← Book details Asanadin Makwabtaka Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 126 OF 137

Sashe 126

Asanadin Makwabtaka Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Lokacin data isa gidan kaman an jefota ta fad'o cikin falon Hajiyan kallabi a hannu ga ledoji a hannu tana ta zare idon son hango Haisam don taje part d'inshi bai nan kuma tasan yau ba ranar zuwa gym bace, Jidderh ce zaune a falon kan sofa 3 seater tana yin chat da wayarta ta d'aura duka k'afafunta saman kujeran jikinta sanye da jallabiya milk colour kanta ba kallabi tayi parking gashinta da yake bak'i sosae mai santsi sai twins dake gefenta suna yin game da ipad, atare suka d'ago suka kalleta kaman yadda itama ta kafesu da ido tana yi masu kallon rashin sani ko kyaftawa batayi, sai faman kallon juna suke an rasa wanda zai tanka ma wani can Mubeen ya kai bakinshi saitin kunnan Mubeena ya rad'a mata wata Magana ai kuwa a firgice ta kalleshi ta kuma kalli Fatun atare sai kace an latsa masu remote suka diro daga kan kujeran bayan sun aje ipad d'in suka ruga hanyar Bedroom d'in Hajiya suna kwala mata kira cike da razana sai kace kaji broilers yadda suke gudun, a daidai Corridor sukayi kacibus da ita ta fito jin kiran da suke mata jikinta sanye da hijab da casbaha a hannunta tun kafin tace wani abu atare suna haki suka ce "Ha...Hajiya a genie has appear" waro ido tayi tace "a genie?" da sauri suka jinjina mata kai alamar eh,
tace"where is d genie" da hannu suka nuna mata cikin falonta, kama hannuwansu tayi tace "Ok let's go and see d genie" suka nufi cikin falon har wani sand'a suke tun kafin su k'arasa ta hango Fatun tsaye k'ikam har lokacin kuma Jidderh bata ce mata komae ba don ganin su twins sun ruga yasa ta d'an ji tsoron Fatun ya kamata, lokacin da suka k'araso cikin falon Hajiya na dariya tace "Lallai kuwa k'atuwar Aljana ce ta bayyana" da sauri Jidderh ta kalleta jin abunda tace amman ganin tana dariya yasa hankalinta kwanciya nan take kuma ta fara hasashen anya ba itace Fatun da Hajiya ke basu labari ba yar gidan ya haisam mai ce mashi Handsome don duk in suna fira sai ta sako masu labarin Fatun, kallon Hajiya su twins sukae suka nuna mata Fatuu wai ga Aljanar tana dariya ta zauna idonta akan Fatun tace "Manyan gari saukar yaushe?" tana tura baki tace "yanzun nan muka dawo Mota ta lalace mana a hanya" da mamaki su twins ke kallon both of them ganin suna Magana, Mubeena ce tace "Granny u know d genie?" kallonsu tayi tana dariya tace "she isn't a genie, she's d Fatuu i ave been telling u about" a tare suka zaro ido suka had'a baki suka ce "Fatuuuu!" kai Hajiya ta d'aga masu lokaci guda suka saki dariya suka nufeta aikuwa ta d'aure masu fuska tana yi masu wani kallo hakan yasa suka ja suka tsaya a gabanta suna kallonta itama kallonsu take da yar harara kawae sai suka fara ta6e baki irin na shagwa6a66un yara alamar zasu yi kuka hannunsu cikin na juna suka juya zasu koma Hajiya tace "ah Fateema ya da haka kuma?" tana tura baki tace "ba sune suke ce man Aljana ba"
"To ai basu sanki bane baki ga bak'i bane gashi sun ganki da wata kalar shiga ga kanki a bud'e shiyasa suka tsorata ai" kallonsu tayi tace suje su bata hakuri a yadda suke ba tare da sun raba hannuwan ba suka koma,tsayawa sukae a gabanta sannan suka saki hannuwan kowa ya kama kunnanshi a tare suka ce"Sis Fatuu we're sorry" kawae sai gani sukae ta kece da dariya don yadda sukae ba k'aramin dariya suka bata ba dama ga uban kumatu tubarkallah suna ganin tayi dariya suka k'ank'ameta suna yi mata welcome, Jidderh da Hajiya ma dariyar suke, Hajiya ce tace ta zauna mana ta nemi wuri kan 2 seater suka zauna, gaida Hajiyar tayi kafin ta maida idonta kan Jidderh dake mata Murmushi itama ta gaidata ta amsa tace mata "an dawo lafiya" tana Murmushi tace "Lafiya lou amman munsha wahala tun Asuba sai yanzu muka iso fa" cikin sanyin muryarta tace "gaskia, sannu ko" amsa mata tayi da yauwa kafin ta kalli Hajiya tace "Hajiya su waye wad'annan?"
tana dariya tace "ai kuwa ya kamata ace kin ganesu basai an fad'a maki ba, ki kallesu da kyau zaki gane ko suwaye" jin haka yasa ta k'ura ma jidderh dake Murmushi ido sai kuma ta maido kallon kan su twins tana k'are masu kallo can tace "wad'annan kumatunsu yayi yawa na kasa ganewa" hajiya tace "to ki kalli wannan da kyau" tayi Maganar tana nuna Jidderh, zuba mata ido ta k'ara yi ganin kaman tana yanayi da Haisam yasa tace ta daina yin dariya zata fi ganowa dariyar ta k'ara yi sosae jin Maganar Fatun kafin ta dakata suna kallon juna can ta kalli hajiya da sauri tace "yan gidansu Ya Handsome ne ko?" aikuwa gaba d'aya harda twins suka sa dariya jin tace Ya Handsome din, bayaninsu Hajiya tayi mata daga baya tace bayan bata nan suka zo, Ledar dake ruke a hannunta su twins suka fara ta6awa suna tambayar miye a ciki tace masu tsaraba ce,
"Za mu ci" suka fad'a suna kara ta6a ledar da sauri ta janyeta tace"kai ba irin abunda kuka saba ci bane wannan shak'e ku zai yi" k'ara had'a baki sukae suka ce zasu ci koma minene tace "kai kuji man yara, so kuke ta shake ku kuja akaini gidan yari ko" kafewa sukae kan su dae ta basu suci su Hajiya na masu dariyar drama d'in da suke can Hajiya tace "miye a ciki ne?" da sauri tace "su goriba da kurna da magarya da aya ne fa na fara kawo maki sai gobe za'a ida kawo sauran tsarabar" kafin Hajiya tace wani abu Jidderh tace "ki basu ai sun iya cin su" da al'ajabi ta kalleta tace "ni ai nazata a Abuja ba'a saida irin wad'annan abubuwan don ance kaman kasar waje take" Jidderh na dariya tace "No akwae kasuwar da ake saida irinsu kuma cikin maids din mu akwae wata Iya yar Daura ce so in tazo tana kai mana tsaraban su har Dad ma naci yace suna Magani" cike da jin dad'i Fatun ta washe baki jin an yaba tsarabar tata, bud'e masu ledar tayi kowa ya d'auki goriba biyu yasa a cikin riga suka rungume sannan suka d'ibi magarya a hannu suka fara sha Hajiya dake kallonsu tace "wai bani aka kawo ma tsarabar bane to a mik'o man mana kuke ta kwashewa" mik'ewa Fatuu tayi ta kai mata ledar ganin tana ta mak'ale d'ayar a hammata tace to ita wannan miye aciki tace ba nata bane tsarabar Ya Handsome ne, bud'e ledar Hajiya tayi ta aje masu suka fara shan magaryar ita da Jidderh su twins suka ba Fatuu goribar wai ta cirar masu dama haka ake masu in kuma irin wadda aka 6an6are ce sai a jika masu tayi taushi sannan su ci suna cikin ci Fatuu ta tambayi Hajiya ina Saude tace tana d'akinta mura ke damunta ne tasha magani ta kwanta tace to ina Ya Handsome yake tace sun fita amman tasan sun kusa dawowa, Hajiya na rufe baki Nameer da Farha suka shigo hannunsu cikin na juna kowannansu na sanye da k'ananan kaya ta zame gyalen kanta ya dawo saman kafad'a, nufo cikin falon sukae Nameer na Fad'in "kai kai wato abun dad'i kuka samu kuna ta shagali shine ko ku tuna damu ko" yana rufe baki Mubeen ya nufe su yana nuna masu Fatuu yace "Ya Nameer guess who she is" d'aga ido yay ya kalli Fatun da itama shi take kallo da mamaki ganin tsananin kamarsu da Haisam, k'uri yay mata ya d'an k'ank'ance ido alamar yana son gano ko wacece d'in duk suka bishi da ido da Murmushi ita kuwa Farha kujera ta nufa ta zauna itama idonta na kan Fatun tana mata wani kallon rashin arziki don dama ita shirgin Mutane bai dameta ba,
Chapter 126 · 0% Book details