Sashe 63
So Da Buri Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ummu bata ga k’arasowar Sakina ba sai tayi tana cewa
“Eh tabbas kam Hajiya Umma kya zauna ai kiyi ta jira tunda daman kallon kwaf da munafurci ne ya kawo ki!
Mu nan dukkannin mu munada aikin yi kuma ba mu da lokacin zaman jira har k’arfe taran dare!
In dai Ango kike son gani to ki bada nan da awa biyu zaki ganshi sun iso tare shi da iyayenshi maza da za su kawo lefe wanda na tabbatar abunda ya tsaidasu kenan
ba wai abunda makirar zuciyarki ta shirya miki ba!”
Umma na shirin k’arasowa inda Sakinar take taga Ummu ta d’auke ta da mari!
Cikin yaren Shuwa Ummu ta hau yiwa Sakinar fad’a k’asa k’asa yanda ta tabbar ba kowa ne zai ji su, tace
“Baki da hankali ashe?
A cikin dangi da y’an uwa za ki bud’e baki kina yiwa babbar mata rashin kunya haka?
So kike a tafi dake a baki?
Wuce!
Wuce ki tafi chaan sama d’akin Shuwa ki rufe!
Idan ba ni na neme ki ba wallahi kika fito sai ranki yayi mugun b’aci!”.
Juyawa kawai Sakina tayi ta wuce tana ji kamar ta had’iye zuciyarta!
A kan Umma aka mareta a gaban mutane haka!?
Kuma ta tabbatar tunda Umma ta fara wannan maganganun to fa idan taka mata burki aka yi ba ko kuma Arshaad d’in ta gani ba tabbas ba zata
tab’a barin mutane su sha ruwa ba.
Ita daman tun d’azu da ta ganta tazo da sassafe ta san ba alkhairi ne ya kawota ba.
Ita da take da abun fad’a a gindi amma shine har take da audacity d’in yin magana!
Wallahi yau da Ummu ta barta da sai ta yiwa Umma zazzagar kwanyo....
Da wannan tunanin ta k’arasa d’akin Shuwa, sai a lokacin hawayen bak’in ciki suka samu nasarar zubo mata…
Daga Shuwa sai Baabaa Talatu ne a d’akin suna
shirya tukuicin da za a bayar in an kawo lefe.
Baaba Talatu tana ganin ta shigo tana kuka ta mik’e tana
“Subahanallah, mai ya
faru?
Ke da waye?”
Da sauri ta k’arasa ta hau shafa fuskarta inda hannun Ummu ya fito tarr!! Ya kwanta akan farar fuskarta
Cikin fad’a Baaba Talatun tace
“Wanne d’an iskan ne ya mare ki??”
Fashewa tayi da kuka
cikin kukan tace
“Umma ce take ta abubuwa a waje, shine Ummu ta mareni
wai dan....”
Ai bata tsaya jin k’arshen ba,
tayi waje.
Shuwa ce ta iya daurewa ta tsaya ta ji labarin Sakinar
tukunna ta mik’e itama tace mata “ta zauna a d’akin, kar taje ko ina .
Bari taje taji ba’asin abunda yasa Angon bai k’araso ba...........”
BULAMA ✍️
So da Buri
Free Book
53
Shuwa ce ta iya daurewa ta tsaya ta ji labarin Sakinar,
tukunna ta mik’e itama tace mata “ta zauna a d’akin, kar taje ko ina.
Bari taje taji ba’asin abunda yasa Angon bai k’araso ba.”
“To”
Kawai Sakina tace,
tana mai sake goge fuskarta
sannan ta koma gefe ta fara warware laffayar jikinta da d’aurin d’ankwalin dake kanta..
Sai da ya rage daga ita sai long camisole d’inta wadda ta saka a ciki mai dogon hannu yayinda dogon gashinta ya kwanta a gadon bayanta sannan ta fara k’ok’arin kiran Arshaad...
Tayi mishi misscalls sun fi ashirin amman shiru. Dan haka
nan da nan hankalinta ya sake tashi…. Tun jiya take danne zuciyarta take k’ok’arin kawar da maganar da Aaima ta gaya mata a cikin kwakwalwarta
amman kuma attitude d’in Arshaad da k’in zuwanshi a yanzu ya yi matuk’ar bata tsoro.
Ba wadda take jin fargabar taji wannan batu irin Hudan
shiyasa jiya ta kwana Sallah akan Allah yasa maganar Aaima ta zama k’arya
idan kuma gaskiyace Allah yasa su Abba su gyara lamarin cikin sauk’i…
Gaba d’aya hankalinta a tashe yake dauriya ce kawai take yi, tana kuma k’ok’arin taga ba wanda ta bari ya ma ji zancen har a samu a gyara lamarin in sha Allah.
Ganin arshaad d’in bashi da niyyar amsa ta ne
yasa kawai ta kira Auwal
dan taji me ke faruwa
a ina aka tsaya..
Shi sai a bakinta ma yake jin wai ‘Arshaad d’in bai je ba’
Saboda shi suna asibiti.
Ganin kamar bai san me yake faruwa ba ya sanya taja bakinta tayi shiru
saboda ance yawan yayata magana kan iya tabbatar da gasgatuwar ta. Dan haka kawai sai tace mishi
“ya duba musu Arshaad din pls”
Daga haka suka yi sallama.
Daman shima yana da shirinshi zai je wajen
So yanzu zai duba Arshaad d’in sai su wuce tare kawai
dan haka ya cewa Dad
“Bara yaje gida,
Sakina ta kirashi wai har yanzu Arshaad be k’arasa ba.”
“to” kawai Dad d’in yace masa.
Yana fita shima Dad din ya d’au waya ya kira Gwaggo Asabe yace
“Dan Allah tazo ta ji da Ummi.
Zai yiwa drivern da zai kawota kwatancen asibitin da suke....”
Drivern da ya kawota (Gwaggwo Asabe) shi ya maidashi mansion d’in.
Yana zuwa ya tarar da Daddy
ya shirya chap yana jiranshi
da akwatuna dozen biyu sun sha decoration
sai kuma basket na gift guda biyar, da akwatunan uwa uba gwaggwo da kawu..
Duk sun had’a. Tun sassafe Mommy ta aiko da kayan
shi kuma ya duba ya tabbatar komai dai dai.
Sai da aka gama loda kayayyakin a motoci wajen goma tukunna Abba ya fito da shirin shi shima da alama rakasu zai yi!
Dad, yana shirin shiga mota har driver ya bud’e mishi k’ofar motar ya hango tahowar Abba!
Wani takaici ne ya d’ebesa
bai san lokacin da ya daka masa tsawa ba! Yace
“Idan ka k’araso nan wallahi sai mun kwashi y’an kallo ni da kai!
Kaji dai na rantse
wallahi!!”
Ya k’arashe maganar yana mishi nuni da yatsar shi manuniya yana nuna sama.
Ajiyar zuciya Abban ya sauk’e kafin yace
“Dad nimafa rakaku zan y....”
Cikin fushi Dad d’in yace
“Kaga mota nan, zo ka shiga!
Amman direct
Asibitin da aka kwantar da Ummi zaka je
Idan kuma ba haka ba to ka koma ka zauna a ciki.
Zab’i d’aya!”
idanuwa direbobin da masu aikin suka tsura musu..Ganin da Abba yayi har sun fara kwasar y’an kallon kamar yadda Dad d’in ya ambata ne yasa kawai ya juya ya koma ciki ranshi a mugun b’ace!.
Tsaki Dad yayi ya shige motar
yana mai cewa
“Ba za ku haukata ni ba,
wallahi!”.
Shi dai Daddy
shiga yayi ya zauna a kusa da shi, yana son tambayarshi
wata zuciyar kuma sai ta bashi shawarar ya bari ya Dad d’in ya d’an sauk’o tukunna sai suyi magana…
A haka drivern ya ja su suka nufi Gandun Albasa
Daddy yana mamakin meye haka yake damun Dad??
Dan tabbas ya san akwai abunda aka yi mishi......
GANDUN ALBASA.
Baaba Talatu tana fita harabar gidan ta tarar gurin har ya fara kachamewa!
Dan bayan Sakina ta bar wajen Umma da Anty Zainab kan Ummu suka dawo
wai “ai itace bata yi mata tarbiyya mai kyau ba shiyasa ta raina manya har haka...”
Ga kuma wannan tsohuwa ita ma ta kafa ta tsare tace
“Sai Ango ya fito tukunna za a fara gabatar da komai!”
Yayinda Ummu da wasu cousins d’inta suke ta k’ok’arin ganin sun yayyafa wa lamarin ruwa amman abun ya faskara!.
Baaba Talatu ce ta k’arasa ta ja wannan tsohuwar gefe suka had’u ita da Shuwa suna mata magana k’asa k’asa…
Ganin kamar ana shirin fara traditional event d’in
cikin kwanciyar hankali ne yasanya Umma ta sake cewa
“Nima fa kamar uwa nake a wajen Hudan!
Dan haka ba zan bari kowa ya tab’a ta ba har sai Angon nata ya k’araso..
idam kuma fasawa yayi ne to kawai a fito a fad’a wa mutane sai a fasa sakata a lallen,
dan ba girman mu bane mu tsaya muna yiwa mutane wasa da hankali!
Ko ya kuka gani?”
Ta k’arashe maganar tana kallon cousins d’in Ummu waenda suke gefen ta! Ba su kad’ai ba kusan kaff wajen babu wanda bai ji abinda tace ba hatta su Shuwa.
“Ga Angon nan”
Muryar Mommy wadda suka fito su uku yanzu ta daki dodon kunnuwansu!
Da sauri Mama da Aslam suka kalleta!
Ba tare da ta kallesu ba ta
kama hannun Aslam ta fara janshi
Mama na binsu a baya kamar rak’umi da akala shi kuma yana binta!..
Bata cikashi ba sai da ta kaishi gefen Hudan sannan ta zaunar da shi.
Da sauri Ummu ta matso k’asa k’asa tace
“Mommy a Al’ada fa dole sai Angon zai....
Cikin katseta Mommy tace
“A addini fa?”
Bata jira Ummu ta bata amsa ba ta sake ce mata
“Kalla nan kinga”
Tayi maganar tana
nuna mata Huda wadda sai a lokacin Ummu ta lura da yanda mayafinta ya jik’e sharkaf!
Wanda kana gani ka san ruwan hawaye ne…
Mommy bata jira jin me zata ce ba ta ci gaba da yi mata magana k’asa k’asa irin na masu hankali,
tace
“Saboda ita kawai ki bari ayi a gama!
Na tabbatar ba wai rashin zuwan Arshaad kad’ai bane ya saka ta kuka ba! Har da maganganun matar nan! Tun muna parlourn bayankun nan muke juyo komai.
Dan Allah kar kice a’a!
Kalla kiga mutane kowa ya zuba ido an fara k’ananun maganganu, na tabbatar in dai ba Angon suka gani ba to haka za a tashi ana gulmace gulmace shima kuma sai idan an samu waenchan matan sun bari anyi d’in kenan.
Na tabbatar mutane k’alilan ne kuma na jikinku sosai suka san ba Arshaad bane wannan, ba kowa ne zai gane ba
so dan Allah ki kwantar da hankalinki ayi abun nan a gama without any more dramas.
Saka lalle ai ba d’aurin aure bane ba, ba komai kawai bidi’a ce so mu bisu kawai ayi a gama.”
Tana gama fad’an haka ta juya ga jamaar wajen tace
“Kuyi hak’uri mun yi latti wani d’an uzuri ne ya tsaida mu!
Sunana Hajiya Aisha
Maman Ango, mun gode kwarai da zuwanku dan taya mu farin ciki.”
Daga nan ta juya ta cewa
Ummu
“Ni zan fara ko ke?”
Da murmushi kwance akan fuskarta.
Kallonta kawai suke yi
daga Ummu har Mama.....……
“Eh tabbas kam Hajiya Umma kya zauna ai kiyi ta jira tunda daman kallon kwaf da munafurci ne ya kawo ki!
Mu nan dukkannin mu munada aikin yi kuma ba mu da lokacin zaman jira har k’arfe taran dare!
In dai Ango kike son gani to ki bada nan da awa biyu zaki ganshi sun iso tare shi da iyayenshi maza da za su kawo lefe wanda na tabbatar abunda ya tsaidasu kenan
ba wai abunda makirar zuciyarki ta shirya miki ba!”
Umma na shirin k’arasowa inda Sakinar take taga Ummu ta d’auke ta da mari!
Cikin yaren Shuwa Ummu ta hau yiwa Sakinar fad’a k’asa k’asa yanda ta tabbar ba kowa ne zai ji su, tace
“Baki da hankali ashe?
A cikin dangi da y’an uwa za ki bud’e baki kina yiwa babbar mata rashin kunya haka?
So kike a tafi dake a baki?
Wuce!
Wuce ki tafi chaan sama d’akin Shuwa ki rufe!
Idan ba ni na neme ki ba wallahi kika fito sai ranki yayi mugun b’aci!”.
Juyawa kawai Sakina tayi ta wuce tana ji kamar ta had’iye zuciyarta!
A kan Umma aka mareta a gaban mutane haka!?
Kuma ta tabbatar tunda Umma ta fara wannan maganganun to fa idan taka mata burki aka yi ba ko kuma Arshaad d’in ta gani ba tabbas ba zata
tab’a barin mutane su sha ruwa ba.
Ita daman tun d’azu da ta ganta tazo da sassafe ta san ba alkhairi ne ya kawota ba.
Ita da take da abun fad’a a gindi amma shine har take da audacity d’in yin magana!
Wallahi yau da Ummu ta barta da sai ta yiwa Umma zazzagar kwanyo....
Da wannan tunanin ta k’arasa d’akin Shuwa, sai a lokacin hawayen bak’in ciki suka samu nasarar zubo mata…
Daga Shuwa sai Baabaa Talatu ne a d’akin suna
shirya tukuicin da za a bayar in an kawo lefe.
Baaba Talatu tana ganin ta shigo tana kuka ta mik’e tana
“Subahanallah, mai ya
faru?
Ke da waye?”
Da sauri ta k’arasa ta hau shafa fuskarta inda hannun Ummu ya fito tarr!! Ya kwanta akan farar fuskarta
Cikin fad’a Baaba Talatun tace
“Wanne d’an iskan ne ya mare ki??”
Fashewa tayi da kuka
cikin kukan tace
“Umma ce take ta abubuwa a waje, shine Ummu ta mareni
wai dan....”
Ai bata tsaya jin k’arshen ba,
tayi waje.
Shuwa ce ta iya daurewa ta tsaya ta ji labarin Sakinar
tukunna ta mik’e itama tace mata “ta zauna a d’akin, kar taje ko ina .
Bari taje taji ba’asin abunda yasa Angon bai k’araso ba...........”
BULAMA ✍️
So da Buri
Free Book
53
Shuwa ce ta iya daurewa ta tsaya ta ji labarin Sakinar,
tukunna ta mik’e itama tace mata “ta zauna a d’akin, kar taje ko ina.
Bari taje taji ba’asin abunda yasa Angon bai k’araso ba.”
“To”
Kawai Sakina tace,
tana mai sake goge fuskarta
sannan ta koma gefe ta fara warware laffayar jikinta da d’aurin d’ankwalin dake kanta..
Sai da ya rage daga ita sai long camisole d’inta wadda ta saka a ciki mai dogon hannu yayinda dogon gashinta ya kwanta a gadon bayanta sannan ta fara k’ok’arin kiran Arshaad...
Tayi mishi misscalls sun fi ashirin amman shiru. Dan haka
nan da nan hankalinta ya sake tashi…. Tun jiya take danne zuciyarta take k’ok’arin kawar da maganar da Aaima ta gaya mata a cikin kwakwalwarta
amman kuma attitude d’in Arshaad da k’in zuwanshi a yanzu ya yi matuk’ar bata tsoro.
Ba wadda take jin fargabar taji wannan batu irin Hudan
shiyasa jiya ta kwana Sallah akan Allah yasa maganar Aaima ta zama k’arya
idan kuma gaskiyace Allah yasa su Abba su gyara lamarin cikin sauk’i…
Gaba d’aya hankalinta a tashe yake dauriya ce kawai take yi, tana kuma k’ok’arin taga ba wanda ta bari ya ma ji zancen har a samu a gyara lamarin in sha Allah.
Ganin arshaad d’in bashi da niyyar amsa ta ne
yasa kawai ta kira Auwal
dan taji me ke faruwa
a ina aka tsaya..
Shi sai a bakinta ma yake jin wai ‘Arshaad d’in bai je ba’
Saboda shi suna asibiti.
Ganin kamar bai san me yake faruwa ba ya sanya taja bakinta tayi shiru
saboda ance yawan yayata magana kan iya tabbatar da gasgatuwar ta. Dan haka kawai sai tace mishi
“ya duba musu Arshaad din pls”
Daga haka suka yi sallama.
Daman shima yana da shirinshi zai je wajen
So yanzu zai duba Arshaad d’in sai su wuce tare kawai
dan haka ya cewa Dad
“Bara yaje gida,
Sakina ta kirashi wai har yanzu Arshaad be k’arasa ba.”
“to” kawai Dad d’in yace masa.
Yana fita shima Dad din ya d’au waya ya kira Gwaggo Asabe yace
“Dan Allah tazo ta ji da Ummi.
Zai yiwa drivern da zai kawota kwatancen asibitin da suke....”
Drivern da ya kawota (Gwaggwo Asabe) shi ya maidashi mansion d’in.
Yana zuwa ya tarar da Daddy
ya shirya chap yana jiranshi
da akwatuna dozen biyu sun sha decoration
sai kuma basket na gift guda biyar, da akwatunan uwa uba gwaggwo da kawu..
Duk sun had’a. Tun sassafe Mommy ta aiko da kayan
shi kuma ya duba ya tabbatar komai dai dai.
Sai da aka gama loda kayayyakin a motoci wajen goma tukunna Abba ya fito da shirin shi shima da alama rakasu zai yi!
Dad, yana shirin shiga mota har driver ya bud’e mishi k’ofar motar ya hango tahowar Abba!
Wani takaici ne ya d’ebesa
bai san lokacin da ya daka masa tsawa ba! Yace
“Idan ka k’araso nan wallahi sai mun kwashi y’an kallo ni da kai!
Kaji dai na rantse
wallahi!!”
Ya k’arashe maganar yana mishi nuni da yatsar shi manuniya yana nuna sama.
Ajiyar zuciya Abban ya sauk’e kafin yace
“Dad nimafa rakaku zan y....”
Cikin fushi Dad d’in yace
“Kaga mota nan, zo ka shiga!
Amman direct
Asibitin da aka kwantar da Ummi zaka je
Idan kuma ba haka ba to ka koma ka zauna a ciki.
Zab’i d’aya!”
idanuwa direbobin da masu aikin suka tsura musu..Ganin da Abba yayi har sun fara kwasar y’an kallon kamar yadda Dad d’in ya ambata ne yasa kawai ya juya ya koma ciki ranshi a mugun b’ace!.
Tsaki Dad yayi ya shige motar
yana mai cewa
“Ba za ku haukata ni ba,
wallahi!”.
Shi dai Daddy
shiga yayi ya zauna a kusa da shi, yana son tambayarshi
wata zuciyar kuma sai ta bashi shawarar ya bari ya Dad d’in ya d’an sauk’o tukunna sai suyi magana…
A haka drivern ya ja su suka nufi Gandun Albasa
Daddy yana mamakin meye haka yake damun Dad??
Dan tabbas ya san akwai abunda aka yi mishi......
GANDUN ALBASA.
Baaba Talatu tana fita harabar gidan ta tarar gurin har ya fara kachamewa!
Dan bayan Sakina ta bar wajen Umma da Anty Zainab kan Ummu suka dawo
wai “ai itace bata yi mata tarbiyya mai kyau ba shiyasa ta raina manya har haka...”
Ga kuma wannan tsohuwa ita ma ta kafa ta tsare tace
“Sai Ango ya fito tukunna za a fara gabatar da komai!”
Yayinda Ummu da wasu cousins d’inta suke ta k’ok’arin ganin sun yayyafa wa lamarin ruwa amman abun ya faskara!.
Baaba Talatu ce ta k’arasa ta ja wannan tsohuwar gefe suka had’u ita da Shuwa suna mata magana k’asa k’asa…
Ganin kamar ana shirin fara traditional event d’in
cikin kwanciyar hankali ne yasanya Umma ta sake cewa
“Nima fa kamar uwa nake a wajen Hudan!
Dan haka ba zan bari kowa ya tab’a ta ba har sai Angon nata ya k’araso..
idam kuma fasawa yayi ne to kawai a fito a fad’a wa mutane sai a fasa sakata a lallen,
dan ba girman mu bane mu tsaya muna yiwa mutane wasa da hankali!
Ko ya kuka gani?”
Ta k’arashe maganar tana kallon cousins d’in Ummu waenda suke gefen ta! Ba su kad’ai ba kusan kaff wajen babu wanda bai ji abinda tace ba hatta su Shuwa.
“Ga Angon nan”
Muryar Mommy wadda suka fito su uku yanzu ta daki dodon kunnuwansu!
Da sauri Mama da Aslam suka kalleta!
Ba tare da ta kallesu ba ta
kama hannun Aslam ta fara janshi
Mama na binsu a baya kamar rak’umi da akala shi kuma yana binta!..
Bata cikashi ba sai da ta kaishi gefen Hudan sannan ta zaunar da shi.
Da sauri Ummu ta matso k’asa k’asa tace
“Mommy a Al’ada fa dole sai Angon zai....
Cikin katseta Mommy tace
“A addini fa?”
Bata jira Ummu ta bata amsa ba ta sake ce mata
“Kalla nan kinga”
Tayi maganar tana
nuna mata Huda wadda sai a lokacin Ummu ta lura da yanda mayafinta ya jik’e sharkaf!
Wanda kana gani ka san ruwan hawaye ne…
Mommy bata jira jin me zata ce ba ta ci gaba da yi mata magana k’asa k’asa irin na masu hankali,
tace
“Saboda ita kawai ki bari ayi a gama!
Na tabbatar ba wai rashin zuwan Arshaad kad’ai bane ya saka ta kuka ba! Har da maganganun matar nan! Tun muna parlourn bayankun nan muke juyo komai.
Dan Allah kar kice a’a!
Kalla kiga mutane kowa ya zuba ido an fara k’ananun maganganu, na tabbatar in dai ba Angon suka gani ba to haka za a tashi ana gulmace gulmace shima kuma sai idan an samu waenchan matan sun bari anyi d’in kenan.
Na tabbatar mutane k’alilan ne kuma na jikinku sosai suka san ba Arshaad bane wannan, ba kowa ne zai gane ba
so dan Allah ki kwantar da hankalinki ayi abun nan a gama without any more dramas.
Saka lalle ai ba d’aurin aure bane ba, ba komai kawai bidi’a ce so mu bisu kawai ayi a gama.”
Tana gama fad’an haka ta juya ga jamaar wajen tace
“Kuyi hak’uri mun yi latti wani d’an uzuri ne ya tsaida mu!
Sunana Hajiya Aisha
Maman Ango, mun gode kwarai da zuwanku dan taya mu farin ciki.”
Daga nan ta juya ta cewa
Ummu
“Ni zan fara ko ke?”
Da murmushi kwance akan fuskarta.
Kallonta kawai suke yi
daga Ummu har Mama.....……