← Book details Asanadin Makwabtaka Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 134 OF 137

Sashe 134

Asanadin Makwabtaka Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

ALBISHIRUNKU MATAN AFRICA DA KEWAYE SHAHARARRAR MAISAIDA KAYAN MATAN NAN WADDA KUKAFI SANI DA MAMAN HAIDAR TANA YIMAKU ALBISHIR DA CEWA ZAKU IYA SAMUN KAYANTA ADUK INDA KUKE AFADIN NIGERIA DA NIJAR, KARKU MANTA MACE MAI GYARA BATA BORANCI💃💃💃💃💃💃💃💃💃💃08040448621
Akwai zafafan kayan mata masu matukar kyau da arha cikin sauki zamu aika miki da kayanki cikin aminci da yardar Allah su isa har inda kike ba cuta ba cutarwa karku bari abaku labari.
Muna kawo kalolin ingantattun kaya kamar haka 💥💫💥💫👇👇👇👇
1-Maganin sanyi
2-Maganin gyaran nono
3-Maganin hips
4-Akwai gumba kala kala
5-Maganin matsi masu ciko da gaba ki koma kamar budurwa
6-Kalolin garirrika masu bawa mace ni'ima da jimawa ajiki yana aiki
7-Akwai tsumi sha yanxu magani yanzu
8-Akwai jigidar sirri kala kala
Sannan kuma muna dahuwa kamar haka 💥💫💥💫👇👇👇👇
1-dahuwar kaza
2-yan shila
3-ciccibi
Dadai sauran su.Abubuwa dayawa gaskiya bazasu lissafu bah saboda lokaci maiso ta bini PC don ganin Kalolin kayan da muke dasu 08040448621,

ALLAH YAYI MAKI KIMA DA DARAJA AMATSAYINKI NA MACE👰,KADA KI WOFINTAR DA KANKI A WURIN MIJI SABODA RASHIN GYARA KAI, BURIN MAMAN HAIDAR KO WACE MACE TA ZAMA TAURARUWA⭐YAR LELE AGUN MIJINTA😍 SAI AN GWADA AKAN SAN NA KWARAI🤝

*💖A SANADIN MAKWABTAKA💖*
_*(Love and Destiny)*_

_*BY ZAINAB LALUH📲*_
~(Oumm Imam)~

*DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI*

7️⃣2️⃣

Bayan shekara biyu

Lokaci ya shude shak'uwa sosae ta shiga tsakanin Haisam da Fatuu a wannan lokacin ya zama tamkar dan uwanta na jini da yawan Mutane ma kallon da suke masu kenan wad'anda basu san ainihin tsakaninsu ba, a babbar sallar data wuce ne ta had'u da Mahaifiyar Haisam suka gaisa a gidan Hajiya lokacin sunzo salla su Jidderh suka nuna mata ita dama tana ta jin Labarinta a wurinsu, yanzu shekararta sha bakwae zuwa sha takwas har sun shiga ss 3 an bata muk'amin Senior prefect wato SP, a islamiyya kuma sunyi sauka an had'a masu gagarumar walima har Haisam sai da yaje wurin taron walimar da akayi a harabar Makarantarsu ya kuma bada gudunmawar kudi masu yawa yanzu a ajin hadda suke, gaba d'aya dawainiyarta Haisam ne ke yi mata ta canja sosae ta koma kalar yaran hutu gashi ta k'ara girma saidae bata da tsawo sosae tsaka tsakiyace baza'a kirata gajera ba ba kuma za'a kirata da mai tsawo ba, a bangaren jiki kuwa abun saidae ace Tubarkallah don tana da k'ira gashi hasashen da gwaggo tayi akanta ya tabbata sak jikin Mahaifiyarta ta d'aukko harma ta zarta ta haka gwaggon ke fad'a don kuwa in ka kalli kafadun Fatuu bazaka ta6a cewa k'ugun dake ajikinta nata bane don ya bud'e sosae har ta cikin Uniform d'inta ana gani haka mazaunanta ma fam suke hakan yasa Sauran Students ke kiranta da Fatuu Bum Bum, har Malamai ma sun san da irin k'irar dake gareta don akwae wata rana zasu yi Cultural dance a club d'insu na English tayi shigar fulani lokacin da suka shigo cikin Assembly hall ita da wad'anda sukayi shigan fulanin gabadaya hankalin malamai da d'aliban dake cikin Hall d'in ya dawo kanta nan da nan malamai mata suka fara Maganar rashin dacewar kasancewarta haka don kayan sun fito mata da shape sosae, jin hakan yasa Formistress d'insu Malama Lubabatu ta kirata bayan sun fita waje tace mata tasa kallabinta ta d'aura a kugu sai ta nemi hula tasa Fatun tace ai k'arami ne sai lokacin ta lura da bai rufe mata kai gaba daya ba tace ta jirata anan tana zuwa ta koma cikin Hall d'in ta samo mata aron farin gyalen wata Malama ta kawo mata ta rufe k'ugun.

Zaune suke cikin Class kowa da abunda yake wasu na hira wasu na rubutu da yake free period ce malamin da ke garesu ya sanar bazai samu shigowa ba, Fatuu na zaune saman seat d'insu dake a farkon layin karshe na ajin ta juya ma allo baya suna hira da wata kawarsu mai suna Fiddausy dake zaune ita kad'ai a kujerarsu sauran wad'anda suke zaman sun tafi yawo wani seat d'in, can tace ma Fatun wai mi Haulat keyi ne ta duk'ar da kanta tun d'azun bata d'ago ba, juyawa Fatun tayi ta kalli Haulat dake gefenta can k'arshen bango ta duk'e kafin ta juya ta kalli Fiddausyn ta d'an ta6e baki tace "kema ai kinsan mi zaisa ta duk'e haka" yar dariya tayi tace "halan karatun Novel take" Fatuu tace "shine fa ta maida abu kamar ibada in batayi ba bata jin dadi Allah yasa ma in tayi auren ta rink'a kula da gidanta"

"Wllh baki sani bane karatunne shiga rai gareshi in kika saba da wuya ki iya bari" d'an ta6e baki Fatun ta k'ara yi tace "tunda fa ana rubuta iskanci ba dole a rink'a jin dadinshi ba" waro ido Fiddausy tayi tace "ke waya gaya maki iskanci ake rubutawa?"

"Haka naji ana fad'i nasan kuma shiyasa gwaggo ma ta hana ni karanta irinsu duk da dama ko bata hana ba nima bayi zanyi ba don banda lokacinshi ta karatuna nike bata shirme ba" girgiza kai Fiddausy tayi "Wllh ba yadda kike zato bane duk da ba k'arya bane Maganar gaskia akwae wanda ba komae ciki sai tsantsar batsa amman kuma akwae masu tsafta wad'anda in kana karantawa zaka k'aru sosae don ana fadakarwa da ilimantarwa ta fannin addini uwa uba kuma zaka koyi abubuwa masu mahimmanci da suka shafi rayuwa ba kamar gamu mata misali zamantakewar aure da dai sauransu wasu har abinci in suka sa anyi acikin littafi zaki ga sunyi bayanin yadda ake yi in kamar sun san ba irin wanda aka saba yi bane, ni kinga ina yin karatun Novel kuma ko Mamarmu ta sani itama tana yi kuma wani lokacin in ta karanta littafi taga yayi ma'ana da kanta take turo man tace in karanta sam bana karanta mara ma'ana don asarar lokaci ne wllh" still ta6e baki Fatuu tayi ta gyad'a mata kai, mik'ewa Fiddausy tayi tace "bari inje inyi Fitsari tun d'azun nike jinshi ina matsewa kar ya zubo man a wando in shiga ukku anma ce fa ba'a son rike fitsari don lalura yake sawa" har zata fita daga cikin seat d'in ta juyo tace ma Fatun bazata rakata ba,

"Ke dai jeki, yadda kurata tayi kuka yanzu da an ganni waje sai ace nayi laifi, bari in baki ma ki siyo man aya" tayi Maganar tana kokarin curo kud'in acikin Aljihun wandon Uniform d'inta, naira dari ta fiddo ta bata tace ta siyo mata ta Hamsin ta d'auki sauran Hamsin d'in don yanzu Fatuu zama da Haisam ta koyi yin kyauta sosae sam abunta bai sha mata kai ba daka nuna kana son wani abu nata sai ta baka ko kuma kazo aro sai tace ta baka kyauta hakan kuma ba k'aramin farinjini ya k'ara mata ba kowa sonta yake tana matuk'ar burge mutane, Godiya Fiddausyn tayi mata bayan ta amshi kud'in ta tafi,

juyawa tayi ta koma tana Facing allo ta duk'a a hankali ba tare da Haulat ta ankare ba taji ta fige yar wayarta da take karatun da ita, a wani firgice ta d'ago koda taga Fatuu ce sai ta wurga mata harara tace "Don Allah ki bani kar ki fitar man inda nike" itama hararar tata tayi tace bazata bata ba, magiya ta hau yi mata Fatun tace "to zan baki amman sai naga abunda kike karantawa in kuma baki bari ba Wllh bazan bari kici gaba da yin karatun ba" sanin halinta yasa tace to ta tsaya ta duba, kallon screen d'in wayar tayi ta fara karanta inda Haulat d'in take, suffar jarumin littafin ake bayyanawa bayan ta gama karantawa ta d'ago ta kalli Haulat tace "Waye wannan kaman Aljani?" dariya haulat d'in tayi tace "Mijin Novel kenan"
"Mijin Novel haka sunanshi yake?"
"A'a haka dae ake cewa wai ba'a iya samunsu a zahiri saboda kyaun da ake sawa suna dashi" da mamaki Fatuu ta k'ara duba wurin kafin tace "wannan ne ba'a iya samu a zahiri?" kai haulat ta d'aga mata "haka ake cewa" yar harara ta wurga mata kafin tace "to wllh ko ni nasan mai irin wannan suffar za'a wani ce ba'a samun irinshi a zahiri" haulat na dariya tace "nima nasan wani mai irin suffar amman ke wanene wanda kika sani mai wannan kamannin?" tace "yo Ya Handsome mana ke baki ga sak suffarshi ce aka bayyana ba"
"Wllh nima ina karantawa shi ya fad'o man a rai" d'an ta6e baki fatuu tayi tace "to ke miye na zama kita karanta kamanin wani Namiji bayan an bayar dake"
"To in banda abunki waya k'i abu mai kyau kuma dae nasan ba samun irinshi zanyi ba, ke dai ai kinji dad'i kinsamu mijin Novel" ta k'arasa tana dariya, da mamaki fatuu tace "ni kuma mukai dake ina da saurayi irinshi balle har ki kirashi da mijina" tayi Maganar tana harararta,

"Ina nufin wanda yanzu kika ce yana da irin sufar da aka fad'i" waro ido Fatuu tayi harda d'an juyawa gefe wai taga ba wanda yaji abunda haulat d'in tace don kowa kallon yayanta yake mashi ido waje tace "ke, nina gaya maki Ya Handsome saurayi na ne yaushe mukai hakan dake?" wata dariya haulat tayi tace "habawa yan mata an gaya maki a banza nike karatun Novel, ai ko yaro yaji labarin tsakaninki dashi zai fahimci son ki yake shiyasa yake maki duk abubuwan da yake maki kawae dai nasan k'ilan lokacin da zai bayyana maki hakan baiyi bane shiyasa bai fito ya nuna maki ba amman ina nan dake zaki ce na gaya maki" wani irin kallo Fatuu ke binta dashi da alama ta kashe mata bakinta don ita tunda take da Haisam bata ta6a sawa aranta wai sonta yake ba can tace "amman dai ai kin fi kowa sanin halinshi in don abubuwan da yake man ne ai ba ni kadai yake ma abun alkhairi ba ko",
Chapter 134 · 0% Book details