Sashe 39
Asanadin Makwabtaka Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Tunda ta fito zata tafi makaranta take kallon gidan hajiya ji take kaman taje sai dai tasan kawu Amadu sai ya tambayi abunda zata je yi tun da safe kuma lokacin tafiya makaranta,hakan yasa ta mik'i hanya kawai don biya ma haulatu,
Tana tafiya tana waiwayen bayanta wai ko zata hango Haisam ya taho a mota amman har ta kawo lungun su haulat bata ga wata mota ta taho ba balle tasa ran shine,lokaci guda gabanta ya fara fad'uwa ta fara tunani a ranta ko dai saboda ciwon da yaji jiya ne yasa bai fito ba,a fili tace"kar fa kuma ya dawo yace bai yafe gilashin ba saboda nasa yaji ciwo,daman naga sai d'aure fuska yake jiyan..." jikinta ne yayi mugun sanyi ta shiga damuwar da har fuskarta ta bayyana,
Tana zuwa kopar gidan haulatun ta fito,fuskarta d'auke da dan murmushi tace"ashe kin taho har inata sauri inje mutaho tare..." kasa karasa maganar tayi saboda yanayin fuskar fatun da ta gani,a hankali tace"miya faru kawata?baki je kin basa hakurin bane ?",
"ba komai,mu tafi karmu makara" daga haka ta wuce gaba,bin bayanta Haulat tayi jiki asanyaye tana ta faman tunane-tunane cikin ranta.
Har akayi masu break fatuu bata saki jikinta ba duk ta shiga damuwa ganin duk yan ajin sun fita yin break fatun na a zaune yasa haulat tace mata"ki taso muje muyi break fatuu" kifa fuskarta tayi saman desk tace"ki tafi kawai bana jin yunwa" jin hakan yasa Haulat da har ta mik'e komawa ta zauna,hannu tasa ta d'an bubbugi bayan fatun tace"wai miyake damunki ne,kodai mutumin cewa yayi bazai yafe bane?kinji ki fada man"
Dagowa tayi fuskarta a d'aure tace"wai bana ce maki ba komai ba,ki kyale ni kije kiyi break dinki" daga haka ta sake maida kanta ta kifa a saman desk din.
Shiru Haulat tayi,sai taji duk zuwa break din ma ya fita ranta dama kuma naira ashirin ce da ita,can ta mike da niyyar zuwa ta siyo ruwa saboda kishin da ta fara ji, "Haulat" taji fatuu ta kira sunanta,a hankali ta juya ta kalleta fuskarta a dan d'aure don bata ji dadin abunda fatun tayi mata ba,kudi fatun ta mik'o mata,kallon kudin tayi kafin ta kalli fatun tace"mi zan siyo maki?",
girgiza kai tayi"ba komai ki had'a kiyi break"shiru Haulat tayi duk da bata da isassun kudi amma tace"a'a ki barshi"daga haka ta juya,
"Fushi kika yi?" fatuu ta jefo mata tambaya,banza ta mata taci gaba da tafiya,ganin hakan yasa da sauri fatuu tace"ki yi hakuri to...."tsayawa da yin tafiyar haulat tayi ta juya ta d'an kalli fatun hakan yasa ta cigaba"banje na bashi hakurin bane shiyasa kika ga duk na damu,tsoro na yau Monday kada maganar Gaye ta tabbata" sai da kirjinta ya buga data ambaci sunan gayen,ita kuwa Haulat jin hakan yasa ta koma inda fatun take ta tsaya a gaban desk din tace"to kuma sai inta faman tambayarki ki k'i gaya man abunda ke damunki",
"to ai nace kiyi hakuri ko" fatun tace,
"Shikenan,in sha Allahu ba abunda zai faru ma,yanzu ki taso muje muyi break din,alabashshi da yamma in aka taso mu islamiyya sai muje tare mu bashi hakurin,nasan in Allah ya yarda zai hakura" mik'ewa fatuu tayi har ta fito daga cikin seat d'in ta koma ta janyo jakarta,bude ciki tayi ta fiddo lemun da Haisam ya bata daga haka suka fuce.
*** *** *** ***
Wuraren karfe 9 na safe Haisam ya farka daga bacci tun bayan da yayi sallan Asuba anan cikin dakinsa,yana farkawa kiran Hajiya ya shigo wayarsa don tana ta kiran telephone bai dauka ba sai tayi tunanin ko bai tashi bane,ganin lokaci nata tafiya yasa ta kira wayarsa,bayan ya d'aga kiran sun gaisa take tambayar ko ya wuce wurin aiki ne,don bata ga yaje sun gaisa ba kaman yadda yake yi kullum kafin ya tafi don bai cika yin breakfast ba a cewarshi yayi safiya da yawa,sai hajiyan ta matsa masa ne ma wani lokacin yake shan tea kawae,sanar mata yayi cewa yana nan bai tafi ba bada wuri zai je bane,in ya gama abunda yake zai shigo.
Toilet ya nufa don yin wanka bayan ya gama ya shirya cikin wata navy blue jallabiya mai gajeran hannu ya fito falo hannunsa rike da wayarsa yana d'an dangyasa kafan mai ciwo ya nufi kujera ya zauna,fara latsa wayan yayi ya kira Tk,yana d'aga kiran yace"t.k are u at home?" da sauri t.k yace "a'a wllh na tafi skul.."kafin ya k'ara cewa wani abu Haisam ya katse kiran,d'an kwantar da kansa yayi yana tunanin yadda zai tafi asibiti, don jiya da tsakan dare kafan ya takura masa da zogi duk da pain reliever din da ya sha,sai wuraran asubahi ya samu yin bacci sosae,duk motocin da zai yi amfani dasu manual ne dole sai yayi amfani da kafan mai ciwo in zai tuka su,gashi a yadda yake jin kafan ba zai iya yin tuki da ita ba.
Bayan wani lokaci ya mik'e, komawa yayi cikin corridor yasa takalma slippers kafin ya dawo cikin parlon ya fuce,wajen gate ya nufa ta k'aramar kopa ya fita,tunkarar Officer CD dake zaune saman benci shi kadai yayi,Officern na ganin haisam din ya tunkaro sa yana d'angyasa kafa ya mike da sauri ya nufo sa yana zuwa wurinsa yace"yalla6ai barka da safiya..."hannu haisam ya mik'a masa suka gaisa kafin yaci gaba"yalla6ai rauni ka ji haka?" d'aga masa kai kawai yayi,cike da jajantawa Officer ya shiga girgiza kai yana fad'in"wai sannu,Allah ya kyauta gaba" "Amin" haisam ya amsa kafin yace"in ba damuwa inason zaka kaini hospital ne,sai dai motan is manual I don't know if u could drive it" ya tambaye shine don yasan ba kowa ya iya tuka mota manual ba,
d'an sosa k'eya Officern yayi yana d'an murmushi yace"wllh yalla6ai kwata kwata ma ni ban iya tukin mota ba.." d'age gira haisam yayi yace"really?" Officer dake ta murmushi ya daga masa kai alamar eh kafin yace"sai dai ko in ma Officer Jamil magana don shi ya iya tuka mota don wani lokacin ma yakan fita da Hajiya in t.k baya nan" jinjina kai Haisam yayi yace"ok bari in koma ciki in yazo sai kayi masa magana..."da sauri Officer ya katseshi"ai yana nan,ya shiga ciki ya kimtsa da yake ba dashi mukai aikin dare ba bai jima da zuwa ba,bari in masa magana" ya k'arasa maganar tare da juyawa ya nufi cikin gidan,
Ba da jimawa ba suka fito atare Officer police ne Jamilun da aka kira ya nufo haisam yana gyara hulansa yana zuwa ya mika mashi hannu suka gaisa yace"yalla6ai ashe tsautsai ka had'u dashi" d'aga masa kai kawai yayi yace"to Allah ya kiyaye gaba" a hankali haisam yace"Amin",
"Yauwa wani motan za'a fiddo ne?Nura yace kana so a kaika asibiti" daga masa kai haisam yayi tare da mika masa makullin mota dake rike a hannunsa na hagu" amsar key d'in Officer jamil yayi ya d'an duba shi kafin ya juya don fiddo motan,Officer Nura kuma ya fara sliding gate din,ba 6ata lokaci ya fito da motan Haisam ya shiga suka tafi.
Wuraren karfe biyu na rana gwaggo na zaune a tsakan gida jikinta sanye da kayan aiki ita da wata mata dukkansu suna zaune a saman kujera yar tsugunno da alama bak'uwa tayi,da gudu fatuu ta shigo daga bakin kopar shigowan ta wurgo jakarta tsakar gida tayi bandaki da gudu,gaba dayansu sai da suka tsorata bakuwar matar ce ta juya ta kalli gwaggon tace"kaman fatima ko?" girgiza kai gwaggo tayi ta d'an ta6e baki tace"itace wllh,haka take don iskanci sai ta tara matsuwa,maimakon tun can makarantar tasan tana ji tayi"
Yar dariya matar tayi tace"ina ruwan fatuu" adaidai lokacin fatun ta fito tana gyara wandonta ta duk'a inda jakarta take ta dauka ta wuce ciki,kallon bakuwar tayi tace"Ladidi mai waina ina yini" amsawa tayi"lafiya lau fatima yan makaranta" kallon Gwaggo tayi tace"sannu da gida gwaggo" yar harararta gwaggon tayi batare da ta amsa mata ba,hakan yasa fatuu yin dariya ta wuce d'aki don tasan hararar ta shigowar da tayi da gudu ce,
"....Oh ladidi kina fadi man wannan al'amari mai cike da tashin hankali" ladidin ta kar6e"wllh bari,ni fa ina cikin tuyan waina da safe naji yara suna cewa wai gashi can an zo kama Gaye nace wane gayen? wai Ashiru d'an gidan Malam Tanimu,shine fa su Bilki suka fita don jin ba'asi nidai bansamu fita ba saboda tuyan wainan da nike,da suka dawo ne suke ban labarin wai yunkurin fyade su kai ma wata jiya da daddare shi da abokanansa Allah baisa sun kaiga yin nasarar aikatawan ba wani mutumi ya gansu,ance ma tun jiya da daddaren yan sanda suka zo neman shi basu same shi agida ba shine suka fad'a ma mahaifinsa mlm tanimun laifin da ake tuhumar d'an nasa,suka kuma bukaci ya basu hadin kai da zarar yaron ya dawo gida ya kira su ya sanar dasu kuma kar ya bari ya fita in ba haka ba zasu dawo su kamashi tare da mahaifiyar Ashirun wato Zulai,aikam yau da safe sai gashi ya dawon don bai kwana a gida ba,yana ko zuwa malam tanimun ya kira yan sandan"
Tana tafiya tana waiwayen bayanta wai ko zata hango Haisam ya taho a mota amman har ta kawo lungun su haulat bata ga wata mota ta taho ba balle tasa ran shine,lokaci guda gabanta ya fara fad'uwa ta fara tunani a ranta ko dai saboda ciwon da yaji jiya ne yasa bai fito ba,a fili tace"kar fa kuma ya dawo yace bai yafe gilashin ba saboda nasa yaji ciwo,daman naga sai d'aure fuska yake jiyan..." jikinta ne yayi mugun sanyi ta shiga damuwar da har fuskarta ta bayyana,
Tana zuwa kopar gidan haulatun ta fito,fuskarta d'auke da dan murmushi tace"ashe kin taho har inata sauri inje mutaho tare..." kasa karasa maganar tayi saboda yanayin fuskar fatun da ta gani,a hankali tace"miya faru kawata?baki je kin basa hakurin bane ?",
"ba komai,mu tafi karmu makara" daga haka ta wuce gaba,bin bayanta Haulat tayi jiki asanyaye tana ta faman tunane-tunane cikin ranta.
Har akayi masu break fatuu bata saki jikinta ba duk ta shiga damuwa ganin duk yan ajin sun fita yin break fatun na a zaune yasa haulat tace mata"ki taso muje muyi break fatuu" kifa fuskarta tayi saman desk tace"ki tafi kawai bana jin yunwa" jin hakan yasa Haulat da har ta mik'e komawa ta zauna,hannu tasa ta d'an bubbugi bayan fatun tace"wai miyake damunki ne,kodai mutumin cewa yayi bazai yafe bane?kinji ki fada man"
Dagowa tayi fuskarta a d'aure tace"wai bana ce maki ba komai ba,ki kyale ni kije kiyi break dinki" daga haka ta sake maida kanta ta kifa a saman desk din.
Shiru Haulat tayi,sai taji duk zuwa break din ma ya fita ranta dama kuma naira ashirin ce da ita,can ta mike da niyyar zuwa ta siyo ruwa saboda kishin da ta fara ji, "Haulat" taji fatuu ta kira sunanta,a hankali ta juya ta kalleta fuskarta a dan d'aure don bata ji dadin abunda fatun tayi mata ba,kudi fatun ta mik'o mata,kallon kudin tayi kafin ta kalli fatun tace"mi zan siyo maki?",
girgiza kai tayi"ba komai ki had'a kiyi break"shiru Haulat tayi duk da bata da isassun kudi amma tace"a'a ki barshi"daga haka ta juya,
"Fushi kika yi?" fatuu ta jefo mata tambaya,banza ta mata taci gaba da tafiya,ganin hakan yasa da sauri fatuu tace"ki yi hakuri to...."tsayawa da yin tafiyar haulat tayi ta juya ta d'an kalli fatun hakan yasa ta cigaba"banje na bashi hakurin bane shiyasa kika ga duk na damu,tsoro na yau Monday kada maganar Gaye ta tabbata" sai da kirjinta ya buga data ambaci sunan gayen,ita kuwa Haulat jin hakan yasa ta koma inda fatun take ta tsaya a gaban desk din tace"to kuma sai inta faman tambayarki ki k'i gaya man abunda ke damunki",
"to ai nace kiyi hakuri ko" fatun tace,
"Shikenan,in sha Allahu ba abunda zai faru ma,yanzu ki taso muje muyi break din,alabashshi da yamma in aka taso mu islamiyya sai muje tare mu bashi hakurin,nasan in Allah ya yarda zai hakura" mik'ewa fatuu tayi har ta fito daga cikin seat d'in ta koma ta janyo jakarta,bude ciki tayi ta fiddo lemun da Haisam ya bata daga haka suka fuce.
*** *** *** ***
Wuraren karfe 9 na safe Haisam ya farka daga bacci tun bayan da yayi sallan Asuba anan cikin dakinsa,yana farkawa kiran Hajiya ya shigo wayarsa don tana ta kiran telephone bai dauka ba sai tayi tunanin ko bai tashi bane,ganin lokaci nata tafiya yasa ta kira wayarsa,bayan ya d'aga kiran sun gaisa take tambayar ko ya wuce wurin aiki ne,don bata ga yaje sun gaisa ba kaman yadda yake yi kullum kafin ya tafi don bai cika yin breakfast ba a cewarshi yayi safiya da yawa,sai hajiyan ta matsa masa ne ma wani lokacin yake shan tea kawae,sanar mata yayi cewa yana nan bai tafi ba bada wuri zai je bane,in ya gama abunda yake zai shigo.
Toilet ya nufa don yin wanka bayan ya gama ya shirya cikin wata navy blue jallabiya mai gajeran hannu ya fito falo hannunsa rike da wayarsa yana d'an dangyasa kafan mai ciwo ya nufi kujera ya zauna,fara latsa wayan yayi ya kira Tk,yana d'aga kiran yace"t.k are u at home?" da sauri t.k yace "a'a wllh na tafi skul.."kafin ya k'ara cewa wani abu Haisam ya katse kiran,d'an kwantar da kansa yayi yana tunanin yadda zai tafi asibiti, don jiya da tsakan dare kafan ya takura masa da zogi duk da pain reliever din da ya sha,sai wuraran asubahi ya samu yin bacci sosae,duk motocin da zai yi amfani dasu manual ne dole sai yayi amfani da kafan mai ciwo in zai tuka su,gashi a yadda yake jin kafan ba zai iya yin tuki da ita ba.
Bayan wani lokaci ya mik'e, komawa yayi cikin corridor yasa takalma slippers kafin ya dawo cikin parlon ya fuce,wajen gate ya nufa ta k'aramar kopa ya fita,tunkarar Officer CD dake zaune saman benci shi kadai yayi,Officern na ganin haisam din ya tunkaro sa yana d'angyasa kafa ya mike da sauri ya nufo sa yana zuwa wurinsa yace"yalla6ai barka da safiya..."hannu haisam ya mik'a masa suka gaisa kafin yaci gaba"yalla6ai rauni ka ji haka?" d'aga masa kai kawai yayi,cike da jajantawa Officer ya shiga girgiza kai yana fad'in"wai sannu,Allah ya kyauta gaba" "Amin" haisam ya amsa kafin yace"in ba damuwa inason zaka kaini hospital ne,sai dai motan is manual I don't know if u could drive it" ya tambaye shine don yasan ba kowa ya iya tuka mota manual ba,
d'an sosa k'eya Officern yayi yana d'an murmushi yace"wllh yalla6ai kwata kwata ma ni ban iya tukin mota ba.." d'age gira haisam yayi yace"really?" Officer dake ta murmushi ya daga masa kai alamar eh kafin yace"sai dai ko in ma Officer Jamil magana don shi ya iya tuka mota don wani lokacin ma yakan fita da Hajiya in t.k baya nan" jinjina kai Haisam yayi yace"ok bari in koma ciki in yazo sai kayi masa magana..."da sauri Officer ya katseshi"ai yana nan,ya shiga ciki ya kimtsa da yake ba dashi mukai aikin dare ba bai jima da zuwa ba,bari in masa magana" ya k'arasa maganar tare da juyawa ya nufi cikin gidan,
Ba da jimawa ba suka fito atare Officer police ne Jamilun da aka kira ya nufo haisam yana gyara hulansa yana zuwa ya mika mashi hannu suka gaisa yace"yalla6ai ashe tsautsai ka had'u dashi" d'aga masa kai kawai yayi yace"to Allah ya kiyaye gaba" a hankali haisam yace"Amin",
"Yauwa wani motan za'a fiddo ne?Nura yace kana so a kaika asibiti" daga masa kai haisam yayi tare da mika masa makullin mota dake rike a hannunsa na hagu" amsar key d'in Officer jamil yayi ya d'an duba shi kafin ya juya don fiddo motan,Officer Nura kuma ya fara sliding gate din,ba 6ata lokaci ya fito da motan Haisam ya shiga suka tafi.
Wuraren karfe biyu na rana gwaggo na zaune a tsakan gida jikinta sanye da kayan aiki ita da wata mata dukkansu suna zaune a saman kujera yar tsugunno da alama bak'uwa tayi,da gudu fatuu ta shigo daga bakin kopar shigowan ta wurgo jakarta tsakar gida tayi bandaki da gudu,gaba dayansu sai da suka tsorata bakuwar matar ce ta juya ta kalli gwaggon tace"kaman fatima ko?" girgiza kai gwaggo tayi ta d'an ta6e baki tace"itace wllh,haka take don iskanci sai ta tara matsuwa,maimakon tun can makarantar tasan tana ji tayi"
Yar dariya matar tayi tace"ina ruwan fatuu" adaidai lokacin fatun ta fito tana gyara wandonta ta duk'a inda jakarta take ta dauka ta wuce ciki,kallon bakuwar tayi tace"Ladidi mai waina ina yini" amsawa tayi"lafiya lau fatima yan makaranta" kallon Gwaggo tayi tace"sannu da gida gwaggo" yar harararta gwaggon tayi batare da ta amsa mata ba,hakan yasa fatuu yin dariya ta wuce d'aki don tasan hararar ta shigowar da tayi da gudu ce,
"....Oh ladidi kina fadi man wannan al'amari mai cike da tashin hankali" ladidin ta kar6e"wllh bari,ni fa ina cikin tuyan waina da safe naji yara suna cewa wai gashi can an zo kama Gaye nace wane gayen? wai Ashiru d'an gidan Malam Tanimu,shine fa su Bilki suka fita don jin ba'asi nidai bansamu fita ba saboda tuyan wainan da nike,da suka dawo ne suke ban labarin wai yunkurin fyade su kai ma wata jiya da daddare shi da abokanansa Allah baisa sun kaiga yin nasarar aikatawan ba wani mutumi ya gansu,ance ma tun jiya da daddaren yan sanda suka zo neman shi basu same shi agida ba shine suka fad'a ma mahaifinsa mlm tanimun laifin da ake tuhumar d'an nasa,suka kuma bukaci ya basu hadin kai da zarar yaron ya dawo gida ya kira su ya sanar dasu kuma kar ya bari ya fita in ba haka ba zasu dawo su kamashi tare da mahaifiyar Ashirun wato Zulai,aikam yau da safe sai gashi ya dawon don bai kwana a gida ba,yana ko zuwa malam tanimun ya kira yan sandan"