Sashe 67
So Da Buri Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cikin kuka tace
“Lalata mini rayuwa da farin cikin da kayi bai isheka ba sai da ka had’a da Huda ko?
A haka sai faman ik’irari da pretending d’in kana k’aunarta kake yi!..
Abba in dai har kana son ta mai yasa ka jefa ta a irin wannan relationship d’in???
Da ka san mahaukaciyar matar yayanka ba zata so auren Arshaad da Hudan ba mai yasa tun farko kuka had’a?
Saboda ku maidamu abun kwatance ko me??
An tara mutane
k’iiri k’iri Ango yak’i zuwa! A Ina aka tab’a yin haka?
To bara kaji in gaya maka
Tunda har Mahaifiyar Arshaad da kanta ta furta cewar bata son y’ata a matsayin suruka
To
Wallahi ko ta dawo tace tana so, Ina so ka san cewa
‘maganar aure babu ita!!’
Sak’o ne wannan na baka, ka gaya mata ka gayawa Arshaad da wakilin shi!
Dan ba zan tab’a yarda in kai Huda gidan da ba’a k’aunarta ba wallahi.
Saboda na san zafin k’iyayyar surukai”
Ta fad’i haka tana fashewa da wani matsanancin kuka.
Da sauri Abba wanda yakejin zuciyarshi tana wani mahaukacin racing yace
“Maryam listen to me dan Allah ki bar wannan kukan”
Cikin tsananin b’acin rai tace “Abba kuka yanzu na fara!
Na san zan yi kuka especially idan Allah ya kaimu gobe aka yi calling off auren y’ata na ganta a cikin tashin hankali dole zan yi kuka.....”
Kasa cigaba ta yi da maganar dan haka ta yi jifa da wayar akan gadon ta durk’ushe a k’asa tana kuka.
Sakina na shirin yin magana Ummu da Mommy suka shigo.
Ajiyar zuciya Mommy ta sauk’e tanaji itama kamar ta fashe da kukan, a hankali ta d’an matso Maman sannan tace
“Wannan dalilin fa shiyasa nak’i gaya miki tun farko,
kin yi min alk’awarin ba zaki d’aga hankalinki ba yanzu menene haka?
Ki kwantar da hankalinki ni na san Mammy bata isa ta hana komai ba!
Dad ba zai barta ba.”
Cikin katseta Mama tace “Wallahi ko Dad ya barta ko bai barta ba babu maganar aure tsakanin Huda da Arshaad
Idan ita ta hak’ura to gobe ni zan hana!
Ta yaya kuke tunanin zan bar y’ata ta rayu da surukar da bata sonta?
Mommy na san mecece k’iyayyar surukai!
Kullum addua ta Allah ya had’a Huda da surukan da zasu k’aunaceta.
Taya za ki yi tunanin yanzu zan amince ta auri Arshaad??”
Cikin katseta Mommy tace
“Kar kiyi haka dan Allah,
kawai mu zuba ido amman kar kice zaki shiga tsakanin kaddara!
Idan kika yi hakan ai kun zama d’aya ke da Mammy kenan.”
Cikin katseta tace
“In zuba ido y’ata ta tafi inda ba a k’aunarta kome kike nufi?
In zuba ido rayuwar Huda ta lalace kamar yadda tawa ta lalace?”
Cikin rashin jin dad’i Mommy tace
“Haba Maryam,
rayuwarki bata lalace ba,
da ni da ke fa kusan mataki d’aya muka taka a rayuwar aure. Tabbas mun jigatu kuma mun sha wahala
amman a ko da yaushe idan na kalli Aslam wallahi ji nake gaba d’aya wahalar it’s worth it!
Dan Allah yayi mana kyauta.
Kuma dama a rayuwa dole akwai jarabta da kuma gwajin imani.
Ni dai shawarar da zan Baki itace
Dan Allah kar kiyi interfering
ki zuba ido ki barwa mazan komai, su sun san me za suyi.”
Cikin sharar kwallah Ummu tace
“hakane tabbas!
Mama dan Allah ki gwada yin hak’urin da kika saba
wata rana sai labari.”
Da sauri Baaba Talatu wadda bama su san ta biyo su ba
ta k’araso tace
“Taya zaku ce mata haka?
In dai uwar Yaro tace batayi to muma ba zamu kai jikarmu mai tsada inda ba’a k’aunarta ba wallahi!
Allah na tuba maza da yawa a gari..
Ga mai sunan kakan ta nan, d’an wajen Jamilu, idan Arshaad d’in zai kawo matsala ana iya d’aura musu aure gobe in sha Allah.
Na san ba zai tab’a cewa a’a ba, saboda daman ni na d’an so in fahimci take takenshi tun ba yau ba.”
Gyaran murya Shuwa wadda ta shigo yanzu tayi, dan haka duk suka juya suna kallonta.
A hankali ta k’araso cikin tafiyar ta wadda ke nuna tsufan da ya rufar mata.
Sai da tazo gaban Maryam
tukunna ta kama hannuwanta duka biyu ta fara magana
“Dan Allah dan annabi kar ki yi komai kar ki yi kuka kar ki d’agawa y’ar ki hankali.
Ki bar komai a hannun Ubangiji, tun kafin ki haifi Huda already an riga an gama rubuta k’addararta da komai nata.
Kar ki yi interfering wai dan kina tunanin zaki iya kub’utar da ita!
ki zuba ido ki yi mata addua
komai zai tafi bisa yanda Ubangiji ya riga ya tsara.
Bamu isa mu saka ko mu hana komai ba. Kin ji y’ar albarka?”
Ta k’arashe maganar tana mai sa hannu ta share mata hawayenta duka biyu.
Kuka Mama ta sake fashewa da shi ta fad’a jikin Shuwa suka rungume juna. Ita kanta Shuwan k’arfin hali ne kawai da dauriya suka hanata kukan
Ta rasa gane wachche iriyar k’addara ce
A rayuwar Maryam da Huda,
Astaghfirullah.....
Shigowar ta tare da matan da suka ruk’o ta ne ya sanya d’akin yin shiru. Har yanzu
fuskarta a rufe take amman kana gani ka san kuka take yi.
Sakina na ganinta taji kuka na shirin kufce mata dan haka da sauri ta fita a d’akin.
Suna zaunar da ita a bakin gado Mama ma ta
saki Shuwa ta fice.
Shuwan ce tayi k’arfin halin cewa
“Mommy da Ummu da kuma mata biyun da suka shigo da ita “Su je akwai motoci
a fara kwasar kayan Amarya ana kaiwa gidanta, dan ba zata yarda da ajjiye wannan dukiyar a gidanta ba, tunda kowa ya gani kawai su kai mata abunta gidanta.”
Murmushi Mommy tayi kafin tace
“Ni kam gida zan wuce..
Ina a matsayin uwar Ango ina ni ina ziryar gidansu
Ai nayi jere sai kuma in ta haihu nan da wata tara in sha Allah ni da in koma.”
Da sauri cikin raha ragowar matan suka ce
“In shaa Allah”
Ba a wani dad’e ba suka fito dukkansu a tare
Mommy ta d’anso ta sake ganin Mama amman kuma kawai sai ta rabu da ita, a cewarta ‘in ta d’an sauk’o zuwa anjima zata kira ta a waya’…..
A tare suka fito da Ummu,
su suka fara yin gaba da akwatuna ita kuma ta shiga mota ta nufi MT estate dan already drivern ya zo tun d’azu.
NASARAWA g r a.
Daddy da Dad na zaune sai zazzagawa Abba fad’a suke yi akan ‘ya mayar da Ummi tun kafin zance ya isa kunnen Granpa’ shi kuma ya tubure ya k’i!.
Suna a haka wayar Mama ta shigo…
Tsaf! Duk sun ji abubuwan da ta fad’a, dan wayar a high volume take kuma suna kurkusa da juna.
Yana gama wayar Dad yace
“Abba ka mayar da Ummi yanzunnan in dai na isa da kai.”
Haka shima Daddy
same thing ya fad’a mishi.
Ba yadda ya iya haka ya maida ita yana ji kamar yayi ta kurma uban ihu!.
Daganan Dad ya mik’e!
Kamar Daddy ya san meye a ranshi yayi saurin mik’ewa shima ya tsaya a gabanshi sannan yace
“Dan Allah kar ka yi haka.
Ka tsaya zan yiwa Adama magana, na san kafin zuwa gobe in sha Allah zata nutsu.”
Cikin fad’a fad’a Dad yace
“Ba zata nutsu ba!
Sam ba zata nutsu ba.
Da ace zata nutsu da tun tuni ta nutsu, ku bar ni kawai!!”
Ya fad’i haka yana k’ok’arin zagaye Daddy ya wuce.
Da sauri Daddy ya kuma tareshi sannan yace
“Ya abunda muka gama gyarawa yanzu! Da girman ka kake k’ok’arin aikatawa?”
Cikin tsananin b’acin rai Dad yace
“This is a different case..”
Cikin katseshi Daddy yace
“Ba wani different case anan duk abu d’aya ne!
Idan kayi mata haka ma ai ka ji haushi kenan, wato ta ci
riba ma kenan tunda har kaji haushi ka hukuntata, ai idan mata suna haukarsu ba a biye musu.
Tabbas na san dole ana buk’atar albarkar ta
amman ka b’ullo mata ta bayan fage.
Wani abun fa dole sai ka sauk’o, ka san yadda za ayi a d’aura auren shine ka ci riba!
Amman yanzu idan ka biyeta
ka saketa aka zo ta sake birkicewa
Wa gari ya waya?
Abunda ya kamata kayi shine
ka san ta inda zaka b’ullo mata
ka bawa iska ajiyar ta
ka nuna kamar bama ka san me take yi ba! Ka d’aure ta da jijiyoyin jikinta
Tana ji tana gani a d’aura auren gobe kamar bata existing a duniyar!
This is the best punishment da tayi deserving, amma
yanzu idan kayi haka( ka saketa) ai jagula komai za kayi,
kuma itace zata yi nasara at the end of the day tunda
Uwa ce.
Ka ga dai
ga Granpa a gefe wanda a yanzu haka jira kawai yake yi a tab’a shi!
Kai da kanka kace yayi mana warning a kansu duk mu ukun
I assure you wallahi idan kayi wani abun ba zai duba laifintaba zai bi takanka......”
Sannu a hankali Daddy ya samu ya shawo kan Dad da kyar! Ya hak’ura.
Shi dai Abba yana nan zaune bai ce musu uffan ba!
Dan ba fahimtarsu yake yi ba
har yanzu ba abunda yake yi mishi yawo a kunne sai kukan Maryam da tashin hankalin da ya jita a ciki.
Tabbbas sai ya gasawa Ummi aya a hannunta!
Hakan ba halinshi bane ba kuma bai kamata yayi mata hakaba a matsayin ta na mahaifiyar su Sudais
amman ba yanda ya iya…Dole ta san waye Abba! Ba ita kad’ai ba har su Mammmy, kasancewar su yayu a gareshi ba zai hanashi ya ja musu fasali ba.
A hankali ya mik’e ya yiwa su yaya rakiya, daga nan shima ya fita ya bar gidan.
“Lalata mini rayuwa da farin cikin da kayi bai isheka ba sai da ka had’a da Huda ko?
A haka sai faman ik’irari da pretending d’in kana k’aunarta kake yi!..
Abba in dai har kana son ta mai yasa ka jefa ta a irin wannan relationship d’in???
Da ka san mahaukaciyar matar yayanka ba zata so auren Arshaad da Hudan ba mai yasa tun farko kuka had’a?
Saboda ku maidamu abun kwatance ko me??
An tara mutane
k’iiri k’iri Ango yak’i zuwa! A Ina aka tab’a yin haka?
To bara kaji in gaya maka
Tunda har Mahaifiyar Arshaad da kanta ta furta cewar bata son y’ata a matsayin suruka
To
Wallahi ko ta dawo tace tana so, Ina so ka san cewa
‘maganar aure babu ita!!’
Sak’o ne wannan na baka, ka gaya mata ka gayawa Arshaad da wakilin shi!
Dan ba zan tab’a yarda in kai Huda gidan da ba’a k’aunarta ba wallahi.
Saboda na san zafin k’iyayyar surukai”
Ta fad’i haka tana fashewa da wani matsanancin kuka.
Da sauri Abba wanda yakejin zuciyarshi tana wani mahaukacin racing yace
“Maryam listen to me dan Allah ki bar wannan kukan”
Cikin tsananin b’acin rai tace “Abba kuka yanzu na fara!
Na san zan yi kuka especially idan Allah ya kaimu gobe aka yi calling off auren y’ata na ganta a cikin tashin hankali dole zan yi kuka.....”
Kasa cigaba ta yi da maganar dan haka ta yi jifa da wayar akan gadon ta durk’ushe a k’asa tana kuka.
Sakina na shirin yin magana Ummu da Mommy suka shigo.
Ajiyar zuciya Mommy ta sauk’e tanaji itama kamar ta fashe da kukan, a hankali ta d’an matso Maman sannan tace
“Wannan dalilin fa shiyasa nak’i gaya miki tun farko,
kin yi min alk’awarin ba zaki d’aga hankalinki ba yanzu menene haka?
Ki kwantar da hankalinki ni na san Mammy bata isa ta hana komai ba!
Dad ba zai barta ba.”
Cikin katseta Mama tace “Wallahi ko Dad ya barta ko bai barta ba babu maganar aure tsakanin Huda da Arshaad
Idan ita ta hak’ura to gobe ni zan hana!
Ta yaya kuke tunanin zan bar y’ata ta rayu da surukar da bata sonta?
Mommy na san mecece k’iyayyar surukai!
Kullum addua ta Allah ya had’a Huda da surukan da zasu k’aunaceta.
Taya za ki yi tunanin yanzu zan amince ta auri Arshaad??”
Cikin katseta Mommy tace
“Kar kiyi haka dan Allah,
kawai mu zuba ido amman kar kice zaki shiga tsakanin kaddara!
Idan kika yi hakan ai kun zama d’aya ke da Mammy kenan.”
Cikin katseta tace
“In zuba ido y’ata ta tafi inda ba a k’aunarta kome kike nufi?
In zuba ido rayuwar Huda ta lalace kamar yadda tawa ta lalace?”
Cikin rashin jin dad’i Mommy tace
“Haba Maryam,
rayuwarki bata lalace ba,
da ni da ke fa kusan mataki d’aya muka taka a rayuwar aure. Tabbas mun jigatu kuma mun sha wahala
amman a ko da yaushe idan na kalli Aslam wallahi ji nake gaba d’aya wahalar it’s worth it!
Dan Allah yayi mana kyauta.
Kuma dama a rayuwa dole akwai jarabta da kuma gwajin imani.
Ni dai shawarar da zan Baki itace
Dan Allah kar kiyi interfering
ki zuba ido ki barwa mazan komai, su sun san me za suyi.”
Cikin sharar kwallah Ummu tace
“hakane tabbas!
Mama dan Allah ki gwada yin hak’urin da kika saba
wata rana sai labari.”
Da sauri Baaba Talatu wadda bama su san ta biyo su ba
ta k’araso tace
“Taya zaku ce mata haka?
In dai uwar Yaro tace batayi to muma ba zamu kai jikarmu mai tsada inda ba’a k’aunarta ba wallahi!
Allah na tuba maza da yawa a gari..
Ga mai sunan kakan ta nan, d’an wajen Jamilu, idan Arshaad d’in zai kawo matsala ana iya d’aura musu aure gobe in sha Allah.
Na san ba zai tab’a cewa a’a ba, saboda daman ni na d’an so in fahimci take takenshi tun ba yau ba.”
Gyaran murya Shuwa wadda ta shigo yanzu tayi, dan haka duk suka juya suna kallonta.
A hankali ta k’araso cikin tafiyar ta wadda ke nuna tsufan da ya rufar mata.
Sai da tazo gaban Maryam
tukunna ta kama hannuwanta duka biyu ta fara magana
“Dan Allah dan annabi kar ki yi komai kar ki yi kuka kar ki d’agawa y’ar ki hankali.
Ki bar komai a hannun Ubangiji, tun kafin ki haifi Huda already an riga an gama rubuta k’addararta da komai nata.
Kar ki yi interfering wai dan kina tunanin zaki iya kub’utar da ita!
ki zuba ido ki yi mata addua
komai zai tafi bisa yanda Ubangiji ya riga ya tsara.
Bamu isa mu saka ko mu hana komai ba. Kin ji y’ar albarka?”
Ta k’arashe maganar tana mai sa hannu ta share mata hawayenta duka biyu.
Kuka Mama ta sake fashewa da shi ta fad’a jikin Shuwa suka rungume juna. Ita kanta Shuwan k’arfin hali ne kawai da dauriya suka hanata kukan
Ta rasa gane wachche iriyar k’addara ce
A rayuwar Maryam da Huda,
Astaghfirullah.....
Shigowar ta tare da matan da suka ruk’o ta ne ya sanya d’akin yin shiru. Har yanzu
fuskarta a rufe take amman kana gani ka san kuka take yi.
Sakina na ganinta taji kuka na shirin kufce mata dan haka da sauri ta fita a d’akin.
Suna zaunar da ita a bakin gado Mama ma ta
saki Shuwa ta fice.
Shuwan ce tayi k’arfin halin cewa
“Mommy da Ummu da kuma mata biyun da suka shigo da ita “Su je akwai motoci
a fara kwasar kayan Amarya ana kaiwa gidanta, dan ba zata yarda da ajjiye wannan dukiyar a gidanta ba, tunda kowa ya gani kawai su kai mata abunta gidanta.”
Murmushi Mommy tayi kafin tace
“Ni kam gida zan wuce..
Ina a matsayin uwar Ango ina ni ina ziryar gidansu
Ai nayi jere sai kuma in ta haihu nan da wata tara in sha Allah ni da in koma.”
Da sauri cikin raha ragowar matan suka ce
“In shaa Allah”
Ba a wani dad’e ba suka fito dukkansu a tare
Mommy ta d’anso ta sake ganin Mama amman kuma kawai sai ta rabu da ita, a cewarta ‘in ta d’an sauk’o zuwa anjima zata kira ta a waya’…..
A tare suka fito da Ummu,
su suka fara yin gaba da akwatuna ita kuma ta shiga mota ta nufi MT estate dan already drivern ya zo tun d’azu.
NASARAWA g r a.
Daddy da Dad na zaune sai zazzagawa Abba fad’a suke yi akan ‘ya mayar da Ummi tun kafin zance ya isa kunnen Granpa’ shi kuma ya tubure ya k’i!.
Suna a haka wayar Mama ta shigo…
Tsaf! Duk sun ji abubuwan da ta fad’a, dan wayar a high volume take kuma suna kurkusa da juna.
Yana gama wayar Dad yace
“Abba ka mayar da Ummi yanzunnan in dai na isa da kai.”
Haka shima Daddy
same thing ya fad’a mishi.
Ba yadda ya iya haka ya maida ita yana ji kamar yayi ta kurma uban ihu!.
Daganan Dad ya mik’e!
Kamar Daddy ya san meye a ranshi yayi saurin mik’ewa shima ya tsaya a gabanshi sannan yace
“Dan Allah kar ka yi haka.
Ka tsaya zan yiwa Adama magana, na san kafin zuwa gobe in sha Allah zata nutsu.”
Cikin fad’a fad’a Dad yace
“Ba zata nutsu ba!
Sam ba zata nutsu ba.
Da ace zata nutsu da tun tuni ta nutsu, ku bar ni kawai!!”
Ya fad’i haka yana k’ok’arin zagaye Daddy ya wuce.
Da sauri Daddy ya kuma tareshi sannan yace
“Ya abunda muka gama gyarawa yanzu! Da girman ka kake k’ok’arin aikatawa?”
Cikin tsananin b’acin rai Dad yace
“This is a different case..”
Cikin katseshi Daddy yace
“Ba wani different case anan duk abu d’aya ne!
Idan kayi mata haka ma ai ka ji haushi kenan, wato ta ci
riba ma kenan tunda har kaji haushi ka hukuntata, ai idan mata suna haukarsu ba a biye musu.
Tabbas na san dole ana buk’atar albarkar ta
amman ka b’ullo mata ta bayan fage.
Wani abun fa dole sai ka sauk’o, ka san yadda za ayi a d’aura auren shine ka ci riba!
Amman yanzu idan ka biyeta
ka saketa aka zo ta sake birkicewa
Wa gari ya waya?
Abunda ya kamata kayi shine
ka san ta inda zaka b’ullo mata
ka bawa iska ajiyar ta
ka nuna kamar bama ka san me take yi ba! Ka d’aure ta da jijiyoyin jikinta
Tana ji tana gani a d’aura auren gobe kamar bata existing a duniyar!
This is the best punishment da tayi deserving, amma
yanzu idan kayi haka( ka saketa) ai jagula komai za kayi,
kuma itace zata yi nasara at the end of the day tunda
Uwa ce.
Ka ga dai
ga Granpa a gefe wanda a yanzu haka jira kawai yake yi a tab’a shi!
Kai da kanka kace yayi mana warning a kansu duk mu ukun
I assure you wallahi idan kayi wani abun ba zai duba laifintaba zai bi takanka......”
Sannu a hankali Daddy ya samu ya shawo kan Dad da kyar! Ya hak’ura.
Shi dai Abba yana nan zaune bai ce musu uffan ba!
Dan ba fahimtarsu yake yi ba
har yanzu ba abunda yake yi mishi yawo a kunne sai kukan Maryam da tashin hankalin da ya jita a ciki.
Tabbbas sai ya gasawa Ummi aya a hannunta!
Hakan ba halinshi bane ba kuma bai kamata yayi mata hakaba a matsayin ta na mahaifiyar su Sudais
amman ba yanda ya iya…Dole ta san waye Abba! Ba ita kad’ai ba har su Mammmy, kasancewar su yayu a gareshi ba zai hanashi ya ja musu fasali ba.
A hankali ya mik’e ya yiwa su yaya rakiya, daga nan shima ya fita ya bar gidan.