← Book details Sooraj Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 28 OF 91

Sashe 28

Sooraj Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Na faɗama ka kwantar da hankalinka Alhaji, Insha Allah Sooraj zai farfaɗo nan bada jimawa ba, sai dai kawai akwai wata matsalane da sai yanzu, da mukayi masa gwaji muka san da ita!"  Dr.Mohd yafaɗi haka yana mai shakkan abun da zai faɗawa Alh.Mansur, kasancewar baisan tayaya Alhaji'n zai ɗauki maganartasa ba. 

"Innalillahi wa'inna ilaihirraju'n!! Doctor mai kuma yasake faruwa?" Alhaji Mansur ya tambaya cike da damuwa.

"Amm bawata matsalabace Alhaji matuƙar za akula,  nace dama tuncan kunsan cewa yana ɗauke da ciwon zuciya ne?"  

Ai tamkar rugugin aradu haka Alhaji Mansur yaji sauƙan kalaman Dr.Mohd acikin kunnuwansa.

Daɓas haka Alhaji Mansur ya zauna tare da sanya hanu ya dafe kansa.  "Innalillahi wa'inna ilaihirraju'un!!" kawai yaketa ambata acikin rai da zuciyarsa.  "Shikenan kuma lokacin dazai rasa ɗansa mafi soyuwa agaresa yazo, haƙiƙa  wannan ƙaddaran tana da girma agaresu baki ɗaya, Allah yabasu ikon cinyeta!" yafaɗi haka acikin zuciyarsa.

Aƙalla yaɗauki kusan sama da 12 minute ahaka,
Idanunsa da sukai jajur dasu ya ɗago ya kalli Dr.Mohd. 

"Idan nafahimci kalamanka Doctor kanaso kace dani Sooraj É—ana yana É—auke da ciwon zuciya ko?"

"Ƙwarai kuwa haka nake nufi Alhaji, amma ciwon batayi tsanani sosaiba, idan har ya riƙe magani da yardan Allah Zai iya warkewa ako da yaushe, kada ka tashi hankalinka Alhaji, Insha Allah komai zaizo da sauƙi!!"
Inji cewar Dr.Mohd wanda yake cike da buri da kuma fatan ƙarfafawa Alhaji Mansur ɗin guiwa.

Ajiyar zuciya Alhaji Mansur ya sauƙe tare da cewa. 

"Ni musulmi ne kuma nayarda da ƙaddaran da Allah Ya aikomin mai kyau ko marar kyau, kowani cuta aduniya tana da maganinta, cutar mutuwa ce kaɗai bata da magani, haƙiƙa komai da komai na Allah Ne, samun cuta da kuma sauƙi duk waƴannan ikonsa ne, kafun ka tsara naka shi yajima da tsara nashi, idan Allah Ya ƙadarta maka ƙaddara mummuna babu wani mahaluƙi daya isa sauya maka ita, haka idan ya nufeka da kyakkyawa babu wanda ya isa sauya maka ita,  babu wani abu aduniya da yafi ƙarfin ikon Allah da kuma Addu'a, zamuyita addu'a Insha Allah komai zai zamo tarihi watarana!!"  handkerchief ɗin dake cikin aljihunsa ya ciro tare da sanyawa yaɗan share ƙwallan da suka cika idanunsa.

Murmushi Dr.Mohd yayi tare da cewa "Haƙiƙa duk wani musulmin ƙwarai irinka akeso yakasance Alhaji Mansur, Allah yayi mana jagora"

Da "Ameen" kawai Alhj Mansur ya iya amsawa, sannan suka tashi suka fice daga cikin office É—in.

Direct ɗakin da su Ummu suke suka nufa. 

"Hajiya zaku iya ganinsa yanzu" faɗar Dr.Mohd. 

Dukansu suka ɗunguma sukabi bayan Dr.Mohd ciki kuwa harda Ziyada.   Wani waje suka nufa daganin wajen kasan na musammanne sannan kuma secret waje ne,   wani ɗan corridor suka shiga sannan suka samu kansu a gaban wani ɗaki.  Dr.Mohd ne ya tura ƙofar ɗakin ahankali, sannan suma suka rufa masa baya, Ziyada ce tayi na ƙarshen shiga.       Tana shiga ɗakin idanunta suka hasko mata shi, kwance yake akan wani gado mai ɗan faɗi, fuskarsa na kallon sama, sanye yake da dogon wando babuko riga ajikinsa, sai bandage ɗin da aka lilliƙa awajen da akayi masa aikin cire bullet.   Wata ƴar wayane aka sanya masa atacikin hancinsa,   sosai ya ƙara haske, gashin kansa kuwa sun kwanta luf,    sam batasan lokacin da hawaye suka gangaro daga cikin idanunta ba, jitayi ƙafafunta gaba ɗaya bazasu iya ɗaukarta ba. Hakan yasa ta jingina bayanta da wani dogon ƙarfe dake kusa da ita.  Ummu kuwa sai aikin share hawaye kawai take da handkerchief ɗinta, shi kansa Alh.Mansur baƙaramin dauriya yayi ba da baiyi kuka ba, musamman ma da yanzu yasan cewa ciwukan ɗan nasa sun zame masa biyu.   Mas'oud ma saida ya share ƙwallan tausayin abokinsa, domin kuwa duk wanda yaga Sooraj ahaka sai ya tausaya masa.   Hannu Ummu takai ta shafi kansa, wasu sabbin hawayene suka sake fitowa daga cikin idanunta.  Bazata iya jurewa ba, hakanne yasanya ta juya da sauri ta fice daga cijin ɗakin,  koda ta fita waje tsayawa tayi ajikin wata rumfa tasaki kukan tausayin Sooraj, ganin Ummu tafita yasa Alh.Mansur binta saboda yasan aikin kuka zataje tai tayi, bayan kuma tana da Hawan jini,  sam bayason ciwonta ya tashi. 

Mas'oud ne ya kalli Ziyada dake ta zubar hawaye ta kafe Sooraj ɗin da kyawawan idanunta, duk abun da ke wakana ma sam ita batasan anayinsa ba, gaba ɗaya hankali da tunaninta suna ga Mr.Helper ɗinta,  har batasan sanda hawaye ke zuba daga cikin idanunta ba. 

"Ziyadah!" Mas'oud yaƙira sunanta murya asanyaye.   Sai alokacin ta dawo daga duniyar tunanin da take, bata iya amsa ƙirannasa  ba, saidai ɗago kai da tayi ta kalleshi.

"Ki share hawayenki  ba komai kuka ke magancewa ba, kiyi masa addu'a kawai, yafi buƙatar hakan agareki" Mas'oud yafaɗi haka yana mai cusa hannayensa acikin aljihun wandonsa.  

Kai kawai ta iya jinjina masa alaman "To" domin bazata iya cewa dashi komaiba ayanzu, gaba ɗaya jikinta ya mutu, zuciyarta tayi rauni, duk wani tunaninta ya tsaya cak. 

Dr.Mohd ne yace sutafi hakanan saboda ba aso hayaniya tayi yawa a inda yake.

Alh. Mansur ne ya kalli Mas'oud tare da cewa. "Mas'oud kakaisu gida, nikuma zan zauna anan"

"Banajin zan iya komawa gida Alhaji, nikam nafiso na zauna anan" Ummu tafaÉ—i haka cikin muryarta da ta soma dashewa saboda kuka.

"Zaman asibiti banaki bane Sulaimiyya kuje kawai gobe da safe sai kuzo!" Alh.Mansur ya faɗi haka  aƙagauce saboda sam bayason musu.

"Abba me zai hana kabiyomu na sauƙeku idan yaso ni sai nadawo na kwana anan ɗin"

"A'a Mas'oud baza ayi haka ba, nine nan zan kwana, kuje kawai saida safe idan Allah Ya kaimu, sannan kuma banyarda kabarsu su kaɗai agidaba, ka kwana agidan kaima" Alhaji Mansur yana gama faɗan haka ya juya ya koma cikin asibitin.   Babu yanda Ummu ta iya haka ta shiga cikin motar Mas'oud ya ɗauki hanyar Maitaima dasu inda anan gidan Abba dake Abuja yake.    Wani irin tamfatsetsen gida Ziyada taga sunshiga, gaba ɗaya ginin gidan, gidan sama ne, gida ne mai kyau da girma, komai na gidan gwanin ban sha'awa ne, ko ina dake cikin gidan awadace yake da hasken ƙwan wuta,   Mas'oud ne yasanya key ajikin ƙofar ya murza. take babban ƙofar falon ta buɗu.  haka suka kutsa kai cikin babban falon dake cike da kayan more rayuwa, kayan ƙyale ƙyale dana ado.   Komai na cikin falon tsab tsab yake, Mas'oud ne ya buɗe gaba ɗaya bedrooms ɗin dake cikin falon, acan sama bedroom ɗin Ummu yake hakan yasa ya wuce sama direct ya buɗe mata nata ɗakin.     Ɗakin dake kusa dana Ummu yace da Ziyada ta shiga, gobe zai kawo mata kaɗan daga cikin kayanta.   Saida ya tabbatar da cewa dukansu sunshiga ɗakunansu, kafun ya dawo ƙasa shima ya shiga wani ɗaki.

Aƴan kwanakinnan tasaba duk dare saitayi wanka kafun ta kwanta saboda yanayin zafi da ake ciki, amma yau hakanan tasamu kanta da rashin duk wani kuzarinta, damuwar dake kwance aranta ma bazata bari tayi wani baccin kirkiba balle har aje ga yin wanka.   Hijabin jikinta ta cire tare da ɗalewa kan gadon ta kwanta jigum, yayinda ta sanya hannayenta ta tallafe ƙuncinta.   Tunanin Mr. Helper ne ya tsaya acikin rai da zuciyarta, ganinsa da tayi acikin ciwo yau yasanya hankalinta gaba ɗaya ya tashi, wani abu takeji agame dashi, wanda takasa tantance menene amma ta ta allaƙa abun da sunan TAUSAYI,  juyin duniya tayi amma bacci yaƙi ɗaukarta, haka tayita saƙe saƙe har kusan asuba sannan tatashi ta ɗauro alwala.

Kamar yanda bacci ya guji Ziyada haka ya gujewa Ummu, haka Ummu ta kusan kwana tana sallah, sauƙi kawai take nemawa ɗanta awajen ALLAH, kuka kam tayishi, domin tun tanayinshi da iyaka ƙarfinta, har hawayen suka daina fita.  

7:30 daidai taji anayi mata knocking ƙofar ɗakin da take ciki, dama tana zaunene akusa da ƙofar hakan yasa ta miƙe taƙarasa jikin ƙofar. Koda ta buɗe Mas'oud tagani tsaye.   kafun yace wani abu tayi saurin cewa "Ina Kwana"

"Lafiya lau" ya amsa yana me miƙo mata wata leda dake hanunsa.

"Kayankine kishirya, saiki fito kiyi breakfast, anjima zamu koma asibiti"

Amsar kayan tayi tare dayi masa godiya, ta koma cikin É—aki, shima juyawa yayi ya koma wajen Ummu dake zaune afalo, tun É—azu ba abun da yake sai aikin rarrashi.

Wanka tayi sannan ta ɗauki doguwar rigan material blue wanda yakawo mata tasanya, ɗinkin rigan irin rapper gown ɗinnan ne, sannan tana da ɗan guntun hanu, kallon kanta tayi acikin madubi, tare da kallon rigan azahiri,  mamakin inda yasamo rigan take, domin kuwa tasan baya ɗaya daga cikin kayanta nacan gidan, gaba ɗaya ma kayan daya kawo mata sabbi ne, kuma duk daga ɗinkin materials sai wasu atamfa guda biyu wanda aka musu ɗinkin riga da sket.  Jihabin data gani haɗe da rigan material ɗin ta ɗauka tasanya ajikinta, kasancewar white skin gareta saigashi kayan sunyi mata kyau sosai.   Afalo ta iskesu duka suna zaune, cike da ladabi ta rusuna ta gaishe da Ummu,  amsa mata gaisuwan nata Ummu tayi tanaɗan dubanta.

Akan sofa ta zauna tare da tanƙwashe ƙafafunta, Mas'oud ne ya turo mata plate ɗin soyayyen chips gabanta tare da kofin tea.

Bata wani iyacin abincin sosaiba, tea ɗinnema ta ɗansha da yawa.   Mas'oud ma sama sama yaci abincin, Ummu kam adole takecin abincin, hakan ma saboda umarnin da Alh.Mansur ya bata ne, da yace "Idan tasan bataci abinci ba karta sake tazo asibitin, idan bahaka ba kuwa zata gamu da fushinsa." banda haka babu abun dazai sanya tasanya wani abu na abinci acikinta.

Yauma dai aɗakin jiya suka zauna, gaba ɗaya zuciyoyinsu babu daɗi. Sai ƙarfe uku sannan Dr.Mohd yayi musu jagora zuwa ɗakin da Sooraj ɗin yake.
Chapter 28 · 0% Book details