Sashe 65
So Da Buri Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Auwal bai damu da yanayinshi ba dan shi ganinsa ma da yayi a zaune ko shirin tafiya bayayi shi yafi komai b’ata masa rai!
Cikin muryar b’acin rai yace
“Haba Arshaad!
Ka sa mutane sun tara jama’a kai kawai ake jira kazo ka wani zauna anan, me kake jira?
Gaka nan dai a shirye tsaf!
Mai kuma ya hana ka tafiya tun d’azun?
Nace maka ina zan taho karka jira ni.
Ka san yanda hankalinsu ya tashi kuwa?
Dagajin muryar Sakina ka san ba lafiya ba!
Taso mu tafi da sauri dallah”
Wata nannauyar ajiyar zuciya Arshaad ya sauk’e kafin a hankali ya samu ya d’an bud’e lumsassun dogayen idanuwanshi, sai da Auwal ya d’an zabura
sakamokon had’a ido da suka yi da Arshaad d’in!
Da kyar ake iya hango maroon eye balls d’inshi da suka b’uya cikin jajawur d’in idanun nasa.
Sai a lokacin Auwal ya lura da yanda jijiyoyin kanshi suka fito sukai rud’u rud’u!
Da sauri ya k’arasa ya zxauna a gefen shi kafin yace
“Lafiya kake??
Me ya sameka haka?”
Ya jera mishi tambayoyin
duk ya rikice.
Banda ajiyar zuciya ba abunda Arshaad yake ta faman sauk’ewa yama kasa yi mishi magana
Da kyar ya samu yace
“Mammy ce ta….”
Sai kuma yayi shiru.
Cikin firgici da tsoro
Auwal yace
“Ta hana ka zuwa??
Lumshe ido Arshaad yayi kafin a hankali yace
“Har ma auren! Tace idan aka d’aura sai ta tsine min!”
A zabure Auwal ya mik’e
kafin yace
“Innalillahi wa innailaihirrajiun!
Shine kuma ka zauna za ka kashe kanka haka?
Zama ai bai ganmu ba!
Bara in je in samu su Dad in yi musu bayani, idan ta kama har Granpa sai a sa a case d’in.
Mai yasa Mammy zata yi mana haka?”
Ya k’arashe maganar kamar mai shirin fashewa da kuka.
A hankali Arshaad d’in yace
“Ba wanda bai sani ba.
Kowa ya san da case d’innan.
Har mamanta da sisters d’inta duk an bata hak’uri amman tak’i hak’ura.”
Wata kakkausar ajiyar zuciya Auwal d’in ya sauk’e kafin yace
“Ya aka yi Mammyn ta sani?
Last time da naje na dubasu naga kamar duk basu san da zancen ba..
Na san dama suna iya causing problems shiyasa nima ban yi gigin fad’a musu komai ba!
Ko maybe Ummi da aka kawo ce ta kirasu ta gaya musu?”
Da d’an mamaki Arshaad d’in yake kallon shi kafin ya sauk’e ajiyar zuciya yace
“Baka had’u da Mom ba hala?
Sun dawo jiya.
All of them”
Da mamamki shima Auwal d’in yake kallonshi ya ma kasa cewa komai.
A hankali Arshaad ya sauk’e ajiyar zuciya kafin yace
“Auwal do me a favour..
Ka kira Sakina, inaso kayi mata bayanin komai
amman kace kar ta fad’awa kowa kawai a san yanda zaai a gudanar da event d’in ba tare da an jira ni ba!
Yanzu na san Mammy idonta a kaina yake dan tun d’azu nake lura tanata turo Aaima tana mata patrol so ba zan iya fita ba.
Sakina is smart she’ll know what to do yanzun
In shaa Allah ni kuma anjima da daddare za mu je
Ina son ganin Hudan
na san abunda zan yi.
For now amman kawai ka lallab’a mun Sakina tayi handling komai, kafin nan da anjima.”
Cike da gamsuwa Auwal d’in ya d’aga kai alamar to
sannan ya zaro waya ya fara kiran Sakina.
Tun lokacin da aka fara rangad’a gud’a taji
dan haka ta mik’e ta lek’a ta windown d’akin Shuwa..
Ji tayi kamar ta zuba ruwa a k’asa ta sha sakamokon hango su su biyu a zaune da ta yi!
Bata ganin fuskar su especially Huda da har yanzu tata fuskar a lullub’e take sannan windown a rufe ne kuma sun yi mata nesa..
Bata san lokacin da hawayen farin ciki suka zubo mata ba!
Tana gani yanda mata suke zuwa suna d’an d’aga mayafin kad’an suna shafa mata da hannuwanta shi kuma a tafukan hannunshi da goshinsa ake shafawa
sannan su ajjiye musu gift a cikin d’an kwanon da aka ajjiye wasu kuma kud’i.
Ba k’aramin burgeta suka yi ba, banda kalmar ‘Alhamdulillah’ ba abunda taketa nanata
a ranta tana mamakin dalilin da ya sanya Aaima karkacewa ta gilla mata wannan uwar k’aryar haka
Wata zuciyar kuma tace maybe an gyara abunne Mammyn ta sauk’o
cikin kawar da tunanin a ranta tace
“Chan ta matse musu”
Sannan ta hau raya yanda zata yiwa Arshaad in sun had’u na k’in d’aukar wayarta da yayi.
K’arar wayarta dake kan gado ce ta katse mata tunani
dan haka ta isa ta d’auki wayar..
Kamar ba zata d’auka ba
ganin sunan Auwal ne sai
kuma ta d’anyi murmushi a ranta tace
‘Kar In zama kaza mana’
dan haka ta d’auka ta kara a kunnenta kafin yace komai tace
“Gashi chan Ya Arshaad d’in yazo suna zaune ana saka su a lalle.
Thanks for your time”
Tana gama fad’in haka ta katse kiran.
Da mamaki suka kalli juna shi da Arshaad dan a hands free wayar take
Shiruu, d’akin ya d’auka chan kuma Auwal yace
“Bara inje wajen maybe ko fushi suka yi shiyasa tayi min gatse”
Cikin katseshi Arshaad yace
“Kaje wajen Mom mana.
Kace bama ka san ta dawo ba
bayan a gida d’aya kuka kwana.
Kaje wajenta daga nan
ka d’an lallab’ata
may be in tasa baki Mammy ta hak’ura.”
Har ya d’anyi gaba sai kuma ya juyo yace
“Su kuma fa?”
“Kar ka damu na gama tsara komai, zuwa anjima da daddare za muje in shaa Allah.
Zan sameka a gida.”
Cewar Arshaad yana mai maida kanshi da lumshe ido dan kanshi ba k’aramin ciwo yake yi ba amma kuma har ga Allah y’ar maganar da ya samu suka yi da Auwal ya d’an ji sassauci a ranshi.
“Allah ya kaimu”
Shine kawai abunda Auwal yace yana me fita daga d’akin
da waya kare a kunnen shi still yana sake kiran Sakina
sai dai har ya tsinke bata d’auka ba.
A tsakiyar main parlourn suka kusa yin karo da Aaima,
kasancewar hankalinshi naga wayarshi yana turawa Sakina message.
D’agowa yayi yana kallonta
itam ma shi take kallo kafin da kyar ta iya cewa
“Ya Auwal Ina wuni”
“Fine”
kawai yace yana me wuce ta.
Da sauri ta sha gabanshi kafin tace
“Am dan Allah gida zaka je?”
Maida hankalinshi yayi a wayar kafin yace
“Eh”
A hankali tace “Owk, d’an jirani plss
Mammy ta bani sak’o wajen Mom ina so zan kai mata.
Bara in d’auko vail d’ina”.
Ba tare da ya kalletaba ya k’arasa kan d’ayan daga cikin kujerun parlourn ya zauna still yana danna wayarshi.
Ta fahimci yaren kuramen nashi dan haka ta wuce sama da d’an sauri …
Bayan 5 minutes ta sauk’o!
Ta chanza kaya daga atamfar ankon dake jikinta
ta d’aura bak’ar abaya tayi rolling, ta sanya lipstick da powder. Ta yi kyau kuwa ba laifi.
Gabanshi tazo ta tsaya sannan tace “muje”
Tun kafin sauk’owarta daman ya san ta taho sakamokon k’amshin turarenta da ya karad’e parlorn! Tana sauk’owa kuwa ya lura da ita amman sai ya kawar da kai…
Wai me Aaima take nufi ne?
Ya kasa gane kanta kwana biyun nan! Har magana take mishi ta WhatsApp yanzu.
Yana tunawa lokacin da suke tare yasha gaya mata yana matuk’ar son yaga mace da black abaya tayi rolling abun yana burgeshi shiyasa
kusan duk lokacin da zasu fita tare takan yi irin wannan shigar kuma ta san baya son native cloth kwata kwata
Inba riga da wando ba to abaya…..
“Mu tafi, na shirya”
Muryarta ta katse shi.
Kallonta yake yi tun daga sama har k’asa! Hakan kuwa ba k’aramin dad’i yayi mata ba.
A hankali taji yace
“Ina sak’on??”
Diriricewa tayi kafin da kyar tace
“Yana cikin purse d’innan”
Tayi maganar tana nuna mishi purse d’inta wadda ta saka iya wayarta da lipstick a ciki.
Ajiyar zuciya ya sauk’e
kafin ya mik’e yayi gaba….
Shi fa har ga Allah kunyar ta yake ji a halin yanzu..idan
ya tuna irin yanda ya fito mata k’iri k’iri ya fad’a mata abunda yake buk’ata daga gareta da kuma yanda ya furta mata kalmar ‘ba ya k’aunarta’
Wasu abubuwan da yawa da ya yiyyi idan yana tunasu a yanzu sai ya dinga ji kamar k’asa ta tsage ya shiga!
Tabbas Daddy yayi gaskiya daman ya tab’a gaya mishi
‘’’Akwai ranar dana sani!Ranar da zaka ji inama ana yin reverse ayi maka domin ka samu ka aikata alkhairi ka kuma goge duk wani abun da kayi marar kyau.
Ranar tana nan zuwa, ko bayan raina za kace na fad’a maka‘’.
Tabbas kuwa tun kafin aje ko Ina gashi ranar ta zo
Ya san dalilin da ya sanya Sakina take gudunshi ta kuma k’i sa! Bai wuce akan tunanin da take yi na alak’ar shi da cikin jikin Jalila ba ne…..bai san
wanne kalar kallo zata yi masa ba idan taji tabbas cikin nasa ne!
Ballantana kuma azo kan maganar halayyarshi
da baya fatan Allah yasa Sakina ta sani!
So yake ya gyara komai
ya zama mutumin da ta ambata tana son kasancewa tare da! Gashi already yana da competition, yanzu ahaka ma ta riga ta nuna mishi ta zab’i Ashraff a kansa
ina kuma ga idan taji wata magana akanshi!
Ya kenan?….,
“Innalillahi wa innailaihirrajiun”
Itace kalmar da ya ambata yana mai dafa motar shi
dan har sun iso bakin motar.
Da sauri Aaima tace
“Subahanallah Ya Auwal mai ya faru?”
Tana mai matsowa inda yake.
Sai da ya d’an runtse idanunsa kafin ya dawo dai dai tukunna ya samu yace mata
“Ba komai, shiga mu tafi”
Yana mai zagayawa ya bud’e mazaunin driver ya zauna.
Tana shigowa ya tada motar yaja suka fita.
Har suka isa mansion d’in nasu babu wanda ya samu damar furta kalmar ‘a’ a cikin su.
Shi ya fara fita daga nan itama ta fito suka nufi ciki.
Suna shiga parlourn suka tarar da Jalila ta d’aura k’afa d’aya kan d’aya ga remote a hannunta tana ta chanja channel…
Lumshe idanuwanshi yayi a hankali ya shak’i iska ya furzar sannan ya bud’e idanuwan nashi
a hankali a fili yace
“My worst regret!!”
Ya kasa gaba ya kasa baya.
Cikin muryar b’acin rai yace
“Haba Arshaad!
Ka sa mutane sun tara jama’a kai kawai ake jira kazo ka wani zauna anan, me kake jira?
Gaka nan dai a shirye tsaf!
Mai kuma ya hana ka tafiya tun d’azun?
Nace maka ina zan taho karka jira ni.
Ka san yanda hankalinsu ya tashi kuwa?
Dagajin muryar Sakina ka san ba lafiya ba!
Taso mu tafi da sauri dallah”
Wata nannauyar ajiyar zuciya Arshaad ya sauk’e kafin a hankali ya samu ya d’an bud’e lumsassun dogayen idanuwanshi, sai da Auwal ya d’an zabura
sakamokon had’a ido da suka yi da Arshaad d’in!
Da kyar ake iya hango maroon eye balls d’inshi da suka b’uya cikin jajawur d’in idanun nasa.
Sai a lokacin Auwal ya lura da yanda jijiyoyin kanshi suka fito sukai rud’u rud’u!
Da sauri ya k’arasa ya zxauna a gefen shi kafin yace
“Lafiya kake??
Me ya sameka haka?”
Ya jera mishi tambayoyin
duk ya rikice.
Banda ajiyar zuciya ba abunda Arshaad yake ta faman sauk’ewa yama kasa yi mishi magana
Da kyar ya samu yace
“Mammy ce ta….”
Sai kuma yayi shiru.
Cikin firgici da tsoro
Auwal yace
“Ta hana ka zuwa??
Lumshe ido Arshaad yayi kafin a hankali yace
“Har ma auren! Tace idan aka d’aura sai ta tsine min!”
A zabure Auwal ya mik’e
kafin yace
“Innalillahi wa innailaihirrajiun!
Shine kuma ka zauna za ka kashe kanka haka?
Zama ai bai ganmu ba!
Bara in je in samu su Dad in yi musu bayani, idan ta kama har Granpa sai a sa a case d’in.
Mai yasa Mammy zata yi mana haka?”
Ya k’arashe maganar kamar mai shirin fashewa da kuka.
A hankali Arshaad d’in yace
“Ba wanda bai sani ba.
Kowa ya san da case d’innan.
Har mamanta da sisters d’inta duk an bata hak’uri amman tak’i hak’ura.”
Wata kakkausar ajiyar zuciya Auwal d’in ya sauk’e kafin yace
“Ya aka yi Mammyn ta sani?
Last time da naje na dubasu naga kamar duk basu san da zancen ba..
Na san dama suna iya causing problems shiyasa nima ban yi gigin fad’a musu komai ba!
Ko maybe Ummi da aka kawo ce ta kirasu ta gaya musu?”
Da d’an mamaki Arshaad d’in yake kallon shi kafin ya sauk’e ajiyar zuciya yace
“Baka had’u da Mom ba hala?
Sun dawo jiya.
All of them”
Da mamamki shima Auwal d’in yake kallonshi ya ma kasa cewa komai.
A hankali Arshaad ya sauk’e ajiyar zuciya kafin yace
“Auwal do me a favour..
Ka kira Sakina, inaso kayi mata bayanin komai
amman kace kar ta fad’awa kowa kawai a san yanda zaai a gudanar da event d’in ba tare da an jira ni ba!
Yanzu na san Mammy idonta a kaina yake dan tun d’azu nake lura tanata turo Aaima tana mata patrol so ba zan iya fita ba.
Sakina is smart she’ll know what to do yanzun
In shaa Allah ni kuma anjima da daddare za mu je
Ina son ganin Hudan
na san abunda zan yi.
For now amman kawai ka lallab’a mun Sakina tayi handling komai, kafin nan da anjima.”
Cike da gamsuwa Auwal d’in ya d’aga kai alamar to
sannan ya zaro waya ya fara kiran Sakina.
Tun lokacin da aka fara rangad’a gud’a taji
dan haka ta mik’e ta lek’a ta windown d’akin Shuwa..
Ji tayi kamar ta zuba ruwa a k’asa ta sha sakamokon hango su su biyu a zaune da ta yi!
Bata ganin fuskar su especially Huda da har yanzu tata fuskar a lullub’e take sannan windown a rufe ne kuma sun yi mata nesa..
Bata san lokacin da hawayen farin ciki suka zubo mata ba!
Tana gani yanda mata suke zuwa suna d’an d’aga mayafin kad’an suna shafa mata da hannuwanta shi kuma a tafukan hannunshi da goshinsa ake shafawa
sannan su ajjiye musu gift a cikin d’an kwanon da aka ajjiye wasu kuma kud’i.
Ba k’aramin burgeta suka yi ba, banda kalmar ‘Alhamdulillah’ ba abunda taketa nanata
a ranta tana mamakin dalilin da ya sanya Aaima karkacewa ta gilla mata wannan uwar k’aryar haka
Wata zuciyar kuma tace maybe an gyara abunne Mammyn ta sauk’o
cikin kawar da tunanin a ranta tace
“Chan ta matse musu”
Sannan ta hau raya yanda zata yiwa Arshaad in sun had’u na k’in d’aukar wayarta da yayi.
K’arar wayarta dake kan gado ce ta katse mata tunani
dan haka ta isa ta d’auki wayar..
Kamar ba zata d’auka ba
ganin sunan Auwal ne sai
kuma ta d’anyi murmushi a ranta tace
‘Kar In zama kaza mana’
dan haka ta d’auka ta kara a kunnenta kafin yace komai tace
“Gashi chan Ya Arshaad d’in yazo suna zaune ana saka su a lalle.
Thanks for your time”
Tana gama fad’in haka ta katse kiran.
Da mamaki suka kalli juna shi da Arshaad dan a hands free wayar take
Shiruu, d’akin ya d’auka chan kuma Auwal yace
“Bara inje wajen maybe ko fushi suka yi shiyasa tayi min gatse”
Cikin katseshi Arshaad yace
“Kaje wajen Mom mana.
Kace bama ka san ta dawo ba
bayan a gida d’aya kuka kwana.
Kaje wajenta daga nan
ka d’an lallab’ata
may be in tasa baki Mammy ta hak’ura.”
Har ya d’anyi gaba sai kuma ya juyo yace
“Su kuma fa?”
“Kar ka damu na gama tsara komai, zuwa anjima da daddare za muje in shaa Allah.
Zan sameka a gida.”
Cewar Arshaad yana mai maida kanshi da lumshe ido dan kanshi ba k’aramin ciwo yake yi ba amma kuma har ga Allah y’ar maganar da ya samu suka yi da Auwal ya d’an ji sassauci a ranshi.
“Allah ya kaimu”
Shine kawai abunda Auwal yace yana me fita daga d’akin
da waya kare a kunnen shi still yana sake kiran Sakina
sai dai har ya tsinke bata d’auka ba.
A tsakiyar main parlourn suka kusa yin karo da Aaima,
kasancewar hankalinshi naga wayarshi yana turawa Sakina message.
D’agowa yayi yana kallonta
itam ma shi take kallo kafin da kyar ta iya cewa
“Ya Auwal Ina wuni”
“Fine”
kawai yace yana me wuce ta.
Da sauri ta sha gabanshi kafin tace
“Am dan Allah gida zaka je?”
Maida hankalinshi yayi a wayar kafin yace
“Eh”
A hankali tace “Owk, d’an jirani plss
Mammy ta bani sak’o wajen Mom ina so zan kai mata.
Bara in d’auko vail d’ina”.
Ba tare da ya kalletaba ya k’arasa kan d’ayan daga cikin kujerun parlourn ya zauna still yana danna wayarshi.
Ta fahimci yaren kuramen nashi dan haka ta wuce sama da d’an sauri …
Bayan 5 minutes ta sauk’o!
Ta chanza kaya daga atamfar ankon dake jikinta
ta d’aura bak’ar abaya tayi rolling, ta sanya lipstick da powder. Ta yi kyau kuwa ba laifi.
Gabanshi tazo ta tsaya sannan tace “muje”
Tun kafin sauk’owarta daman ya san ta taho sakamokon k’amshin turarenta da ya karad’e parlorn! Tana sauk’owa kuwa ya lura da ita amman sai ya kawar da kai…
Wai me Aaima take nufi ne?
Ya kasa gane kanta kwana biyun nan! Har magana take mishi ta WhatsApp yanzu.
Yana tunawa lokacin da suke tare yasha gaya mata yana matuk’ar son yaga mace da black abaya tayi rolling abun yana burgeshi shiyasa
kusan duk lokacin da zasu fita tare takan yi irin wannan shigar kuma ta san baya son native cloth kwata kwata
Inba riga da wando ba to abaya…..
“Mu tafi, na shirya”
Muryarta ta katse shi.
Kallonta yake yi tun daga sama har k’asa! Hakan kuwa ba k’aramin dad’i yayi mata ba.
A hankali taji yace
“Ina sak’on??”
Diriricewa tayi kafin da kyar tace
“Yana cikin purse d’innan”
Tayi maganar tana nuna mishi purse d’inta wadda ta saka iya wayarta da lipstick a ciki.
Ajiyar zuciya ya sauk’e
kafin ya mik’e yayi gaba….
Shi fa har ga Allah kunyar ta yake ji a halin yanzu..idan
ya tuna irin yanda ya fito mata k’iri k’iri ya fad’a mata abunda yake buk’ata daga gareta da kuma yanda ya furta mata kalmar ‘ba ya k’aunarta’
Wasu abubuwan da yawa da ya yiyyi idan yana tunasu a yanzu sai ya dinga ji kamar k’asa ta tsage ya shiga!
Tabbas Daddy yayi gaskiya daman ya tab’a gaya mishi
‘’’Akwai ranar dana sani!Ranar da zaka ji inama ana yin reverse ayi maka domin ka samu ka aikata alkhairi ka kuma goge duk wani abun da kayi marar kyau.
Ranar tana nan zuwa, ko bayan raina za kace na fad’a maka‘’.
Tabbas kuwa tun kafin aje ko Ina gashi ranar ta zo
Ya san dalilin da ya sanya Sakina take gudunshi ta kuma k’i sa! Bai wuce akan tunanin da take yi na alak’ar shi da cikin jikin Jalila ba ne…..bai san
wanne kalar kallo zata yi masa ba idan taji tabbas cikin nasa ne!
Ballantana kuma azo kan maganar halayyarshi
da baya fatan Allah yasa Sakina ta sani!
So yake ya gyara komai
ya zama mutumin da ta ambata tana son kasancewa tare da! Gashi already yana da competition, yanzu ahaka ma ta riga ta nuna mishi ta zab’i Ashraff a kansa
ina kuma ga idan taji wata magana akanshi!
Ya kenan?….,
“Innalillahi wa innailaihirrajiun”
Itace kalmar da ya ambata yana mai dafa motar shi
dan har sun iso bakin motar.
Da sauri Aaima tace
“Subahanallah Ya Auwal mai ya faru?”
Tana mai matsowa inda yake.
Sai da ya d’an runtse idanunsa kafin ya dawo dai dai tukunna ya samu yace mata
“Ba komai, shiga mu tafi”
Yana mai zagayawa ya bud’e mazaunin driver ya zauna.
Tana shigowa ya tada motar yaja suka fita.
Har suka isa mansion d’in nasu babu wanda ya samu damar furta kalmar ‘a’ a cikin su.
Shi ya fara fita daga nan itama ta fito suka nufi ciki.
Suna shiga parlourn suka tarar da Jalila ta d’aura k’afa d’aya kan d’aya ga remote a hannunta tana ta chanja channel…
Lumshe idanuwanshi yayi a hankali ya shak’i iska ya furzar sannan ya bud’e idanuwan nashi
a hankali a fili yace
“My worst regret!!”
Ya kasa gaba ya kasa baya.