Sashe 77
Asanadin Makwabtaka Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Yaya Haisam ina kwana" Amadu ya fad'a,kai kawai ya jinjina mashi fuskarshi asake kafin calmly yace"Zarah fa?" da sauri Amadu yace"Wllh ta rigada ta tafi,dazun ina brush anan waje ta fito ta tafi yanzun ma ina ganin ta isa makarantar",
lumshe ido yayi ya dan jinjina kai,a tunanin Amadu wucewa zaiyi hakan yasa ya dan ja da baya amman sai yaji yace mashi ya shiga Motar,
"Yaya Haisam da kaje kar na 6ata maka lokaci zan hau aca6a" cike da girmamawa yayi Maganar harda dan rankwafowa,
"No problem ka shiga" cikin cool voice dinsa ya fada amsawa yayi da toh ya nufi d'ayan 6arin Motar,gaba ya bude ya shiga ya zauna wani ni'imtaccen sanyi hadi da sanyayyan kamshi suka kai ma hancinshi ziyara har saida ya dan lumshe ido bayan ya rufe kopar haisam yaja suka tafi,tsit kake ji idon haisam na akan hanya shi kam kawu Amadu yayi shiru yana kallon gefen hanya wani irin nishadi yake ji har dan murmushi yake saki,bayan sun hau hanya ne haisam ya tambayeshi wane school yake ya fadi mashi nan take ya gane Makarantar don acan wurin Airport take wato kambarawa,bayan d'an lokaci suka iso Amadu yace ya ajeshi a bakin gate sai ya shiga hannu kawai haisam ya daga mashi alamar ba wani abu ya shige dashi ciki,har gaban Admin block ya kaishi yana kokarin fita ya mika masa kudi 2k yace yayi break, da tsananin mamaki Amadu ya kalli kudin kafin ya kalli haisam,yana so yace mashi ya barsu sai dai sam ya kasa don wani irin kwarjini gareshi gashi ko kallon Amadun ma bai yi ba,hannu ya kai ya amsa hadi da yi mashi godiya daga haka ya bude motar ya fita daidai wasu Abokansa sun taho suna ganinshi suka ja suka tsaya suna kallonshi da mamaki ganin had'addar Motar daya fito wanda a iya saninsu ba'a ta6a kawo shi makarantar a Motar gida ba,tsaye yayi saida haisam din yayi reverse ya juya ya nufi gate kafin ya tunkari abokan nashi yana wani bouncing suna ganin hakan suka sa sowa suna kuranta shi,saida suka gama shegantakar tasu irin ta dalibai sannan suka nufi class.
*** **** ****
Lokacin da su Fatuu suka isa class dinsu Mutum biyu suka iske aciki wurin zamansu suka nufa don su zauna dayake a layin tsakiya suke kuma seat dinsu ne na farko,suna zama Fatuu ta fiddo Assignment dinta tana kara bitar shi haulat dae nata saurararta don ba gane inda ta dosa take ba,a hankali dalibai suka cigaba da zuwa nan da nan ajin ya cika period din farko ta shiga shiru Malamin lissafin bai shigo ba Fatuu duk ta kagara bunu bunu ta kalli kopar shigowa ajin,
"Fatuu gashi nan" Haulat ta fada tana gyara zamanta da sauri fatuu ta kalli kopar daidai malamin ya shigo cikin ajin,wani murmushi ta saki tana kallon haulat,sanye yake da blue jeans da riga mai dogon hannu ya dad'e da bak'in glass,yana shigowa yan ajin suka mike suna gaidashi,seat din farko na layin karshe ya nufa ya d'aura textbook da Allin dake ruke a hannunshi sannan ya kalli Students din fuskarsa ba yabo ba fallasa ya amsa masu gaisuwar kafin yace su zauna,bayan sun zaunan ya juya ya nufi blackboard ya rubuta subject din da yake yi da date yaja layi kafin ya rubuta sabon topic din da suka shiga jiya ya juyo ya dauki textbook din math ya rubuta wasu misalan bayan ya gama ya juyo ya fara masu bayani,itakam Fatuu ganin bai tanka mata ba yasa ta fara tunanin ko ma ya manta da Assignment dinne,saida ya gama yi masu bayanin misalai guda ukku yace in akwae wanda bai ganeba ko mai tambaya yayi,wasu suka fadi abunda basu ganen ba wasu sukayi tambayar saida ya gama dasu kafin ya kalli Fatuu fuska a matukar d'aure yace"where is my Assignment?",
shiru tayi tana binshi da ido hakan yasashi ce mata ta fito gaban Allo,mikewa tayi littafinta a hannu ta fita,
" Who is the class monitor?"ya tambayi yan ajin,
"Malam itace monitar" wasu suka fad'a, jinjina kai yayi ya tambayi ina mataimakiyarta aka nuna mashi Haulat,umarni ya bata taje Staff room ta daukko mashi kujera ta amsa da to kafin ta mike ta nufi hanyar fita,bada jimawa ba ta dawo hannunta ruke da kujerar ta kai mashi inda yake jingine da window ta aje agefenshi kafin ta koma ta zauna,gyara kujerar yayi ya zauna daga haka ya nuna ma Fatuu Allo da hannunshi,
"Ki rubuta Question din dana baki da kuma amsar danace ita zaki samo"amsawa tayi da to,yadda ta amsan a dan sanyaye sai kace batayi Assignment din ba,bayan ta rubuta ta juyo ta kalleshi tun kafin tace wani abu ya tambayi yan ajin sun gama kwafar rubutun tsakiyan allon suka amsa da eh,nuna mata wurin yayi yace ta goge rubutun tayi ma yan ajin bayanin aikin da ya bata har ta gano amsar,shiru tayi tana kallonshi ya dan daka mata tsawa" baki ji mi nace bane!" dan tura baki tayi tace"naji" juyawa tayi ta kalli yan ajin da kowa idonshi na akanta sunyi mata tsuru ba wanda yake tunanin zata iya don sam yanayinta bai nuna ta iyan ba ta galla masu harara,hada ido sukai da haulat ta tura mata baki itakam haulat din dariya tayi ta girgiza kai kawai don halin Fatuu sai ita,shidae math teacher din sai girgiza kafa yake ya dan kya6e baki cikin ranshi kuwa ya tabbatar bazata iya ba hakan yasashi cin alwashin sai ya koya mata hankali,littafinta ruke ahannunta ta fara rubutu a allo bayan ta goge rubutun jikinshi,tambayar ta fara rubutawa kafin ta fara fiddawa tana juyowa tana ma yan ajin bayani,tun tana yi ahankali har ta daga murya ta zage sai uban bayani take kai kace malama ce ke yima dalibai bayani,shin ina malam yake ne?yana dai azaune yayi tsitt sai bin ta da ido yake cike da mamaki abun ya matukar daure mashi kai don bai ta6a tunanin zata iya ko kusa da yadda take yi ba,gashi abunda ma yafi bashi mamaki shine yadda take bayanin ba tare da tana kallo a wani wuri ba da kai take yi,lokacin data zo karshe ta gano irin amsar tashi sai ta juyo ta kalli yan ajin da suka yi sototo suna sauraranta wasu bakinsu a bud'e saboda mamaki,
"kun gane ko asake yi maku bayani?"ta tambayesu tana murmura idanu had'i da sa hannu guda ta dafa kugu,gaba daya suka ce sun gane,juyawa tayi ta kalli malam da har lokacin idonshi na sanye cikin gilashi tace" Gashi nan na fidda har na gano amsar irin taka,nayi daidai ko?"ta tambaya da d'an Murmushi tana d'age ido,farko shiru yayi yana ta kallonta har saida ta k'ara tambayar tayi daidai sannan ya daga mata kai alamar eh,
"To tunda nayi daidai kace a tafa man ko" ta fad'a tana tura baki,d'an jinjina kai yayi yai wani guntun Murmushi da alama ta kashe shi da mamaki sai kace ba mai laifi ba har wani neman atafa mata take, ganin haka yasa tace"yanzu duk wannan uban aikin da nayi malam baza'a tafa man ba" ta k'arasa tana ta tura baki,kallon yan ajin yayi yace su tafa mata aikam kaman da gayya suka fara uban tafi kilan kuma murna suke Allah ya raba su da alakakai,
"Malam shikenan inje in zauna ko tunda dai nayi daidai ae ba batun punishment ko?" ta fad'a tana gwalo ido,d'aga mata kai yayi alamar eh, har ta juya ya tsaidata don ya kasa hakuri so yake yaji yadda akai ta fidda Assignment din don shi kanshi yana a shekararshi ta k'arshe aka basu Assignment d'in wanda ba karamar wuya yasha ba wurin fidda shi,
" Waya koya maki?" yayi tambayar fuskarshi ba wasa,d'age gira tayi tace"Assignment d'in?"kai ya daga alamar eh,d'an murmushi tayi da bud'ar bakinta sai cewa tayi"wani Aljani ne acikin Aljanuna yazo ya koya man",tashin hankali!hannu ya kai ya cire gilashin idonshi yabi ta da wani irin kallo mai kama dana wanda ya razana duk da ya d'an dake,ganin irin kallon da yake mata ne yasa taci gaba da cewa"ba kaji yan ajin nan jiya sunce ina da Aljanu ba,to cikinsu ne ai wani yazo ya koya man har na iya",
ba iya malam d'in ba har yan ajin sun razana da jin abunda take cewa don duk d'aukar mai Aljanu kowa kema Fatun ita kanta Haulat in Fatuu tayi wani abun takan yi kokonton anya ba da gaske tana da Aljanu ba tunma farkon kawota garin amman yanzu tasan k'arya take ma malamin nasu tunda ta gaya mata wanda ya koya matan kawae iskancinta ne,
"Dama Aljanu suna zuwa wurin mutum in yana dasu ne" malam da yayi sototo yana kallonta yayi tambayar,
"Eh baka ga ko bokaye a film ba suna magana da Aljanu kuma suna ganinsu to ai a fili ma hakane,ni dama in dae raina ya 6aci to suna zuwa ko in wani ya ci zalina,to daka ban Assignment d'in naje gida nayi nayi na kasa shine raina ya 6aci har nayi kuka aikuwa sai ga wani cikinsu ya bayyana da suffar saurayi baka ganshi ba kyakkyawa ne sosae kamar balarabe gashinshi liya liya shine ya rarrashe ni ya koya man nan da nan na iya" ta k'arasa tana wani dashe baki ita ala dole dariya take shikam malam din was completely speechless bin ta kawae yake da ido daka kalle shi zaka fahimci hankalinshi ya tashi Haulat dai sai faman girgiza kai take don ta fahimci ya yarda da Maganar Fatun dama kuma shi bak'o ne bai dad'e da zuwa ba balle yasan halinta da cikin tsoffin malamansu ne ta fad'i ma wani hakan ba lalle su yarda ba tunda sun san halinta,
lumshe ido yayi ya dan jinjina kai,a tunanin Amadu wucewa zaiyi hakan yasa ya dan ja da baya amman sai yaji yace mashi ya shiga Motar,
"Yaya Haisam da kaje kar na 6ata maka lokaci zan hau aca6a" cike da girmamawa yayi Maganar harda dan rankwafowa,
"No problem ka shiga" cikin cool voice dinsa ya fada amsawa yayi da toh ya nufi d'ayan 6arin Motar,gaba ya bude ya shiga ya zauna wani ni'imtaccen sanyi hadi da sanyayyan kamshi suka kai ma hancinshi ziyara har saida ya dan lumshe ido bayan ya rufe kopar haisam yaja suka tafi,tsit kake ji idon haisam na akan hanya shi kam kawu Amadu yayi shiru yana kallon gefen hanya wani irin nishadi yake ji har dan murmushi yake saki,bayan sun hau hanya ne haisam ya tambayeshi wane school yake ya fadi mashi nan take ya gane Makarantar don acan wurin Airport take wato kambarawa,bayan d'an lokaci suka iso Amadu yace ya ajeshi a bakin gate sai ya shiga hannu kawai haisam ya daga mashi alamar ba wani abu ya shige dashi ciki,har gaban Admin block ya kaishi yana kokarin fita ya mika masa kudi 2k yace yayi break, da tsananin mamaki Amadu ya kalli kudin kafin ya kalli haisam,yana so yace mashi ya barsu sai dai sam ya kasa don wani irin kwarjini gareshi gashi ko kallon Amadun ma bai yi ba,hannu ya kai ya amsa hadi da yi mashi godiya daga haka ya bude motar ya fita daidai wasu Abokansa sun taho suna ganinshi suka ja suka tsaya suna kallonshi da mamaki ganin had'addar Motar daya fito wanda a iya saninsu ba'a ta6a kawo shi makarantar a Motar gida ba,tsaye yayi saida haisam din yayi reverse ya juya ya nufi gate kafin ya tunkari abokan nashi yana wani bouncing suna ganin hakan suka sa sowa suna kuranta shi,saida suka gama shegantakar tasu irin ta dalibai sannan suka nufi class.
*** **** ****
Lokacin da su Fatuu suka isa class dinsu Mutum biyu suka iske aciki wurin zamansu suka nufa don su zauna dayake a layin tsakiya suke kuma seat dinsu ne na farko,suna zama Fatuu ta fiddo Assignment dinta tana kara bitar shi haulat dae nata saurararta don ba gane inda ta dosa take ba,a hankali dalibai suka cigaba da zuwa nan da nan ajin ya cika period din farko ta shiga shiru Malamin lissafin bai shigo ba Fatuu duk ta kagara bunu bunu ta kalli kopar shigowa ajin,
"Fatuu gashi nan" Haulat ta fada tana gyara zamanta da sauri fatuu ta kalli kopar daidai malamin ya shigo cikin ajin,wani murmushi ta saki tana kallon haulat,sanye yake da blue jeans da riga mai dogon hannu ya dad'e da bak'in glass,yana shigowa yan ajin suka mike suna gaidashi,seat din farko na layin karshe ya nufa ya d'aura textbook da Allin dake ruke a hannunshi sannan ya kalli Students din fuskarsa ba yabo ba fallasa ya amsa masu gaisuwar kafin yace su zauna,bayan sun zaunan ya juya ya nufi blackboard ya rubuta subject din da yake yi da date yaja layi kafin ya rubuta sabon topic din da suka shiga jiya ya juyo ya dauki textbook din math ya rubuta wasu misalan bayan ya gama ya juyo ya fara masu bayani,itakam Fatuu ganin bai tanka mata ba yasa ta fara tunanin ko ma ya manta da Assignment dinne,saida ya gama yi masu bayanin misalai guda ukku yace in akwae wanda bai ganeba ko mai tambaya yayi,wasu suka fadi abunda basu ganen ba wasu sukayi tambayar saida ya gama dasu kafin ya kalli Fatuu fuska a matukar d'aure yace"where is my Assignment?",
shiru tayi tana binshi da ido hakan yasashi ce mata ta fito gaban Allo,mikewa tayi littafinta a hannu ta fita,
" Who is the class monitor?"ya tambayi yan ajin,
"Malam itace monitar" wasu suka fad'a, jinjina kai yayi ya tambayi ina mataimakiyarta aka nuna mashi Haulat,umarni ya bata taje Staff room ta daukko mashi kujera ta amsa da to kafin ta mike ta nufi hanyar fita,bada jimawa ba ta dawo hannunta ruke da kujerar ta kai mashi inda yake jingine da window ta aje agefenshi kafin ta koma ta zauna,gyara kujerar yayi ya zauna daga haka ya nuna ma Fatuu Allo da hannunshi,
"Ki rubuta Question din dana baki da kuma amsar danace ita zaki samo"amsawa tayi da to,yadda ta amsan a dan sanyaye sai kace batayi Assignment din ba,bayan ta rubuta ta juyo ta kalleshi tun kafin tace wani abu ya tambayi yan ajin sun gama kwafar rubutun tsakiyan allon suka amsa da eh,nuna mata wurin yayi yace ta goge rubutun tayi ma yan ajin bayanin aikin da ya bata har ta gano amsar,shiru tayi tana kallonshi ya dan daka mata tsawa" baki ji mi nace bane!" dan tura baki tayi tace"naji" juyawa tayi ta kalli yan ajin da kowa idonshi na akanta sunyi mata tsuru ba wanda yake tunanin zata iya don sam yanayinta bai nuna ta iyan ba ta galla masu harara,hada ido sukai da haulat ta tura mata baki itakam haulat din dariya tayi ta girgiza kai kawai don halin Fatuu sai ita,shidae math teacher din sai girgiza kafa yake ya dan kya6e baki cikin ranshi kuwa ya tabbatar bazata iya ba hakan yasashi cin alwashin sai ya koya mata hankali,littafinta ruke ahannunta ta fara rubutu a allo bayan ta goge rubutun jikinshi,tambayar ta fara rubutawa kafin ta fara fiddawa tana juyowa tana ma yan ajin bayani,tun tana yi ahankali har ta daga murya ta zage sai uban bayani take kai kace malama ce ke yima dalibai bayani,shin ina malam yake ne?yana dai azaune yayi tsitt sai bin ta da ido yake cike da mamaki abun ya matukar daure mashi kai don bai ta6a tunanin zata iya ko kusa da yadda take yi ba,gashi abunda ma yafi bashi mamaki shine yadda take bayanin ba tare da tana kallo a wani wuri ba da kai take yi,lokacin data zo karshe ta gano irin amsar tashi sai ta juyo ta kalli yan ajin da suka yi sototo suna sauraranta wasu bakinsu a bud'e saboda mamaki,
"kun gane ko asake yi maku bayani?"ta tambayesu tana murmura idanu had'i da sa hannu guda ta dafa kugu,gaba daya suka ce sun gane,juyawa tayi ta kalli malam da har lokacin idonshi na sanye cikin gilashi tace" Gashi nan na fidda har na gano amsar irin taka,nayi daidai ko?"ta tambaya da d'an Murmushi tana d'age ido,farko shiru yayi yana ta kallonta har saida ta k'ara tambayar tayi daidai sannan ya daga mata kai alamar eh,
"To tunda nayi daidai kace a tafa man ko" ta fad'a tana tura baki,d'an jinjina kai yayi yai wani guntun Murmushi da alama ta kashe shi da mamaki sai kace ba mai laifi ba har wani neman atafa mata take, ganin haka yasa tace"yanzu duk wannan uban aikin da nayi malam baza'a tafa man ba" ta k'arasa tana ta tura baki,kallon yan ajin yayi yace su tafa mata aikam kaman da gayya suka fara uban tafi kilan kuma murna suke Allah ya raba su da alakakai,
"Malam shikenan inje in zauna ko tunda dai nayi daidai ae ba batun punishment ko?" ta fad'a tana gwalo ido,d'aga mata kai yayi alamar eh, har ta juya ya tsaidata don ya kasa hakuri so yake yaji yadda akai ta fidda Assignment din don shi kanshi yana a shekararshi ta k'arshe aka basu Assignment d'in wanda ba karamar wuya yasha ba wurin fidda shi,
" Waya koya maki?" yayi tambayar fuskarshi ba wasa,d'age gira tayi tace"Assignment d'in?"kai ya daga alamar eh,d'an murmushi tayi da bud'ar bakinta sai cewa tayi"wani Aljani ne acikin Aljanuna yazo ya koya man",tashin hankali!hannu ya kai ya cire gilashin idonshi yabi ta da wani irin kallo mai kama dana wanda ya razana duk da ya d'an dake,ganin irin kallon da yake mata ne yasa taci gaba da cewa"ba kaji yan ajin nan jiya sunce ina da Aljanu ba,to cikinsu ne ai wani yazo ya koya man har na iya",
ba iya malam d'in ba har yan ajin sun razana da jin abunda take cewa don duk d'aukar mai Aljanu kowa kema Fatun ita kanta Haulat in Fatuu tayi wani abun takan yi kokonton anya ba da gaske tana da Aljanu ba tunma farkon kawota garin amman yanzu tasan k'arya take ma malamin nasu tunda ta gaya mata wanda ya koya matan kawae iskancinta ne,
"Dama Aljanu suna zuwa wurin mutum in yana dasu ne" malam da yayi sototo yana kallonta yayi tambayar,
"Eh baka ga ko bokaye a film ba suna magana da Aljanu kuma suna ganinsu to ai a fili ma hakane,ni dama in dae raina ya 6aci to suna zuwa ko in wani ya ci zalina,to daka ban Assignment d'in naje gida nayi nayi na kasa shine raina ya 6aci har nayi kuka aikuwa sai ga wani cikinsu ya bayyana da suffar saurayi baka ganshi ba kyakkyawa ne sosae kamar balarabe gashinshi liya liya shine ya rarrashe ni ya koya man nan da nan na iya" ta k'arasa tana wani dashe baki ita ala dole dariya take shikam malam din was completely speechless bin ta kawae yake da ido daka kalle shi zaka fahimci hankalinshi ya tashi Haulat dai sai faman girgiza kai take don ta fahimci ya yarda da Maganar Fatun dama kuma shi bak'o ne bai dad'e da zuwa ba balle yasan halinta da cikin tsoffin malamansu ne ta fad'i ma wani hakan ba lalle su yarda ba tunda sun san halinta,