Sashe 72
Asanadin Makwabtaka Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ba irin k'okarin da Amadu baiyi ba don ya fidda mata shi amman abun yaci tura duk ya had'a uban gumi, shima sai faman yago papers yake yana jagwalgwalawa kaman dai yadda Fatun tayi, a k'arshe dakyar ya samo wani problem anyi solving mai shige dashi acikin textbook d'inshi, a hankali ya rink'a bin steps d'in da akayi waccan wai ko zai iya fidda mata,sai faman sharce zufa yake Fatuu nayi mashi sannu,can ya d'ago a fusace ya wurga mata bangon littafi yace tayi mashi firfita baiwar Allah da sauri tace to ta d'auki bangon ta fara yi mashi don bata da burin da ya wuce taga yayi mata Assignment din,abu fa ya ture,lissafi an koya maka ma ya gagareka yi balle wanda ba'a koya maka ba,baka ma san hanyar da zaka bi kayi shi ba,kwalwar Amadu fa ta cazu iya cazuwa gashi ba abun yace zaiyi goggling ba tunda wani abunma ba yadda za'ai ya rubuta shi da wayarshi,ak'arshe dae da ya fusata sai ya cillar da biron ya d'auki paper d'in da yake solving d'in ya kekketata a fili yace"ina dalili,haka kawae in haukata kaina,ke nifa dama wllh ban kaunar Maths don ba yarda zanyi nike yinshi tunda ya zama dole",
Fatuu na jin haka idanunta suka cicciko da kwalla ta fara ta6e baki zatai kuka,cikin muryar kuka ta fara mashi Magiya,a harzuke kaman zai kai mata bugu yace"to wai ya kike son inyi ne?ba kiga duk irin kokarin dana yi bane,inda na iya ai zan maki ko,shima malamin daya baku Assignment dinnan ina tunanin yaci kai,taya zai baku abu alhalin bai maku irinshi ba,kuma ya rubuta question kawae ba wani d'an bayanin da mutum zai gane ko wane topic ne",ita dae Fatuu sai faman matsar kwalla take,wani kallo ya wurga mata mai kama da harara ya dan ja guntun tsoki can ya kai hannu ya daukko wayarsa,
"Bari in kira wani abokina d'an Class dinmu yana da kokari sosae shi ke yin na daya a ajinmu kilan shi ya iya yinshi", har Fatuu taji dan sanyi a ranta,bayan ya kirashi yayi mashi bayani kan Assignment din,yace kanwarshi ce aka ba shi kuma yayi iya bakin k'okarinshi ya kasa,Abokin nashi yace ya tura mashi Question d'in ta Whatsapp ya gani,bayan sun gama wayan ya d'auki hoton tambayar ya tura mashin daga haka suka yi jugum jugum suna jiranshi,bayan wani lokaci sai gashi ya kirashi a waya,Amadu na d'auka tambayar daya fara yi mashi itace wai under wane topic ne aka ba sister d'in nashi wannan question d'in,Amadu yace itama bata sani ba kawae tambayar ya rubuta masu yace ga irin amsar dayake so su gano nan,nan take Abokin yace to gaskia wannan zasuyi ta wahala ne kawai,tunda ko su ba'ayi masu irinshi ba balle su san hanyar da zasu bi su gano irin amsar da yake son ba,abunda za'ai ya bari gobe in sunje Makaranta sai su ba Malamin Maths d'insu yayi masu bayanin yadda za'a fidda shi kawae,nan take Amadu yace hakan za'ai,ai shi sam yama manta yayi wannan tunanin kuma yasan Confirm Malamin nasu zai fidda masu don ya had'u a lissafi,daga haka suka yi sallama yayi mashi godiya,
Koda yayi ma Fatuu bayanin shawarar da suka yanke da Abokin nashi sai tasa mashi kuka tana fad'in"ai gobe zai amsa fa,kuma da safe muke dashi",a fusace Amadu ya d'auki littafin ya wurga mata ajikinta,
"Gashi nan to sai kije kisan yadda zaki fidda kayanki,ni ina zargin ma wllh wani laifin kika aikata aka baki wannan aikin mai dan banzan wahala shine zaki zo ki wahalar da Mutane a banza a wofi,da ganin yadda kika tashi hankalinki baki da gaskiya,in ma laifin kikai aka baki Allah ya k'ara yasama karki iya fidda shi har goben tayi a zane ki tunda haka kika fi so,kinga in halinki ne gobe ma sai ki k'ara yin laifin da za'a baki irinshin,dalla tashi ni ki fita ki ban wuri kinzo kin hanani hutawa balle ko shago inje in bud'e",
Cikin tsananin fushi ta mik'e har wani huci take tana d'an harararshi,d'aukar littafin tayi da bironta da ya wurgar can gefe ta nufi hanyar fita,adaidai bakin koparshi ta tsaya,juyowa tayi lokacin yana niyyar kwanciya,
A tsiwace tace"Eh laifin nayi,kuma inna k'ara yin laifin an sake bani wani ai ko na kawo makan ba iya yimun zakai ba tunda yanzu ma gashi ka kasan balle kaman surut....."bata k'arasa ba sakamakon wani kukan kura da yayi ya nufo ta a fusace,aikuwa da gudu kaman walk'iya ta fice kopar gida da gudu,tsaye tayi tsakiyar center tana kallonshi yayi tsaye cikin zaure sai huci yake,yasan in ya biye mata wahalar dashi kawae zatayi ta maidashi kaman Mahaukaci,kwafa yayi a fili ya furta"zaki dawo gidan",daga haka ya shige cikin d'akinshi,
Tsaye tayi awurin abun Duniya duk ya isheta,wani kunci take ji acikin ranta na rashin yin Assignment d'in gashi tasan in dai ta sake ta koma cikin gidan to kuwa kashinta ya bushe,yadda Gwaggo bata nan ai sai kawu Amadu ya kusa kasheta gashi dama bak'ar zuciya ce dashi sam bai iya bugu ba,sai lokacin ta fara danasanin abunda ta gaya mashin,tana cikin tsayuwar nan Ya Handsome ya fad'o mata arai,nan take ta fara tunanin ta kai mashi Assignment d'in kilan shi ya iya shi tunda ya gama karatu har yana aiki,lokaci guda ta saki Murmushi duk da bata da tabbacin ya iya d'in,har ta juya zata tafi ta tuna ai ko kallabi bata dashi kuma gashi tana tsoron shiga gidan ta d'aukko,nan take dubara ta fad'o mata,bud'e tsakiyar littafin tayi ta kifa asaman kanta daga haka ta nufi gidan Hajiyar Sanata.
*💖A SANADIN MAKWABTAKA💖*
_A heart touching story of Love and Destiny_ 💔
*Mallakin*
⬇️
*🌹ZAINAB LALUH*📲✍
_~(Oummu imam)~_
*DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI*
4️⃣9️⃣
Haisam zaune saman kujera L-shape ya dan kishingida jikinshi sanye cikin bak'ak'en kaya jeans da t-shirt gaban rigar anyi rubutu golden colour hannunshi sanye da Agogo golden,tun bayan daya dawo daga aiki wanka kawae yayi ko part d'in Hajiya baije ba yaci abinci ya zauna yana yin video call,yana yin firan yana d'an gutsiran cake dake ajiye gefen laptop dinshi dake kan c-table hannunshi guda na ruke da glass cup mai d'auke da ruwan lemu yana d'an sipping ahankali,
Turo kopar tayi bakinta d'auke da sallama ta shigo,a gefen kujeran ta tsaya idonta akanshi,a hankali ya wurga eyeballs d'inshi kanta suna had'a ido ya d'an yi Murmushi hakan yasa itama tayi mashi,
"Who is dat?" wata zazzak'ar murya daga cikin laptop d'in ta tambaya da alama wadda yake yin video call d'in da itace,maido idanunsa yayi kan screen d'in slowly ya furta"Zarah"yayi Maganar had'i da lumshe ido,
"Oh really?" mai muryar ta tambaya,d'aga mata kai yayi alamar eh,
"I wanna see her,where is she" ta sake fad'a alamar tana son ganin Fatuu,daga yadda take turancin zaka yanke ba bahaushiya bace,kallon fatun yayi yai mata alamar tazo da kanshi,sai lokacin tasa hannu ta cire littafin dake asaman kanta ta d'an matso gaba kadan,da yatsanshi ya nuna mata Laptop dinshi yace"zaku gaisa da ita ne"cikin rashin fahimta tace"wa?",
wani kallo yayi mata"ki duba inda nike pointing mana" da sauri ta juya ta kalli inda yake nuna matan,Matashiyar budurwa ce da zata iya kai shekara 21 zuwa 22 haka,tana zaune asaman gado ta jingina bayanta da kan gadon,lokacin da Fatun ta kalli Computer d'in budurwar ta juya gefe ta dauki ruwan roba dake aje saman bedside drawer ta daga tana sha hakan yasa bata ga ainihin fuskarta ba sai dai dogon gashinta dake gefe da gefen fuskar ya zuba har kan cikinta wanda launinsa brown ne sosae haka fatar jikinta ma fara ce sosae wanda kallo d'aya zakai mata ka kirata da farar fata,sai dae sam kalar hasken fatarta dana haisam ba iri daya bane kowa da launin haskensa,
Ai Koda Fatuu tayi arba da ita a firgice ta juya ta kalli haisam tace"Ya Handsome da wannan zamu gaisa din?"fuskarshi a sake kaman zaiyi dariya ya d'aga mata kai don yadda ta firgitan taso bashi dariya,
a rud'e ta kuma cewa"to amman ai ni fa ban iya irin turancinsu ba mai saurin nan,ba rannan na fad'a maka ba har kace zaka koya man amman sai ka samu isashshen lokaci to yanzu ya zanyi magana da ita....."kafin ta k'arasa budurwar ta katseta da fad'in,
"karki damu nima bahaushiya ne ai" yadda tayi hausar gwanin dad'i,da sauri Fatuu ta maida kallonta gareta lokacin ta gama shan ruwa ta juyo da fuskarta sosae,Tubarkallah Ma sha Allah,kallo daya zakai mata ka shaida kyawun fuskarta,kyakkyawa ce matuk'a ga kwayar idonta brown ce har wani kyalli take,waro ido Fatuu tayi tana kallonta arazane,ba kyawunta ne kad'ai ya razana ta ba, harda furucin da tayi na wai itama bahaushiya ce to ta yaya?shine abunda ya tsaya ma fatun arai.
Hannu ta d'aga ma Fatuu"hi,Zarah how're u?",
Cike da mamaki fatuu tace"da gaske ke bahaushiya ce?"
"Yeah,kuma ina jin hausa kaman jakin kano ba" tayi Maganar tana dariya haka kuma ba k'aramin kyau ya k'ara mata ba,kan fatuu fa ya Matuk'ar daurewa hannu guda tasa ta rufe bakinta alamar mamaki kafin tace"wai har sunan jaki ma kin sani kenan!",ba budurwar ba har Haisam dake saurararsu saida ya d'an murmusa,
"Na fad'a maki nima bahaushiya ne ko baki yarda ba,nasan komae ai saboda nima yar Nigeria ne, anan aka haifeni, anan nayi wayo har na girma",
kai abunfa nayi ne,neman wurin zama Fatuu ta fara don da a duk'e take tayi ruku'u,ganin haka yasa Haisam janye kafarsa daya mik'e kan kujeran ya matsa can gefe,zama tayi sosae tace"to ke wacece,kuma wane gari kike ko ke yar gidansu Ya Handsome ce amman kuma naga ba kalarku daya ba"duk ta jero mata tambayoyin nan,
Murmushi tayi tasa hannunta tana gyara gefe da gefen gashinta kafin ta fara magana"sunana FANAN,ni yar Lagos ne and ni kanwarsa ce but am his Cousin sis kinsan me cousin ke nufi ko?"da sauri Fatuu ta d'aga mata kai"Eh nasani anyi mana shi a English,diya ko dan kanin ko yayan iyayen Mutum",
Fatuu na jin haka idanunta suka cicciko da kwalla ta fara ta6e baki zatai kuka,cikin muryar kuka ta fara mashi Magiya,a harzuke kaman zai kai mata bugu yace"to wai ya kike son inyi ne?ba kiga duk irin kokarin dana yi bane,inda na iya ai zan maki ko,shima malamin daya baku Assignment dinnan ina tunanin yaci kai,taya zai baku abu alhalin bai maku irinshi ba,kuma ya rubuta question kawae ba wani d'an bayanin da mutum zai gane ko wane topic ne",ita dae Fatuu sai faman matsar kwalla take,wani kallo ya wurga mata mai kama da harara ya dan ja guntun tsoki can ya kai hannu ya daukko wayarsa,
"Bari in kira wani abokina d'an Class dinmu yana da kokari sosae shi ke yin na daya a ajinmu kilan shi ya iya yinshi", har Fatuu taji dan sanyi a ranta,bayan ya kirashi yayi mashi bayani kan Assignment din,yace kanwarshi ce aka ba shi kuma yayi iya bakin k'okarinshi ya kasa,Abokin nashi yace ya tura mashi Question d'in ta Whatsapp ya gani,bayan sun gama wayan ya d'auki hoton tambayar ya tura mashin daga haka suka yi jugum jugum suna jiranshi,bayan wani lokaci sai gashi ya kirashi a waya,Amadu na d'auka tambayar daya fara yi mashi itace wai under wane topic ne aka ba sister d'in nashi wannan question d'in,Amadu yace itama bata sani ba kawae tambayar ya rubuta masu yace ga irin amsar dayake so su gano nan,nan take Abokin yace to gaskia wannan zasuyi ta wahala ne kawai,tunda ko su ba'ayi masu irinshi ba balle su san hanyar da zasu bi su gano irin amsar da yake son ba,abunda za'ai ya bari gobe in sunje Makaranta sai su ba Malamin Maths d'insu yayi masu bayanin yadda za'a fidda shi kawae,nan take Amadu yace hakan za'ai,ai shi sam yama manta yayi wannan tunanin kuma yasan Confirm Malamin nasu zai fidda masu don ya had'u a lissafi,daga haka suka yi sallama yayi mashi godiya,
Koda yayi ma Fatuu bayanin shawarar da suka yanke da Abokin nashi sai tasa mashi kuka tana fad'in"ai gobe zai amsa fa,kuma da safe muke dashi",a fusace Amadu ya d'auki littafin ya wurga mata ajikinta,
"Gashi nan to sai kije kisan yadda zaki fidda kayanki,ni ina zargin ma wllh wani laifin kika aikata aka baki wannan aikin mai dan banzan wahala shine zaki zo ki wahalar da Mutane a banza a wofi,da ganin yadda kika tashi hankalinki baki da gaskiya,in ma laifin kikai aka baki Allah ya k'ara yasama karki iya fidda shi har goben tayi a zane ki tunda haka kika fi so,kinga in halinki ne gobe ma sai ki k'ara yin laifin da za'a baki irinshin,dalla tashi ni ki fita ki ban wuri kinzo kin hanani hutawa balle ko shago inje in bud'e",
Cikin tsananin fushi ta mik'e har wani huci take tana d'an harararshi,d'aukar littafin tayi da bironta da ya wurgar can gefe ta nufi hanyar fita,adaidai bakin koparshi ta tsaya,juyowa tayi lokacin yana niyyar kwanciya,
A tsiwace tace"Eh laifin nayi,kuma inna k'ara yin laifin an sake bani wani ai ko na kawo makan ba iya yimun zakai ba tunda yanzu ma gashi ka kasan balle kaman surut....."bata k'arasa ba sakamakon wani kukan kura da yayi ya nufo ta a fusace,aikuwa da gudu kaman walk'iya ta fice kopar gida da gudu,tsaye tayi tsakiyar center tana kallonshi yayi tsaye cikin zaure sai huci yake,yasan in ya biye mata wahalar dashi kawae zatayi ta maidashi kaman Mahaukaci,kwafa yayi a fili ya furta"zaki dawo gidan",daga haka ya shige cikin d'akinshi,
Tsaye tayi awurin abun Duniya duk ya isheta,wani kunci take ji acikin ranta na rashin yin Assignment d'in gashi tasan in dai ta sake ta koma cikin gidan to kuwa kashinta ya bushe,yadda Gwaggo bata nan ai sai kawu Amadu ya kusa kasheta gashi dama bak'ar zuciya ce dashi sam bai iya bugu ba,sai lokacin ta fara danasanin abunda ta gaya mashin,tana cikin tsayuwar nan Ya Handsome ya fad'o mata arai,nan take ta fara tunanin ta kai mashi Assignment d'in kilan shi ya iya shi tunda ya gama karatu har yana aiki,lokaci guda ta saki Murmushi duk da bata da tabbacin ya iya d'in,har ta juya zata tafi ta tuna ai ko kallabi bata dashi kuma gashi tana tsoron shiga gidan ta d'aukko,nan take dubara ta fad'o mata,bud'e tsakiyar littafin tayi ta kifa asaman kanta daga haka ta nufi gidan Hajiyar Sanata.
*💖A SANADIN MAKWABTAKA💖*
_A heart touching story of Love and Destiny_ 💔
*Mallakin*
⬇️
*🌹ZAINAB LALUH*📲✍
_~(Oummu imam)~_
*DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI*
4️⃣9️⃣
Haisam zaune saman kujera L-shape ya dan kishingida jikinshi sanye cikin bak'ak'en kaya jeans da t-shirt gaban rigar anyi rubutu golden colour hannunshi sanye da Agogo golden,tun bayan daya dawo daga aiki wanka kawae yayi ko part d'in Hajiya baije ba yaci abinci ya zauna yana yin video call,yana yin firan yana d'an gutsiran cake dake ajiye gefen laptop dinshi dake kan c-table hannunshi guda na ruke da glass cup mai d'auke da ruwan lemu yana d'an sipping ahankali,
Turo kopar tayi bakinta d'auke da sallama ta shigo,a gefen kujeran ta tsaya idonta akanshi,a hankali ya wurga eyeballs d'inshi kanta suna had'a ido ya d'an yi Murmushi hakan yasa itama tayi mashi,
"Who is dat?" wata zazzak'ar murya daga cikin laptop d'in ta tambaya da alama wadda yake yin video call d'in da itace,maido idanunsa yayi kan screen d'in slowly ya furta"Zarah"yayi Maganar had'i da lumshe ido,
"Oh really?" mai muryar ta tambaya,d'aga mata kai yayi alamar eh,
"I wanna see her,where is she" ta sake fad'a alamar tana son ganin Fatuu,daga yadda take turancin zaka yanke ba bahaushiya bace,kallon fatun yayi yai mata alamar tazo da kanshi,sai lokacin tasa hannu ta cire littafin dake asaman kanta ta d'an matso gaba kadan,da yatsanshi ya nuna mata Laptop dinshi yace"zaku gaisa da ita ne"cikin rashin fahimta tace"wa?",
wani kallo yayi mata"ki duba inda nike pointing mana" da sauri ta juya ta kalli inda yake nuna matan,Matashiyar budurwa ce da zata iya kai shekara 21 zuwa 22 haka,tana zaune asaman gado ta jingina bayanta da kan gadon,lokacin da Fatun ta kalli Computer d'in budurwar ta juya gefe ta dauki ruwan roba dake aje saman bedside drawer ta daga tana sha hakan yasa bata ga ainihin fuskarta ba sai dai dogon gashinta dake gefe da gefen fuskar ya zuba har kan cikinta wanda launinsa brown ne sosae haka fatar jikinta ma fara ce sosae wanda kallo d'aya zakai mata ka kirata da farar fata,sai dae sam kalar hasken fatarta dana haisam ba iri daya bane kowa da launin haskensa,
Ai Koda Fatuu tayi arba da ita a firgice ta juya ta kalli haisam tace"Ya Handsome da wannan zamu gaisa din?"fuskarshi a sake kaman zaiyi dariya ya d'aga mata kai don yadda ta firgitan taso bashi dariya,
a rud'e ta kuma cewa"to amman ai ni fa ban iya irin turancinsu ba mai saurin nan,ba rannan na fad'a maka ba har kace zaka koya man amman sai ka samu isashshen lokaci to yanzu ya zanyi magana da ita....."kafin ta k'arasa budurwar ta katseta da fad'in,
"karki damu nima bahaushiya ne ai" yadda tayi hausar gwanin dad'i,da sauri Fatuu ta maida kallonta gareta lokacin ta gama shan ruwa ta juyo da fuskarta sosae,Tubarkallah Ma sha Allah,kallo daya zakai mata ka shaida kyawun fuskarta,kyakkyawa ce matuk'a ga kwayar idonta brown ce har wani kyalli take,waro ido Fatuu tayi tana kallonta arazane,ba kyawunta ne kad'ai ya razana ta ba, harda furucin da tayi na wai itama bahaushiya ce to ta yaya?shine abunda ya tsaya ma fatun arai.
Hannu ta d'aga ma Fatuu"hi,Zarah how're u?",
Cike da mamaki fatuu tace"da gaske ke bahaushiya ce?"
"Yeah,kuma ina jin hausa kaman jakin kano ba" tayi Maganar tana dariya haka kuma ba k'aramin kyau ya k'ara mata ba,kan fatuu fa ya Matuk'ar daurewa hannu guda tasa ta rufe bakinta alamar mamaki kafin tace"wai har sunan jaki ma kin sani kenan!",ba budurwar ba har Haisam dake saurararsu saida ya d'an murmusa,
"Na fad'a maki nima bahaushiya ne ko baki yarda ba,nasan komae ai saboda nima yar Nigeria ne, anan aka haifeni, anan nayi wayo har na girma",
kai abunfa nayi ne,neman wurin zama Fatuu ta fara don da a duk'e take tayi ruku'u,ganin haka yasa Haisam janye kafarsa daya mik'e kan kujeran ya matsa can gefe,zama tayi sosae tace"to ke wacece,kuma wane gari kike ko ke yar gidansu Ya Handsome ce amman kuma naga ba kalarku daya ba"duk ta jero mata tambayoyin nan,
Murmushi tayi tasa hannunta tana gyara gefe da gefen gashinta kafin ta fara magana"sunana FANAN,ni yar Lagos ne and ni kanwarsa ce but am his Cousin sis kinsan me cousin ke nufi ko?"da sauri Fatuu ta d'aga mata kai"Eh nasani anyi mana shi a English,diya ko dan kanin ko yayan iyayen Mutum",