← Book details Sooraj Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 48 OF 91

Sashe 48

Sooraj Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Zieyaderh Oummu taƙira sunanta, "Na'am" ta amsa asanyaye.  "karki manta inkin dawo ki sameni aɗakina kinsan gobene tafiyarmu"  "To" kawai tace sannan ta juya tafice daga cikin falon, tana fitowa compound ɗin gidan shikuma motarsa na fita daga cikin gidan,  mota tashiga ranta duk ba daɗi.
Ko amakaranta yau bata wani sake ba, bayan sundawo break ne aka turo wae principal na ƙiranta, saida gabanta yafaɗi amma haka ta daure taje, wata leda ya bata wanda ke ɗauke da wasu sabbin uniform har kala uku yace mata daga yau su zatana sanyawa. Sosai tayi mamaki amma sai bata nunaba ta amsa kawai ta fice, koda taje aji suka duba kayan, sket ne irin high waist ɗinnan wanda ƙasansa yake da faɗi, sai kuma wata ƴar rigar makaranta fitted da hijab ɗinta wanda idan tasa zai ɗan sauƙo mata kaɗan.   Mamakine ya kashesu su dukansu.  Shukra ce tace "Wannan fa kayan bakowa kesawa a school ɗinnan ba, kodai kinzama house wife ne bamusani ba?"   hararanta Zieyaderh tayi tare da turo baki gaba cikin takaici tace "Ni bawata house wife ɗin dana zama!" dariya suka sanya su dukansu, daga haka sukaci gaba da hiransu, kaɗan kaɗan take sa musu baki.   Har aka tashi sukuku  haka takejin kanta, koda ta koma gida ko falo bata sauƙo ba, haka ta ƙare kwanciyarta aɗaki...  Washegari   Saturday.     Ƙarfe 8 daidai ta kammala shiryawa cikin kayan da Oummu ta bata tace tasanya, riga da sket ne na tsadaddiyar atamfar Vlisco, wacce taji ɗinki, sket ɗin irin pieces ɗinnan ne yayinda rigan takasance fitted, sosai kayan suka amshi jikinta, kasancewar atamfar kalan Maroon gareta hakan yasanya ta sanya maroon hijab ajikinta, sosai tayi kyau duk da cewa batayi wani kwalliya akan fuskarta ba,  flat shoe ɗinta ta sanya tare da  kallon kanta amadubi, ita kanta tasan tayiwa kanta kyau.      Saida suka biya ta wani super market Oummu tayi sayayya sannan suka ɗauki hanyar zuwa KD inda acan ƙauyen su Zieyaderh yake.  Ƙarfe 1 na rana daidai suka iso cikin ƙauyen nasu na Saminaka, tun daga lokacin ƙirjin Zieyaderh ke dukan uku uku,   da ƙyar take iyayiwa Kamalu driver kwatance har suka iso ƙofar wahalallen gidansu,  tun shigowarsu ƙauyen yara kebinsu yayinda manya kuwa ke bin haɗaɗɗiyar motarsu da kallo.    Shawo kwanan Malam Garba kenan hannunsa ɗauke da wani buhu, turus haka yaja ya tsaya yana me bin motar daya gani fake aƙofar gidansa da kallo.  Da sauri ya ƙarasa daidai lokacin kuma su dukansu suka fito daga cikin motar, koda zata shekara ɗari ne batanan bazai taɓa kasa gane jininsa ba, bakinsa abuɗe fuska ɗauke ɗa mamaki yake kallon Zieyaderh, itama kallonsa take lokaci guda hawaye suka wanke mata fuska, ji take kamar taje ta rungume Baban nata, amma kuma tanajin tsoro.  "Ziyada!" yaƙira sunanta muryarsa na rawa.  Kasa amsa masa tayi sai kawai ta fashe da kuka.  Shima hawayene kwance acikin idanunsa. Kamar wadda aka wurgo daga sama haka Inna Ma'u tafito daga cikin gidanta, don tuni labari yakai mata cewa wata haɗaɗɗiyar mota fa faka aƙofar gidanta.  Bakinta awangale taƙarasa gaban yarinyar da take kallonta kamar Zieyaderh, hannu tasa taɗan taɓa fuskar yarinyar dake kuka,   "Laaaaa ha'ila wallahi itace, shegiyar gari kin gama gararanbanki kindawo ko?" Inna Ma'u tafaɗa tana me ƙarewa Zieyaderh kallo, mamaki kuwa aranta kamar zai kasheta.  Ƙasa Zieyaderh tayi da kanta, Malam Garba shine wanda ya kama hannunta tare da duban Oummu dake tsaye yace.
"Hajiya kushigo daga ciki!" Babu musu Oummu ta bi bayansa yayinda yake riƙe da hannun Zieyaderh, aikuwa Inna Ma'u ma rufa musu baya tayi bayan ta tsaya ta gama ƙarewa motar da sukazo da ita kallo, harwani yawu ta haɗiya natsananin kwaɗayi dason abun duniya, musamman ma da ta hango ɗan ragowan lemun fanta dake gaban motar. 

Gudu gudu sauri sauri haka taje ta ɗauko tabarma ta shumfuɗawa Oummu baki har kunne tace "Hajiyan Birni zauna mana!"  Murmushi Oummu tayi tana me kallonta sannan ta zauna aranta tace "Kamar bayanzu tagama zagi ba"  Malam Garba da kansa ya kawo musu ruwa, ita dai Zieyaderh laɓewa tayi abayan Oummu, don har cikin ranta tana jin tsoron abun dazai biyo baya.  

Gyara zama Oummu tayi tare da ɗagawa baban Zieyaderh gaisuwa, amutumce ya amsa, kafun tasake wata magana Inna Ma'u tayi saurin cewa. "Mutanen Binni Sannu marabanki da zuwa Hajiya!"  Still murmushi Oummu  tayi tare da jinjina kanta alaman yauwa.   Batare da ta bari kowa acikinsu yace wani abuba tace "Lallaima Zieyaderh wato dakika gudu kaina kikeso na aurawa tsoho ɗan dashen? ko kuwa kina tsammanin nida ubanki muna da kuɗin da zamu biyasa abun daya kashe ne, wallahi mudai kin cucemu akan guduwarki saida duk wani ɗan abun dana mallaka ya ƙare saboda ɗan dashe cewa yayi sai mun biyasa kudin daya kashe,  kin cuceni kin cuci mahaifinki wallahi!!" Imma Ma'u tafaɗi haka tana me matse wasu munafukan hawayen ƙarya data ƙaƙalosu da ƙyar.    Sake cewa tayi "Amma Allah ne zai mana sakayya, koda yake ma ai yanzu nasan kintara kuɗi sosai ko bakomai zan fanshe asarata" tana murmushi ta ƙare maganar.   Oummu kam mamaki al'ajabi haɗi da tsoro al'amarin matar ya bata, wato dai ita ko agaban wayene bazata iya ɓoye maitanta ba.  Cikin sauri taɓuɗi baki zata sake cewa wani Abu, da sauri Malam Garba yace "Ya isa haka Ma'u, dafari ya kamatane mufara sanin ina taje bawai irin waƴannan kalaman yakamata ayi mata ba" afusace Inna Ma'u tajuya zata faɗa masa baƙar magana sai kuma tatuna da wani abu tafasa. Saita fara yaƙen ƙarya tana me ƙarewa komai dake jikin Zieyaderh kallo. 

Murmushin takaici Oummu tayi tare da kai dubanta ga Baban Zieyaderh, sannu ahankali tayi masa bayani akan cewa ɗantane ya tsinci Zieyaderh bawai yawon iskanci ta tafi ba.   Ajiyar zuciya me ƙarfi Malam Garba ya sauƙe tare dayiwa Allah godiya daya sanya ƴarsa ta faɗa hannu na gari.  Itakuwa Inna Ma'u afakaice take hararan Oummu aranta kuwa cewa tayi "Kuji ƙaryan banza, yo koma gaskiya ne wayasan abunda sukeyi dashi ɗannaki, kai banma yarda ba yanda yarinyarnan tayi ɓul ɓul da ita akwai abun da take aikatawa wata ƙilama cikine da ita"   tana gama ƙimtsa zancen zucinta tayiwa Zieyaderh ƙuri, ba inda take kallo kamar cikinta, wai adole saita gano ko cikine da ita, burinta bai wuce taga tumbinnata yaɗan taso ba ta tabbatar da zarginta.   

Godiya sosai Malam Garba ya shiga yiwa Oummu na irin riƙon amanar da tayiwa ƴarsa, don har acikin ransa yana me nadamar irin rashin kulawan daya nuna mata abaya, sannan kuma yana ƙaunar ƴarsa sosai, dan itace kaɗai jininsa aduniya, amma yazaiyi da sharri da kuma tsoron Inna Ma'u da yake, duk itace ummul aba'isin faruwar komai.   Miƙewa yayi yace zaije ya samo musu fura.   Aikuwa yana fita Inna Ma'u tace "Hajiyan birni ince dai ɗannaki daya tsinceta gidanki ya kawota ba gidansa ba?" 

Mamakine ya kama Oummu cike da mamakin tambayar tace "Mekike nufi?"  da sauri Inna Ma'u ta washe baki tare da cewa "A'a babu abun danake nufi kawai dai tambaya ne,  ke Zieyaderh cire lufayan mana kisha iska" Tafaɗa cike da zaƙuwan son ganin yanda cikar halittan Zieyaderh'n ya koma, tayi rantsuwa matuƙar taga cikin Ziryaderh yaɗan tasa to wallahi saita cucesu maƙudan kuɗaɗe.  (Chaii guys Inna Ma'u fa ta tsananta😆) 

Kallon Oummu Zieyaderh tayi, idanu Oummu ta mata alaman karta cire mayafinta, aikuwa saita yi burus da maganan Inna Ma'u. Wani irin malolon baƙin cikine ya cika zuciyar Inna Ma'u, don sarai ta ga lokacin da Oummu tayiwa Zieyaderh'n idanu.    Aranta tace "Wallahi ko zaku mutune saina laƙaba muku wani sharrin dasai kunbani kuɗi ƴan iska"     

Babu jimawa Malam Garba ya dawo hannunsa ɗauke da ƙwaryan nono, babu wani ƙyama haka Oummu ta zage tasha nonon daganan tace da Malam Garba idan ba damuwa tanaso tayi magana dashi.    "Magana kuma dashi kaɗai?" Inna Ma'u ta tambaya tana zare ido.  Babu wanda ya kulata saima iso da Malam Garba yayiwa Oummu zuwa soro tayanda babu wanda zaiji abun da suka tattauna, cike da fahimtan juna Oummu tayi masa bayanin duk wani abu dake tafe da ita, har acikin ransa yayarda da matar da kuma kamalanta saboda haka atake ya amincewa buƙatarta baƙaramin daɗi Oummu taji ba, nan suka tsaida magana cewar zata turo manya don atsaida magana, inda shikuma yace ko babu wasu manya ya yarda da ita ya bawa Ɗanta Almustapha Auren Ƴarsa Zieyaderh, duk lokacin da suka shirya kawai suzo ayi biki.

(uhhhh guys kushiryafa kuna da biki😝)

*Vote and Comment*
    
        
           fatymasardauna

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
           
             *SOORAJ!!!*

    *Written By*
Phatymasardauna

*Dedicated To My Life (Sardauna)*
       
            *WATTPAD*
      @fatymasardauna
#romance

*This page is dedicated to you my dear @Zeety delight... heart you dear*

            *Chapter 37*

Da tsananin farinciki ɗauke akan fuskar ko wannensu Oummu da Malam Garba suka shigo cikin gidan, Inna Ma'u na ganin hakan wani ƙaton baƙinciki ya ɗarsu azuciyarta, hakanan taji ajikinta cewa hanyar ƙaruwa suka tattauna, ae kuwa nan ta ƙudura aranta cewa Oummu na tafiya sai tayi maganin Malam Garba, yadae santa ae yakuma san wacece ita.

Kallon Zieyaderh Oummu tayi fuska ɗauke da murmushi tace "Inaga ya kamata ae ace mutafi tun yanzu, kada tafiyan dare ya kamamu"   
Jin abun da Oummu tace yasanya ƙirjinta bugawa, ahankali ta ɗago idanunta tare da ɗan satan  kallon mahaifinnata, cikin rashin sa'a tasamu shiɗinma kallonta yake, da sauri tayi ƙasa da kanta, murmushi yayi tare da cewa "Bakomai kuje Zieyaderh Allah Yakiyaye hanya ya tsare, nima inanan zuwa tunda yanzu nasamu adreshin inda kuke." 
Wani irin sanyi ne Zieyaderh taji na ratsa zuciarta, sam batayi tunanin mahaifinta zai barta ta koma ba. 
Chapter 48 · 0% Book details