan wata rigimar kika jawo,don nasan wannan baccin dama ba na Allah bane,da gani na rashin gaskiya ne" gaban fatuu ya fadi rass cike da tsoro take kallon gwaggon, tasan in har gwaggon taji abunda ta aikata kashinta ya bushe balle kuma taji mutumin dan gidan hajia ne tabb......,tsawa taji gwaggo ta daka mata "ba dake nike bane fatuu,mi ya faru ki ka zo kika kwanta haka? A daburce tace "da..dama kare ne ya biyo ni" sam bata san ta ambaci karen ba,
Gwaggo ta harareta tace"kece ke tsoron wani kare,sau nawa kike zuwa kina tono karen,ina kwanan nan kika je kika kinkimo d'an karya ta biyo ki har kofar gida,shine zaki wani ce man kare ne ya biyo ki...." da sauri ta katse gwaggon ganin zata gano k'arya take tace "ai ba irin shi bane fa,wannan fa irin mai gashi buzu buzu ne mai kaman zaki" ta kai maganar tana ta zare idanu tana hadiyar yawu,
gwaggon tace "to ke miya had'a ki da irin wannan karen, ina ki ka ganshi da zai biyo ki? tace "ina fitowa daga gidan hajia wani mutumi yazo zai wuce dashi shine yaji kamshin abincin hannuna yayo kaina shine na rugo" gwaggo ta girgiza kai don ta yarda da abunda fatun ta fad'a,tace "Allah ya kyauta to" da sauri fatuu tace "Amin,ganin ta yarda da k'aryar da ta gandara,
Gwaggo ta juya tana fadin "ki fito kici abincin,kiyi sallah sai kiyi baccin da kyau..."daga haka ta fice,fatuu ta dafe kirjinta alamar tasha,ta mik'e tabi bayan Gwaggon.
Amadu na gab da fita hannunshi rik'e da plate din daya d'ibi abinci yaji gwaggo ta fito daga dakin fatuu tana magana,ya juya yana tambayarta fatun na ciki? Gwaggo ta ta6e baki tace "tana nan,wai kare ne ya biyo ta shine ta tsorata,harda su baccin dole" dariya Amadu yayi yace "Ashe akwae karen da zai iya firgita ta haka"ya girgixa kai daga haka ya fice.