Sashe 120
Asanadin Makwabtaka Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Haisam na komawa gida shima ya fara shirin tafiya Lagos don da wuri yake son ya sauka saboda baisamu tafiya jiyan ba, Tafiya akace yankin azaba Fatuu saidae tay ta kalle kalle tay bacci ta farka wani lokacin har dan tsoki take ja in ta farka ta tambayi gwaggo sun kusa tace mata da saura gashi bunu bunu tace yunwa take ji duk garin da aka tsaya sai tasa an siya mata abun ci, lokaci bayan lokaci Mahaifin Fatun ke kiran Amadu yaji ya hanya da yake in suka sauka jimeta wani abokinshi ne zai daukesu ya kaisu rugar saboda shi bai nan yaje kasuwar wani gari, lokacin da suka sauka jimetan yamma tayi lis Fatuu ko Magana dakyar take yi ba 6ata lokaci wanda zai daukesu yazo don suna gabda sauka Amadu ya kira Baban Fatun ya sanar mashi, gab Magrib suka isa rugar wadda da ka kalleta zaka fahimci ruga ce ta ainihin fulani tun daga kan jama'ar dake kai kawo wad'anda ke sanye da shiga ta fulani mafi akasarinsu daga kiwo suka dawo, garin nada albarkar shuke shuke ba kamar da yake damuna ta fara kankama ko ina yayi luff da korayen ganyayyaki sannan yawanci duk bukkoki ne masu ginin k'asa basu da yawa an zagaye su da dannin kara, tunda suka shigo garin Fatuu tayi kuri tana kallon masu wucewa a amalenken shanu dayake anfi amfani dashi saboda akwae yawan yashi a hanyar, daidai gaban wani babban gida na ginin kasa Motarsu ta tsaya nan da nan kuma yaran dake a kopar gidan suka yo ma Motar caa da ido wad'anda ke a tsugunne suka mik'e amman ba wanda ya tunkari Motar haka mutanen dake a gefe kasan bishiya suna yin Alwala suma duk suka maido hankalinsu kan Motar dama anan kopar gidan daga can gefe inda ardo ke zama ake taruwa ayi salla, adan can gefe guda kuma akwae teburi mai d'auke da rake a samanshi wanda yayan Fatuu Kamalu ne ke saidawa, tunda yaran gidan wadanda suka san Fatun suka ji batun zuwansu suke ta zaryar zuwa kopar gidan dalili ne kawae ke maidasu cikin gidan ba kamar k'annenta, Amadu ne ya fara fitowa duk suka kura mashi ido don basu sanshi ba wanda kuma suka ta6a ganinshi sun manta shi yana fitowa Fatuu ta fito gyalenta a hannu itama dae idon suka bita dashi da alama itama basu ganetan ba wasu kuma wasiwasi suka fara acikin ransu ba kamar kanwarta Ameena da ake ce ma Mino wadda suke bala'en kama da ita don itama Babansu ta biyo kuma tafi kowa d'okin ganin Fatun don suna kaunar juna kuma lokacin da tana garin bata bari wani ya ta6ata in kuwa akayi mata wani abu sai ta rama mata amman fa ita tana dukanta in tayi mata ba daidai ba, tsaye sukae suna kallon kallon da ita, ita Fatuu ta ganeta ita kuma sai kokonton anya itace take a ranta, gwaggo ce tazo inda suke bayan ta gama yi ma mutumin daya kawo su godiya Amadu kuma yana firfito masu da kayansu,
"Ya aka tsaya ana kallon kallonne, Mino baki gane yar uwar taki bane" gwaggo ta fad'a cikin harshen fullanci, kallon gwaggo da tayi maganar tayi sai kuma ta maido idon kan Fatuu harararta tayi nan take ta gane itace ta saki wata uwar k'ara da fullanci take fad'in ga inna wuron sun iso hakan duk yaja hankalin mutanen wurin sauran yaran kuma suka watsa gida aguje don su sanar saiga Kamalu ya fito shima yana yanayi da Fatuun saidae ba sosae ba don yafi daukko kamannin mahaifiyarsu amman shima fari ne yana hangosu ya watsa a guje yaje ya rungume Amadu wanda yake matsayin babanshi kuma Abokinshi, ita kam mino ta kasa ma rungume Fatun saboda mamaki da kuma Al'ajabin yadda Fatun ta koma sai faman washe mata baki take kawae tana kare mata kallo daga sama har kasa fatun na mata Murmushi, wasu daga cikin mazan gidanne suka zo suna yi masu sannu da zuwa baka jin komae sai fullanci ke tashi yayin da kowa ke mamakin girman da Fatun tayi, ciki harda Yayanta Kamalu baki bud'e yake binta da kallo yana tambayar gwaggo wai wankan inji ta kaita akayi mata ne kuma mi take bata tayi girma haka ba kamar da yake takalma masu tsini ne a kafarta sun k'ara mata tsawo, ita dae gwaggo murmushi kawae take Fatun kuma na tura baki, Kamalu da wasu ne suka d'auki jakunkunan don shigar masu dasu su gwaggo suka rufa masu baya, Babban gida ne mai d'auke da gine ginen wasu gidajen aciki ma'ana yana da 6angarori sosae aciki don gaba d'aya a halin ardo na acikin gidan kowa da bangarenshi, suna shiga Yadikko da ta kosa su shigo tunda ta samu labarin isowarsu ta nufosu cike da farinciki tana masu maraba Mino dake ruk'e da hannun Fatuu ta nuna ma yadikko ita tana Fad'in taga yadda inna wuronsu ta koma, waro ido tay tasa hannu ta ruk'e ha6a alamar mamaki yayin da Fatun ke mata Murmushi buda mata hannu tayi bayan ta gama al'ajabin Fatun ta nufeta ta rungumeta cike da kauna da nuna kewa, saida gwaggo ta gama amsa sannu da zuwan da wadanda suka leko keyi mata sannan suka wuce ciki ita dae Fatuu ba kowa take tanka mawa ba saidae ta bi mutum da ido kaman yadda suma suke binta da idon fuskokinsu dauke da tsantsar Mamaki, koda suka shiga dakin wanda babbane ba laifi yana da shafen plasta amman ba fenti haka saman ma anyi ceiling irin na leda mai kyalkyali akwae gado babba mai rumfa sai kuma karami na katako yana da dan mirror mai dauke da tarkacen kayan shafa sai wardrobe mai gida biyu sai kuma cabinet mai dauke da jeren k'orai da kwalla da kwanoni jikin bangon d'akin ma anyi adon korai masu zane mai kyau da fayafai haka kasan dakin rufe yake da ledar tsakar daki akwae kujera mai mazaunin mutum ukku a gefe a samanta gwaggo ta zauna Fatuu kuma ta nufi gefen k'aramin gado ta zauna mino dai na gefenta sai faman kallonta take tana zabga Murmushi da gani ba karamin burgeta Fatun tayi ba, bayan sun k'ara gaisawa gwaggo ta mik'e don yin salla ita kam Fatuu kwanciyarta tayi koda gwaggo tace bazata tashi tayi salla bane cewa tayi sai ta huta bata iya tsayuwar sallan, bayan gwaggon ta gama saida tayi mata da gaske sannan ta tashi tayi sallan tana gamawa anan kan abun sallan bacci ya kwasheta, kan kace mi an cika d'akin da kwanoni da k'oran abinci dasu Fura da aka aiko ma baki ba yadda ba ai ba Fatuu ta tashi taci abinci amman ta kiya gwaggo tace su rabu da ita in taji yunwar sosae zata tashi ne, sai can bayan isha Mahaifin Fatun ya dawo cike da girmamawa ya duk'a suka shiga gaisawa da gwaggo dama shi Amadu sun gaisa dashi acan waje wurin Kamalu, sai lokacin gwaggo ta tada Fatun tace ta tashi to ga Baffanta ya dawo ai tana jin hakan ta mik'e zaune idonta akanshi shi dae sai faman Murmushi yake mata yadikko nace mashi ashe haka inna wuron ta koma da yake kwanaki da yaje bayan ya dawo yana ta basu labarin girman da tayi, bayan sun gama gaisawa ne gwaggo tace mashi yayi mata jagora zata gaishe da ardo, koda gwaggo tace mata tazo suje ta gaishe shi cewa tayi taje gobe taje ita yanzu yunwa take ji abinci zata ci hakan yasa ta rabu da ita, tana gama cin abincin lokacin gwaggo ta dawo tace ta watsa ruwa tafi jin dadin jikinta, bayan tayo wanka canja kaya tayi zuwa na bacci ta nufi d'akin Baffanta wai acan zata kwana da kyar ya lalla6ata yace ta dawo cikin yan'uwanta ta kwanta don sunyi kewarta sosae, saida ya rakota har kopar daki sannan ya koma maimakon ta shiga sai kawae tayi hanyar waje ta nufi dakinsu Kamalu dake acan soro lokacin tuni Amadu yayi bacci amman saida tasa aka tashe shi tace wai Ya kira mata Ya Handsome zata gaya mashi sun iso tunda da suna Mota ya kira ya tambaya, uban tsoki ya ja ya hau yi mata fadan tashinshi da tasa akai karshe rai 6ace yace bai kira tunda bai dade da yayi waya da Haisam d'in ba kuma ya sanar dashi sun iso lafiya don haka ta tafi ta bashi wuri, ba don taso ba tana kumbura baki Kamalu na mata dariya ta baro soron ta nufi cikin gidan dama don tasan gwaggo bazata bari ta kirashi a wannan lokacin bane yasa taje wurin Amadun.
"Ya aka tsaya ana kallon kallonne, Mino baki gane yar uwar taki bane" gwaggo ta fad'a cikin harshen fullanci, kallon gwaggo da tayi maganar tayi sai kuma ta maido idon kan Fatuu harararta tayi nan take ta gane itace ta saki wata uwar k'ara da fullanci take fad'in ga inna wuron sun iso hakan duk yaja hankalin mutanen wurin sauran yaran kuma suka watsa gida aguje don su sanar saiga Kamalu ya fito shima yana yanayi da Fatuun saidae ba sosae ba don yafi daukko kamannin mahaifiyarsu amman shima fari ne yana hangosu ya watsa a guje yaje ya rungume Amadu wanda yake matsayin babanshi kuma Abokinshi, ita kam mino ta kasa ma rungume Fatun saboda mamaki da kuma Al'ajabin yadda Fatun ta koma sai faman washe mata baki take kawae tana kare mata kallo daga sama har kasa fatun na mata Murmushi, wasu daga cikin mazan gidanne suka zo suna yi masu sannu da zuwa baka jin komae sai fullanci ke tashi yayin da kowa ke mamakin girman da Fatun tayi, ciki harda Yayanta Kamalu baki bud'e yake binta da kallo yana tambayar gwaggo wai wankan inji ta kaita akayi mata ne kuma mi take bata tayi girma haka ba kamar da yake takalma masu tsini ne a kafarta sun k'ara mata tsawo, ita dae gwaggo murmushi kawae take Fatun kuma na tura baki, Kamalu da wasu ne suka d'auki jakunkunan don shigar masu dasu su gwaggo suka rufa masu baya, Babban gida ne mai d'auke da gine ginen wasu gidajen aciki ma'ana yana da 6angarori sosae aciki don gaba d'aya a halin ardo na acikin gidan kowa da bangarenshi, suna shiga Yadikko da ta kosa su shigo tunda ta samu labarin isowarsu ta nufosu cike da farinciki tana masu maraba Mino dake ruk'e da hannun Fatuu ta nuna ma yadikko ita tana Fad'in taga yadda inna wuronsu ta koma, waro ido tay tasa hannu ta ruk'e ha6a alamar mamaki yayin da Fatun ke mata Murmushi buda mata hannu tayi bayan ta gama al'ajabin Fatun ta nufeta ta rungumeta cike da kauna da nuna kewa, saida gwaggo ta gama amsa sannu da zuwan da wadanda suka leko keyi mata sannan suka wuce ciki ita dae Fatuu ba kowa take tanka mawa ba saidae ta bi mutum da ido kaman yadda suma suke binta da idon fuskokinsu dauke da tsantsar Mamaki, koda suka shiga dakin wanda babbane ba laifi yana da shafen plasta amman ba fenti haka saman ma anyi ceiling irin na leda mai kyalkyali akwae gado babba mai rumfa sai kuma karami na katako yana da dan mirror mai dauke da tarkacen kayan shafa sai wardrobe mai gida biyu sai kuma cabinet mai dauke da jeren k'orai da kwalla da kwanoni jikin bangon d'akin ma anyi adon korai masu zane mai kyau da fayafai haka kasan dakin rufe yake da ledar tsakar daki akwae kujera mai mazaunin mutum ukku a gefe a samanta gwaggo ta zauna Fatuu kuma ta nufi gefen k'aramin gado ta zauna mino dai na gefenta sai faman kallonta take tana zabga Murmushi da gani ba karamin burgeta Fatun tayi ba, bayan sun k'ara gaisawa gwaggo ta mik'e don yin salla ita kam Fatuu kwanciyarta tayi koda gwaggo tace bazata tashi tayi salla bane cewa tayi sai ta huta bata iya tsayuwar sallan, bayan gwaggon ta gama saida tayi mata da gaske sannan ta tashi tayi sallan tana gamawa anan kan abun sallan bacci ya kwasheta, kan kace mi an cika d'akin da kwanoni da k'oran abinci dasu Fura da aka aiko ma baki ba yadda ba ai ba Fatuu ta tashi taci abinci amman ta kiya gwaggo tace su rabu da ita in taji yunwar sosae zata tashi ne, sai can bayan isha Mahaifin Fatun ya dawo cike da girmamawa ya duk'a suka shiga gaisawa da gwaggo dama shi Amadu sun gaisa dashi acan waje wurin Kamalu, sai lokacin gwaggo ta tada Fatun tace ta tashi to ga Baffanta ya dawo ai tana jin hakan ta mik'e zaune idonta akanshi shi dae sai faman Murmushi yake mata yadikko nace mashi ashe haka inna wuron ta koma da yake kwanaki da yaje bayan ya dawo yana ta basu labarin girman da tayi, bayan sun gama gaisawa ne gwaggo tace mashi yayi mata jagora zata gaishe da ardo, koda gwaggo tace mata tazo suje ta gaishe shi cewa tayi taje gobe taje ita yanzu yunwa take ji abinci zata ci hakan yasa ta rabu da ita, tana gama cin abincin lokacin gwaggo ta dawo tace ta watsa ruwa tafi jin dadin jikinta, bayan tayo wanka canja kaya tayi zuwa na bacci ta nufi d'akin Baffanta wai acan zata kwana da kyar ya lalla6ata yace ta dawo cikin yan'uwanta ta kwanta don sunyi kewarta sosae, saida ya rakota har kopar daki sannan ya koma maimakon ta shiga sai kawae tayi hanyar waje ta nufi dakinsu Kamalu dake acan soro lokacin tuni Amadu yayi bacci amman saida tasa aka tashe shi tace wai Ya kira mata Ya Handsome zata gaya mashi sun iso tunda da suna Mota ya kira ya tambaya, uban tsoki ya ja ya hau yi mata fadan tashinshi da tasa akai karshe rai 6ace yace bai kira tunda bai dade da yayi waya da Haisam d'in ba kuma ya sanar dashi sun iso lafiya don haka ta tafi ta bashi wuri, ba don taso ba tana kumbura baki Kamalu na mata dariya ta baro soron ta nufi cikin gidan dama don tasan gwaggo bazata bari ta kirashi a wannan lokacin bane yasa taje wurin Amadun.