Sashe 75
Asanadin Makwabtaka Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Banyi daidai ba ko Ya Handsome?" murya na rawa ta tambayeshi,daga yadda yake yace"check your book"da sauri ta nufi saman Desk inda ta aje littafinta ta d'aukko shi ta dawo gaban allon tana duba amsar data samo da wadda Malamin Maths d'in ya bata,sai ta kalli cikin littafin sai ta d'ago ta kalli allon,wata uwar k'ara ta fasa ta daka uban tsalle kai kace zata ta6o ceiling d'in dakin ne,cike da farinciki ta fara fad'in"Wllh iri d'aya ne,nayi daidai...."sai faman tsalle take wutsiyoyin kitsonta na tashi sama suma,sai lokacin ya saki wani k'ayataccen Murmushi ya sauke hannayenshi daga kan kirjin ya d'an had'a tafin hannunshi ya tafa mata sau ukku kafin ya saka yatsun cikin na juna yana ci gaba da kallonta da d'an murmushi,(Jama'a wai Fatuu bata san ta fara girma bane wannan uban tsalle haka,yakamata team Fatuu kuyi mata karatun ta natsu fa😂),cike da murna tanata dariya duk dimples dinta sun lotsa sosae ta nufi haisam dake zaune yana kallonta,tana zuwa ta d'aga mashi hannu alamar su tafa,d'an bud'a mata ido yayi had'i da dage gira hakan yasa da sauri tasa bayan hannunta ta rufe bakinta,ganin yana mata wani kallo yasa ta sunnar da kai k'asa alamar taji kunya,
"Zarah!" taji ya kira sunanta,koda ta d'ago abun mamaki sai taga ya bud'e mata tafin hannunshi fari kwal dashi,bud'a ido tayi alamar mamaki shi kuma ya d'an lumshe nashi had'i da jinjina mata kai,washe baki tayi ta buda tafin hannunta na dama ta buga a nashin da k'arfi ji kake fasss har saida ya d'an cije baki,tana ganin abunda yayi ta kyalkyace da dariya tace"thank u,God bless u Sweethrt"girgiza kai kawae yayi tare da mikewa,
"Ki copying solution d'in Magrib ya kusa" daga haka ya fita daga cikin d'akin,da sauri ta d'aukko littafinta da tuni ya fad'i a k'asa da tana tsalle ta zauna saman kujeran ta fara kwafar rubutun kaman yadda yace mata tana yi tana sakin Murmushi,
Yana fita fridge ya nufa ya daukko bottle water mai sanyi da glass cup ya nufi kujera ya zauna inda ya tashi lokacin da Fatuu ta shigo,tsiyaya ruwan yayi kaman rabin cup d'in kafin ya rufe robar ya kai cup d'in baki ya fara shan ruwan ahankali,yana niyyar aje robar ruwan akan c-table Fatuu ta fito har ta gama kwafar rubutun dama saurin rubutu ne da ita,kan d'aya daga cikin armchairs ta zauna idonta akanshi,
"Ko zaki sha ne?" ya tambayeta bayan ya cire cup d'in ta d'aga mashi kai alamar eh, sauran na cikin robar ya mik'o mata ta mike ta kar6o kafin ta dawo ta zauna,
"Ki d'aukko cup acikin fridge" girgiza mashi kai tayi"ai shanye shi zanyi bari insha a robar" kai ya gyad'a mata shiru ya biyo baya na d'an wani lokacin,
"Wai Ya Handsome kodae kaima malami ne naga ka iya bayani fa sosae"girgiza mata kai yayi alamar a'a,ganin tana ta binshi da ido yasashi cewa" hakan is part of my work,ina yawan presentation kinsan miye hakan ko?"ya tambayeta idonshi akanta,d'aga mashi kai tayi"eh yima mutane bayani"jinjina kai yayi daga haka ya d'aura kafarsa d'aya akan c-table d'in gabanshi ya d'age kanshi yana facing saman d'akin,duk jinshi ake wani iri ya saba kaman yanzu yana gym,
"Ya Handsome" Fatuu ta kira shi,amsa mata yayi ba tare daya d'ago ba,
"In tambayeka?" ta sake cewa,shiru ya d'an yi ya maimaita abunda ta fad'an acikin ranshi,saboda duk in zata tambayeshi kai tsaye take jefo mashi kowacce irin tambaya,daga yadda yake ya d'an juyo da fuskarshi side d'in da take,
"Am all ears" ya fad'a,
"Wai don Allah da wane irin dutsen goge kaushi kake amfani ne kafanka tayi haka kaman ta jarirai sumul ba kaushi?" ta k'arasa tana nuna kafarshi da ya d'aura saman c-table, kai jama'a ashe tunda ya dauran ta k'ura ma k'afar ido tanata kallonta har ta kasa daurewa saida ta tambaya, shi kuma sam bai gane ma mi take nufi ba,ganin tanata kallonshi yasa shi ce mata"miye shi abun da kika fad'in?"idanunshi a lumshe ya tambaya,
"Dutsen goge kaushin kake nufi?" kai ya d'aga mata alamar eh,
"Wannan fa dutsen mai gurjigurji wanda ake sakawa acikin kwandon wanka ana gurje tafin k'afa dashi mai kaushi ko faso"tayi maganar tana kwatanta mashi yadda ake goge k'afan dashi da tafin kafanta da ta d'an d'age sama,still idanunshi alumshe suke ahakan yake kallonta,yanzu ya gane abunda take nufi duk da shi bai san ma dutsen ba,
"kina son abunne?"da sauri ta girgiza mashi kai "a'a bani ke so ba Kawu Amadu zan sai ma irin nakan k'ilan ya gyara mashi k'afarshi ta koma kaman taka, wllh baka ga kafarshi bafa, ina...kasan dawon fura in ya kwana,to haka k'afarshi ke komawa cikin sanyi haka zaka ga yanata dirzarta a gefen inda nike yin wanke wanke,har wani k'aton dutsen goge kaushi gwaggo ta siyo mashi a kasuwar yar kutungu yana amfani dashi,kwanaki fa cewa tayi in kafarshi nayin hakan in yayi Amarya zai rinka yaga mata zanin gado"ta k'arasa tana 6a66aka Dariya,d'an bud'e idanun yayi yana kallonta fuskarshi d'auke da dan guntun Murmushin gefen baki,
"Shiyasa na tambayekan in ka fad'i man inda ka siyo naka sai in siyo mashi k'ilan ta daina tunda ni dai banso yayi Amarya ya yaga mata zanen gado kuma in ta canja wani taga ya k'ara yaga mata ai kaga tana iya yin yaji ko?" tsakaninta da Allah take yin Maganar😂,
d'ago kan yayi gaba d'aya daga saman bayan kujeran yace mata"bani amfani da abun ina kaita ana wanke man ne" wata zabura tayi ta zaro ido tace "kafan kake kaiwa wanki sai kace kayan wanki!" tayi maganar hannunta guda ruk'e da ha6arta alamar mamaki,kai ya d'aga mata kafin yayi mata bayanin yadda ake pedicure d'in,cike da Al'ajabi take kallonshi hakan yasa ya d'age mata gira"zaki kaishi arika wanke mashi kafan ko?" a razane tace "wa!ba ruwana wllh,ban shirya zuwa gidan yari ba,haka kawae muje kafan tashi ta lalata masu inji ace sai na biya miliyoyi,ai ma yanzu ta d'an gyaru tunda zafi ake sai sanyi yazo take tsatstsagewan sosae zan dai gaya mashi in yana so to sai yaje amman ba ruwana ni dai" tana Maganar tana d'aga hannuwa sama alamar ba ruwanta,gyad'a kai yayi kawae yana niyyar k'ara kwantar da kan nashi aka fara kwala kiran sallar magrib hakan yasa ya dakata,
"kije gida kiyi salla sai ki kara duba Assignment d'in karki manta ko" kallonshi tayi ta d'an marairaice "to ai yanzu gwaggo bata isa dawowa ba, kuma wllh in na koma kakkarya ni kawu Amadu zaiyi kaman kara dama ya ta6a gota ni a hannu,kofa Gwaggon na nan yana buguna balle yanzu da bata nan"shiru baice komae ba can ya mik'e tsaye yana gyara rigarshi ta daga kai tana kallonshi,
"Ki jira in dawo" yace mata ganin bata da kallabi kuma magriba tayi bai kamata ta fita haka ba,da sauri tace mashi toh tana gyara zamanta,Bedroom d'inshi ya nufa yayo alwala,yana fitowa zai wuce tace ya kunna mata kallo,remote ya dauka asaman c-table ya latsa power daga haka ya mik'a mata ya fita.
Ana gama sallan ba 6ata lokaci ya dawo part din nashi,lokacin daya shigo parlon iske Fatuu yayi ta baje a d'ayan 6arin L-shape sai sharar bacci take,(nima inyi ta hajiya ja'ira ta gaji),dama tun agida take jin baccin amman tak'i yi saboda rashin yin Assignment,tsaye yayi tsakiyan falon yana kallonta yayinda ya shiga tunanin yadda zaiyi da ita don fita yake son yi gashi da gani tana enjoying baccin,tunanin ko ya barta yaje ya dawo ya shiga yi sai kuma yayi tunanin za'a iya zuwa nemanta wurin hajiya kuma bata san har yanzu tana wurinshi ba kuma ma is'nt proper taci gaba da zama anan wannan lokacin, yin wannan tunanin yasashi fara kiran sunanta daga nan inda yake atsaye sai dai ko motsi bata yi ba tun yana kiran ahankali har ya d'an k'ara d'aga murya amman ina tuni sanyin Ac yasa tayi nisan kiwo acikin barcin da alama ma bata Nigeria,d'an k'ara matsawa yayi gabanta ya k'ara kiran sunanta nan ma shiru,still yayi da alama baison zuwa kusa da ita ne balle yasa hannu ya tasheta,har zai juya yaga ta motsa zata gyara kwanciya da d'an karfi ya furta"Zarahh"slowly idanunta suka fara bud'ewa suna kuma d'an lumshewa duk alokaci d'aya alamar dae baccin take ji sosae, yana ganin zata juya mashi baya ya sake kiranta wannan karon da k'arfi yace"Zarah!" amsawa tayi tare da bud'e idon sosae cikin Muryar bacci tace"Na'amm",
"Tashi muje na raka ki gida" amsawa tayi da toh ta fara k'okarin tashi zaune idonta akanshi tace"wai bacci nayi?"kai ya daga mata alamar eh,
"Wllh bansan ma nayi ba,kallo fa nike yi shine ya sace ni shiyasa ma ake ce mashi 6arawo ashe"da wata irin kasalallar murya take maganar,d'an murmushin gefe yayi yace"tashi muje",
"Gidan zaka kaini" kai ya d'aga mata alamar eh,
"To amman fa gwaggon bata isa dawowa ba yanzunma kar kawun ya dokeni",
"zamu je sai ki bashi hakuri",da sauri ta jinjina kai ta fara k'okarin tashi tsaye,har zai nufi kopar fita sai kuma ya juya yace mata yana zuwa,Bedroom d'inshi ya nufa bada jimawa ba ya fito lokacin har ta zauna don jikinta ba kwari,hannunshi ruke da wani bakin abu ya nufi inda take,mik'a mata yayi"kisa wannan akan ki" amsa tayi tana dubawa,hula ce skullcap irin mai matse kai,sawa tayi akanta kuma tayi mata da yake roba ce,kallonshi tayi tana da murmushi tace"thank u Sweethrt ya handsome"d'an kya6e baki yayi da Murmushi ya nuna mata hanya alamar su tafi, saida ta d'auki littafinta data aje kan armchair kafin ta wuce yabi bayanta suka fita daga parlon.
"Zarah!" taji ya kira sunanta,koda ta d'ago abun mamaki sai taga ya bud'e mata tafin hannunshi fari kwal dashi,bud'a ido tayi alamar mamaki shi kuma ya d'an lumshe nashi had'i da jinjina mata kai,washe baki tayi ta buda tafin hannunta na dama ta buga a nashin da k'arfi ji kake fasss har saida ya d'an cije baki,tana ganin abunda yayi ta kyalkyace da dariya tace"thank u,God bless u Sweethrt"girgiza kai kawae yayi tare da mikewa,
"Ki copying solution d'in Magrib ya kusa" daga haka ya fita daga cikin d'akin,da sauri ta d'aukko littafinta da tuni ya fad'i a k'asa da tana tsalle ta zauna saman kujeran ta fara kwafar rubutun kaman yadda yace mata tana yi tana sakin Murmushi,
Yana fita fridge ya nufa ya daukko bottle water mai sanyi da glass cup ya nufi kujera ya zauna inda ya tashi lokacin da Fatuu ta shigo,tsiyaya ruwan yayi kaman rabin cup d'in kafin ya rufe robar ya kai cup d'in baki ya fara shan ruwan ahankali,yana niyyar aje robar ruwan akan c-table Fatuu ta fito har ta gama kwafar rubutun dama saurin rubutu ne da ita,kan d'aya daga cikin armchairs ta zauna idonta akanshi,
"Ko zaki sha ne?" ya tambayeta bayan ya cire cup d'in ta d'aga mashi kai alamar eh, sauran na cikin robar ya mik'o mata ta mike ta kar6o kafin ta dawo ta zauna,
"Ki d'aukko cup acikin fridge" girgiza mashi kai tayi"ai shanye shi zanyi bari insha a robar" kai ya gyad'a mata shiru ya biyo baya na d'an wani lokacin,
"Wai Ya Handsome kodae kaima malami ne naga ka iya bayani fa sosae"girgiza mata kai yayi alamar a'a,ganin tana ta binshi da ido yasashi cewa" hakan is part of my work,ina yawan presentation kinsan miye hakan ko?"ya tambayeta idonshi akanta,d'aga mashi kai tayi"eh yima mutane bayani"jinjina kai yayi daga haka ya d'aura kafarsa d'aya akan c-table d'in gabanshi ya d'age kanshi yana facing saman d'akin,duk jinshi ake wani iri ya saba kaman yanzu yana gym,
"Ya Handsome" Fatuu ta kira shi,amsa mata yayi ba tare daya d'ago ba,
"In tambayeka?" ta sake cewa,shiru ya d'an yi ya maimaita abunda ta fad'an acikin ranshi,saboda duk in zata tambayeshi kai tsaye take jefo mashi kowacce irin tambaya,daga yadda yake ya d'an juyo da fuskarshi side d'in da take,
"Am all ears" ya fad'a,
"Wai don Allah da wane irin dutsen goge kaushi kake amfani ne kafanka tayi haka kaman ta jarirai sumul ba kaushi?" ta k'arasa tana nuna kafarshi da ya d'aura saman c-table, kai jama'a ashe tunda ya dauran ta k'ura ma k'afar ido tanata kallonta har ta kasa daurewa saida ta tambaya, shi kuma sam bai gane ma mi take nufi ba,ganin tanata kallonshi yasa shi ce mata"miye shi abun da kika fad'in?"idanunshi a lumshe ya tambaya,
"Dutsen goge kaushin kake nufi?" kai ya d'aga mata alamar eh,
"Wannan fa dutsen mai gurjigurji wanda ake sakawa acikin kwandon wanka ana gurje tafin k'afa dashi mai kaushi ko faso"tayi maganar tana kwatanta mashi yadda ake goge k'afan dashi da tafin kafanta da ta d'an d'age sama,still idanunshi alumshe suke ahakan yake kallonta,yanzu ya gane abunda take nufi duk da shi bai san ma dutsen ba,
"kina son abunne?"da sauri ta girgiza mashi kai "a'a bani ke so ba Kawu Amadu zan sai ma irin nakan k'ilan ya gyara mashi k'afarshi ta koma kaman taka, wllh baka ga kafarshi bafa, ina...kasan dawon fura in ya kwana,to haka k'afarshi ke komawa cikin sanyi haka zaka ga yanata dirzarta a gefen inda nike yin wanke wanke,har wani k'aton dutsen goge kaushi gwaggo ta siyo mashi a kasuwar yar kutungu yana amfani dashi,kwanaki fa cewa tayi in kafarshi nayin hakan in yayi Amarya zai rinka yaga mata zanin gado"ta k'arasa tana 6a66aka Dariya,d'an bud'e idanun yayi yana kallonta fuskarshi d'auke da dan guntun Murmushin gefen baki,
"Shiyasa na tambayekan in ka fad'i man inda ka siyo naka sai in siyo mashi k'ilan ta daina tunda ni dai banso yayi Amarya ya yaga mata zanen gado kuma in ta canja wani taga ya k'ara yaga mata ai kaga tana iya yin yaji ko?" tsakaninta da Allah take yin Maganar😂,
d'ago kan yayi gaba d'aya daga saman bayan kujeran yace mata"bani amfani da abun ina kaita ana wanke man ne" wata zabura tayi ta zaro ido tace "kafan kake kaiwa wanki sai kace kayan wanki!" tayi maganar hannunta guda ruk'e da ha6arta alamar mamaki,kai ya d'aga mata kafin yayi mata bayanin yadda ake pedicure d'in,cike da Al'ajabi take kallonshi hakan yasa ya d'age mata gira"zaki kaishi arika wanke mashi kafan ko?" a razane tace "wa!ba ruwana wllh,ban shirya zuwa gidan yari ba,haka kawae muje kafan tashi ta lalata masu inji ace sai na biya miliyoyi,ai ma yanzu ta d'an gyaru tunda zafi ake sai sanyi yazo take tsatstsagewan sosae zan dai gaya mashi in yana so to sai yaje amman ba ruwana ni dai" tana Maganar tana d'aga hannuwa sama alamar ba ruwanta,gyad'a kai yayi kawae yana niyyar k'ara kwantar da kan nashi aka fara kwala kiran sallar magrib hakan yasa ya dakata,
"kije gida kiyi salla sai ki kara duba Assignment d'in karki manta ko" kallonshi tayi ta d'an marairaice "to ai yanzu gwaggo bata isa dawowa ba, kuma wllh in na koma kakkarya ni kawu Amadu zaiyi kaman kara dama ya ta6a gota ni a hannu,kofa Gwaggon na nan yana buguna balle yanzu da bata nan"shiru baice komae ba can ya mik'e tsaye yana gyara rigarshi ta daga kai tana kallonshi,
"Ki jira in dawo" yace mata ganin bata da kallabi kuma magriba tayi bai kamata ta fita haka ba,da sauri tace mashi toh tana gyara zamanta,Bedroom d'inshi ya nufa yayo alwala,yana fitowa zai wuce tace ya kunna mata kallo,remote ya dauka asaman c-table ya latsa power daga haka ya mik'a mata ya fita.
Ana gama sallan ba 6ata lokaci ya dawo part din nashi,lokacin daya shigo parlon iske Fatuu yayi ta baje a d'ayan 6arin L-shape sai sharar bacci take,(nima inyi ta hajiya ja'ira ta gaji),dama tun agida take jin baccin amman tak'i yi saboda rashin yin Assignment,tsaye yayi tsakiyan falon yana kallonta yayinda ya shiga tunanin yadda zaiyi da ita don fita yake son yi gashi da gani tana enjoying baccin,tunanin ko ya barta yaje ya dawo ya shiga yi sai kuma yayi tunanin za'a iya zuwa nemanta wurin hajiya kuma bata san har yanzu tana wurinshi ba kuma ma is'nt proper taci gaba da zama anan wannan lokacin, yin wannan tunanin yasashi fara kiran sunanta daga nan inda yake atsaye sai dai ko motsi bata yi ba tun yana kiran ahankali har ya d'an k'ara d'aga murya amman ina tuni sanyin Ac yasa tayi nisan kiwo acikin barcin da alama ma bata Nigeria,d'an k'ara matsawa yayi gabanta ya k'ara kiran sunanta nan ma shiru,still yayi da alama baison zuwa kusa da ita ne balle yasa hannu ya tasheta,har zai juya yaga ta motsa zata gyara kwanciya da d'an karfi ya furta"Zarahh"slowly idanunta suka fara bud'ewa suna kuma d'an lumshewa duk alokaci d'aya alamar dae baccin take ji sosae, yana ganin zata juya mashi baya ya sake kiranta wannan karon da k'arfi yace"Zarah!" amsawa tayi tare da bud'e idon sosae cikin Muryar bacci tace"Na'amm",
"Tashi muje na raka ki gida" amsawa tayi da toh ta fara k'okarin tashi zaune idonta akanshi tace"wai bacci nayi?"kai ya daga mata alamar eh,
"Wllh bansan ma nayi ba,kallo fa nike yi shine ya sace ni shiyasa ma ake ce mashi 6arawo ashe"da wata irin kasalallar murya take maganar,d'an murmushin gefe yayi yace"tashi muje",
"Gidan zaka kaini" kai ya d'aga mata alamar eh,
"To amman fa gwaggon bata isa dawowa ba yanzunma kar kawun ya dokeni",
"zamu je sai ki bashi hakuri",da sauri ta jinjina kai ta fara k'okarin tashi tsaye,har zai nufi kopar fita sai kuma ya juya yace mata yana zuwa,Bedroom d'inshi ya nufa bada jimawa ba ya fito lokacin har ta zauna don jikinta ba kwari,hannunshi ruke da wani bakin abu ya nufi inda take,mik'a mata yayi"kisa wannan akan ki" amsa tayi tana dubawa,hula ce skullcap irin mai matse kai,sawa tayi akanta kuma tayi mata da yake roba ce,kallonshi tayi tana da murmushi tace"thank u Sweethrt ya handsome"d'an kya6e baki yayi da Murmushi ya nuna mata hanya alamar su tafi, saida ta d'auki littafinta data aje kan armchair kafin ta wuce yabi bayanta suka fita daga parlon.