Sashe 12
Asanadin Makwabtaka Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
K'arfe sha biyu da rabi na rana daidai aka tashe su kasantuwar ranar juma'a ce,Haulatu ce tsaye tana ta faman kwala ma Fatuu kira "fatuu ki taho mu tafi kar acika bus d'in kinsan yau Juma'a fa gaba daya ake tashi harda seniors" ita kuwa fatun tana can sai faman bin students take da gudu tana bugun su,wai na bankwana daga yau sai Monday,girgiza kai Haulat take tayi don ta gaji da tsayuwar,sai da ta gama buge bugen ta taho da d'an gudu sai faman nishi take tana daria, jakarta a hannu d'aya,
Dafa kafad'ar Haulat tayi da dayan hannun tace muje k'awalliya,juyawa kawai haulat tayi bata ce mata komae ba suka tafi.
Abunda haulat ke gudu shi ya faru don kuwa School Bus d'in ta cika dam sai dai su tsaya a tsaye ko su zauna a k'asa,Haulat ta kalli Fatu tace"Kinga abun da kika ja mana ko,da ana tashi muka taho ai da mun samu seat kika tsaya shiririta,yanzu ai sai mu zauna a k'asan" ta k'arasa maganar da dan 6acin rai,fatuu tace"tabb nikam bazan zauna a k'asa ba duk a tattake ni,ga k'asan ma duk k'asar sandals din mutane,"To ya zamuyi,nidai ban iya tsayuwa gaskia da anzo tudu ko wurin yin kwana mutum yayi ta bugewa" inji Haulat,
"ki tsaya kika ga ni,sai na samu seat d'in zama" fatuu tayi maganar yayin da take kutsawa cikin Bus d'in,hango wata yar senior section tayi wadda unguwar su d'aya don tare suke hawa Bus a bakin titi,su biyu ne a zaune,a daidai wurin su ta tsaya tace "D'an matsa man in zauna, "Kamarya? Yarinyar ta tambaya,fatuu tace "Ai ku biyu ne kuma har mutum ukku ana zama ko" tayi maganar tana turo baki,"To in mu biyu ne mu tsaranki ne? Fatuu tace "Yo ina ruwan mota da wani tsara ai dai duk makaranta d'aya muke ko" da sauri yarinyar ta nunata da yatsa tace"Ke karki yi man rashin kunya yanzun nan in mari wannan kumatun naki,dama naji ance baki da kunya to ni in kika yiman zane ki zanyi wallahi" da alama itama yarinyar masifaffa ce, cikin harzuka fatuu tace "Ki zane wa,ai ni wallahi nafi k'arfin ki zane ni sai dai mu zane juna,don ba fina k'arfi kikai ba ehee" ta murgud'a mata baki,da sauri yarinyar ta yunk'uro zata mari Fatuu,ita kuma fatun tayi saurin kaucewa....Sauran Students din cikin motar ne suka had'a baki wurin cewa"Kwandasta ana fad'a" da sauri Haulat ta nufi inda fatuu take bata san mike faruwa ba,amman tana jin ance ana fad'a tasan da Fatuu ne,shima kwandastan ya nufo ciki yana fadin"suwa ke mana fad'an? "gasu nan" students suka ce,
daidai inda suke ya tsaya yarinyar ta rik'e wuyan hijabin Fatuu itama fatun haka sunyi cirko cirko,cikin daka tsawa Kwandastan yace"ku saki juna!! Kowa ya saki kowa,yaci gaba"miya had'a ku" da sauri yarinyar tace"Wannan yar rainin wayon ce,wai sai mun matsa mata ta zauna,kuma na gaya mata ba wuri amman zata yima mutane rashin kunya sai kace wani ya hanata tazo da wuri..." ta k'arasa maganar tana ta huci ita kuwa Fatuu ta cika famm kaman zata fashe sai hararar yarinyar take,kwandastan ya juya wurin ta yace "Ah kece baki da gaskia,tunda an riga ki sai ki hakura ki zauna a k'asa ko ki tsaya ki rike karfe,In kuma baki iyawa sai ki hakura ki fita kawai,Amman kar wanda ya kara yimana fad'a,in ba haka ba zan kori mutun ne" ya juya ya nufi gaban motar yana jaddada masu abunda yace.
Haulat ce ta kama hannun fatuu wadda ta cika fam,tana yima yarinyar wani irin kallo,"Zo mu zauna a k'asan kawai fatuu don Allah ki kyale ta kar a kore mu kin...."da karfi Fatuu ta fuzge hannunta,ita kuwa yarinyar sai faman cika take tana batsewa tana wani yamutsa fuska.
Wata student ce yar junior section acan dayan 6angaren motar tace"Fatuu zo ki zauna ga wuri na matsa maki" k'wafa fatun tayi ta duk'a ta dauki jakarta wadda ta yarda lokacin da zata rike hijabin yarinyar da suke fada,ta nufi inda aka matsa mata ta zauna,ita kuwa haulat baiwar Allah wuri ta samu a k'asa ta zauna sam bata iya tsayuwar.
Adaidai kan kwanar da aka saba aje yan unguwar Bus din ta tsaya students d'in unguwar suka fara fitowa harda su Fatuu,sannan yarinyar da sukai fad'an itama ta fito tana ta suratai da kawayenta yan senior guda biyu"Yan section d'insu ke tsoronta shiyasa take masu iskanci,ni in yarinya tace zata yi man wallahi maganinta zanyi yadda gobe ko ance taja wani fad'a bazata yi ba,hakanan azo garin mu ana cin arzikin mu kuma ace za'a rik'a yimana iya shegeee" wata cikin kawayen tace"Wai daman ba yar nan garin bace? "Eh yar jahar Adamawa ce,da gani ma acan d'in yar k'auye ce irin yan rugar nan,kinsan dan k'auye daya samu wuri sai iya shege iri iri" k'awayen suka tuntsire da daria,d'aya tace"kai Murja" wadda aka kira da murja tace "Allah kuwa,duk tabi ta Addabi mutane,duk da ba a layin gidansu nike ba,a layin bayansu muke inajin labarin iskancinta,shiyasa a cikin Bus din nan naso in saita mata hankali da kwandastan nan bai zo ba,tasan ni ban tsoronta" duk maganganun da suke a kunnan Fatuu don a bayansu suke kuma da karfi yarinyar ke maganar don Fatun taji,
A farkon kwanar gidansu kawayen nata yake,Murja tace "bari in biyo ku inyi fitsari" suka shige tare,tsayawa fatuu tayi wadda kiris ya rage ta fashe don fushi tana kallon gidan da suka shiga,Haulat tayi saurin cewa"Don Allah,mu tafi Fatuu,karki biye mata" tana kokarin janta" k'in tafiya fatun tayi ta cije a wurin haulat taci gaba "In kika tsaya yin fad'a yanzun nan kinsan za'aje a fad'i ma gwaggo gara ki rabu da ita kawai" A hankali Fatun ta juya suka fara tafiya amman ba haka taso b..,can ta tuna ai gwaggon ma ta tafi aiki tunda ta tabbatar mata bazata dawo ta iske ta ba,da sauri Fatuu ta mika ma haulat jakarta tace"Ki tafi man da ita gidan ku,da safe sai kitaho man da ita Islamiyya",
"Ina zaki kuma?" haulat ta tambaya fatun tace"Na manta ne gwaggo ta aike ni..." Haulat tace "to mutafi tare man....da sauri Fatu tace"A'a kije kawai ni kad'ai zanje" Haulat ta girgiza kai tace "ba wani aiken ki da akai fad'an dai zaki tsaya ko...?da tsiwa Fatuu tace "Eh d'in fadan zan tsaya ina ruwanki" haulat tace"Don Allah fatuu kiyi hakuri mana"
"Inyi hakuri? Kinajin yadda take gaya man maganganun banza zaki wani ce inyi hakuri, to wallahi bazan yi ba" Haulat tace "haba fatuu,Allah fa yana tare da masu hakuri..."
"To ni banda hakurinn ehe" Fatuu tace,hannu haulat tasa ta rufe baki, jin abunda Fatun tace.
Ganin haka yasa fatuu ci gaba da magana"Ai ba haramun bane in anyi ma mutum abu yaji bai iya yafewa ya rama,ke komai akai sai kice ma mutum yayi wai hakuri shikenan so kike a raina ni,inzama sakarya kamar ki ko" cikin sanyin murya Haulat tace"Ni babu wanda ya raina ni,kinga wani na tsokanata ne? Kuma yin hakuri ba sakarci bane,wani lokacin rashin hakuri ba abunda yake ja ma mutum sai dana sani mara Amfani,gara ma kayi hakurin tunda Allah da kansa yace yana tare da masu hakuri,in kayi hakurin sai kiga ya saka maka ta inda bakai zato ba"daga haka ta mik'a ma Fatu hannu,ta bata jakar,ita kuma ta juya don tasan ba lalle ta iya hanata yin fad'an ba,
cikin d'aga murya Fatuu tace "In ma k'ara ta zaki ki kai to gwaggon bata nan tana wajen Aiki" girgiza kai kawai Haulat tayi batare da tace mata komai ba bare ma ta juyo.
Wani gida dake kallon jikin gidan da Murja ta shiga nan Fatuu ta shiga ta 6oye a bayan k'aure tana lek'o waje ta tsagar jikin kofar jira kawai take taga fitowarta,Aikuwa bata fi minti biyar ba sai ga murja ta fito tana yarfe hannunta da alama ruwa ne a hannun,da sauri fatuu ta cire hijabinta ta d'aure ta tamau a k'ugu ta k'ara gyara d'aurin kallabinta,sai da ta bari murjar ta wuce kofar gidan data 6uyan ta fito cikin sand'a tamkar mage na shirin kama k'adangare da gudu ta shak'o murja ta baya cikin sa'a ta kada ita k'asa ta fara bugu dama Fatuu badai karfi ba gashi takai mata hari ta baya sai faman bugunta take,tana fad'in "kafin kiyi magani na ni zanyi naki" cikin wahala murja tace "Don Allah kiyi hak.....bugu Fatuu takai mata a baki nan take bakin ya fashe tace "hak'urin uwarki zanyi,badai ni kike ce ma yar kauye ba, aikam zaki ga yar k'auye,
Lokaci guda yara suka kewaye su suna kallon fada,yawanci duk d'alibai ne masu dawowa daga makaranta had'i da Almajirai ba wanda yayi yunk'urin raba su don yaran sun san halin Fatuu.
Dafa kafad'ar Haulat tayi da dayan hannun tace muje k'awalliya,juyawa kawai haulat tayi bata ce mata komae ba suka tafi.
Abunda haulat ke gudu shi ya faru don kuwa School Bus d'in ta cika dam sai dai su tsaya a tsaye ko su zauna a k'asa,Haulat ta kalli Fatu tace"Kinga abun da kika ja mana ko,da ana tashi muka taho ai da mun samu seat kika tsaya shiririta,yanzu ai sai mu zauna a k'asan" ta k'arasa maganar da dan 6acin rai,fatuu tace"tabb nikam bazan zauna a k'asa ba duk a tattake ni,ga k'asan ma duk k'asar sandals din mutane,"To ya zamuyi,nidai ban iya tsayuwa gaskia da anzo tudu ko wurin yin kwana mutum yayi ta bugewa" inji Haulat,
"ki tsaya kika ga ni,sai na samu seat d'in zama" fatuu tayi maganar yayin da take kutsawa cikin Bus d'in,hango wata yar senior section tayi wadda unguwar su d'aya don tare suke hawa Bus a bakin titi,su biyu ne a zaune,a daidai wurin su ta tsaya tace "D'an matsa man in zauna, "Kamarya? Yarinyar ta tambaya,fatuu tace "Ai ku biyu ne kuma har mutum ukku ana zama ko" tayi maganar tana turo baki,"To in mu biyu ne mu tsaranki ne? Fatuu tace "Yo ina ruwan mota da wani tsara ai dai duk makaranta d'aya muke ko" da sauri yarinyar ta nunata da yatsa tace"Ke karki yi man rashin kunya yanzun nan in mari wannan kumatun naki,dama naji ance baki da kunya to ni in kika yiman zane ki zanyi wallahi" da alama itama yarinyar masifaffa ce, cikin harzuka fatuu tace "Ki zane wa,ai ni wallahi nafi k'arfin ki zane ni sai dai mu zane juna,don ba fina k'arfi kikai ba ehee" ta murgud'a mata baki,da sauri yarinyar ta yunk'uro zata mari Fatuu,ita kuma fatun tayi saurin kaucewa....Sauran Students din cikin motar ne suka had'a baki wurin cewa"Kwandasta ana fad'a" da sauri Haulat ta nufi inda fatuu take bata san mike faruwa ba,amman tana jin ance ana fad'a tasan da Fatuu ne,shima kwandastan ya nufo ciki yana fadin"suwa ke mana fad'an? "gasu nan" students suka ce,
daidai inda suke ya tsaya yarinyar ta rik'e wuyan hijabin Fatuu itama fatun haka sunyi cirko cirko,cikin daka tsawa Kwandastan yace"ku saki juna!! Kowa ya saki kowa,yaci gaba"miya had'a ku" da sauri yarinyar tace"Wannan yar rainin wayon ce,wai sai mun matsa mata ta zauna,kuma na gaya mata ba wuri amman zata yima mutane rashin kunya sai kace wani ya hanata tazo da wuri..." ta k'arasa maganar tana ta huci ita kuwa Fatuu ta cika famm kaman zata fashe sai hararar yarinyar take,kwandastan ya juya wurin ta yace "Ah kece baki da gaskia,tunda an riga ki sai ki hakura ki zauna a k'asa ko ki tsaya ki rike karfe,In kuma baki iyawa sai ki hakura ki fita kawai,Amman kar wanda ya kara yimana fad'a,in ba haka ba zan kori mutun ne" ya juya ya nufi gaban motar yana jaddada masu abunda yace.
Haulat ce ta kama hannun fatuu wadda ta cika fam,tana yima yarinyar wani irin kallo,"Zo mu zauna a k'asan kawai fatuu don Allah ki kyale ta kar a kore mu kin...."da karfi Fatuu ta fuzge hannunta,ita kuwa yarinyar sai faman cika take tana batsewa tana wani yamutsa fuska.
Wata student ce yar junior section acan dayan 6angaren motar tace"Fatuu zo ki zauna ga wuri na matsa maki" k'wafa fatun tayi ta duk'a ta dauki jakarta wadda ta yarda lokacin da zata rike hijabin yarinyar da suke fada,ta nufi inda aka matsa mata ta zauna,ita kuwa haulat baiwar Allah wuri ta samu a k'asa ta zauna sam bata iya tsayuwar.
Adaidai kan kwanar da aka saba aje yan unguwar Bus din ta tsaya students d'in unguwar suka fara fitowa harda su Fatuu,sannan yarinyar da sukai fad'an itama ta fito tana ta suratai da kawayenta yan senior guda biyu"Yan section d'insu ke tsoronta shiyasa take masu iskanci,ni in yarinya tace zata yi man wallahi maganinta zanyi yadda gobe ko ance taja wani fad'a bazata yi ba,hakanan azo garin mu ana cin arzikin mu kuma ace za'a rik'a yimana iya shegeee" wata cikin kawayen tace"Wai daman ba yar nan garin bace? "Eh yar jahar Adamawa ce,da gani ma acan d'in yar k'auye ce irin yan rugar nan,kinsan dan k'auye daya samu wuri sai iya shege iri iri" k'awayen suka tuntsire da daria,d'aya tace"kai Murja" wadda aka kira da murja tace "Allah kuwa,duk tabi ta Addabi mutane,duk da ba a layin gidansu nike ba,a layin bayansu muke inajin labarin iskancinta,shiyasa a cikin Bus din nan naso in saita mata hankali da kwandastan nan bai zo ba,tasan ni ban tsoronta" duk maganganun da suke a kunnan Fatuu don a bayansu suke kuma da karfi yarinyar ke maganar don Fatun taji,
A farkon kwanar gidansu kawayen nata yake,Murja tace "bari in biyo ku inyi fitsari" suka shige tare,tsayawa fatuu tayi wadda kiris ya rage ta fashe don fushi tana kallon gidan da suka shiga,Haulat tayi saurin cewa"Don Allah,mu tafi Fatuu,karki biye mata" tana kokarin janta" k'in tafiya fatun tayi ta cije a wurin haulat taci gaba "In kika tsaya yin fad'a yanzun nan kinsan za'aje a fad'i ma gwaggo gara ki rabu da ita kawai" A hankali Fatun ta juya suka fara tafiya amman ba haka taso b..,can ta tuna ai gwaggon ma ta tafi aiki tunda ta tabbatar mata bazata dawo ta iske ta ba,da sauri Fatuu ta mika ma haulat jakarta tace"Ki tafi man da ita gidan ku,da safe sai kitaho man da ita Islamiyya",
"Ina zaki kuma?" haulat ta tambaya fatun tace"Na manta ne gwaggo ta aike ni..." Haulat tace "to mutafi tare man....da sauri Fatu tace"A'a kije kawai ni kad'ai zanje" Haulat ta girgiza kai tace "ba wani aiken ki da akai fad'an dai zaki tsaya ko...?da tsiwa Fatuu tace "Eh d'in fadan zan tsaya ina ruwanki" haulat tace"Don Allah fatuu kiyi hakuri mana"
"Inyi hakuri? Kinajin yadda take gaya man maganganun banza zaki wani ce inyi hakuri, to wallahi bazan yi ba" Haulat tace "haba fatuu,Allah fa yana tare da masu hakuri..."
"To ni banda hakurinn ehe" Fatuu tace,hannu haulat tasa ta rufe baki, jin abunda Fatun tace.
Ganin haka yasa fatuu ci gaba da magana"Ai ba haramun bane in anyi ma mutum abu yaji bai iya yafewa ya rama,ke komai akai sai kice ma mutum yayi wai hakuri shikenan so kike a raina ni,inzama sakarya kamar ki ko" cikin sanyin murya Haulat tace"Ni babu wanda ya raina ni,kinga wani na tsokanata ne? Kuma yin hakuri ba sakarci bane,wani lokacin rashin hakuri ba abunda yake ja ma mutum sai dana sani mara Amfani,gara ma kayi hakurin tunda Allah da kansa yace yana tare da masu hakuri,in kayi hakurin sai kiga ya saka maka ta inda bakai zato ba"daga haka ta mik'a ma Fatu hannu,ta bata jakar,ita kuma ta juya don tasan ba lalle ta iya hanata yin fad'an ba,
cikin d'aga murya Fatuu tace "In ma k'ara ta zaki ki kai to gwaggon bata nan tana wajen Aiki" girgiza kai kawai Haulat tayi batare da tace mata komai ba bare ma ta juyo.
Wani gida dake kallon jikin gidan da Murja ta shiga nan Fatuu ta shiga ta 6oye a bayan k'aure tana lek'o waje ta tsagar jikin kofar jira kawai take taga fitowarta,Aikuwa bata fi minti biyar ba sai ga murja ta fito tana yarfe hannunta da alama ruwa ne a hannun,da sauri fatuu ta cire hijabinta ta d'aure ta tamau a k'ugu ta k'ara gyara d'aurin kallabinta,sai da ta bari murjar ta wuce kofar gidan data 6uyan ta fito cikin sand'a tamkar mage na shirin kama k'adangare da gudu ta shak'o murja ta baya cikin sa'a ta kada ita k'asa ta fara bugu dama Fatuu badai karfi ba gashi takai mata hari ta baya sai faman bugunta take,tana fad'in "kafin kiyi magani na ni zanyi naki" cikin wahala murja tace "Don Allah kiyi hak.....bugu Fatuu takai mata a baki nan take bakin ya fashe tace "hak'urin uwarki zanyi,badai ni kike ce ma yar kauye ba, aikam zaki ga yar k'auye,
Lokaci guda yara suka kewaye su suna kallon fada,yawanci duk d'alibai ne masu dawowa daga makaranta had'i da Almajirai ba wanda yayi yunk'urin raba su don yaran sun san halin Fatuu.