Sashe 12
So Da Buri Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Binta kawai yake yi da ido, tanata karairaya…
A hankali yasa hannu ya zarota daga jikinshi kafin yace
“Ki kawo mini abincina sama, kaina yana d’an yi min ciwo.”
Murmushi ta kuma saki kafin tace “ok dear”
Ta juya, shi kuma ya kama hanyar b’angaren shi.
Sai da taga hayewarshi
sannan taje wajen Mom ta rad’a mata wata magana, a take suka kwashe da dariya
kafin Mom d’in tace “ki tabbatar kin yi amfani da abunda na baki.”
Dariya tayi sannan tace “da gudu ma kuwa” kafin ta nufi hanyar kitchen tanata rawar kai!
A nutse ta sake gyara kulolin har da ruwan tea tayi mishi warming da duk wani abunda ta san zai buk’ata.
Haka nan ta had’o abincin a k’aton baske tayi saman itama.
Abba yana shiga d’aki ya kira Dad…bayan sun gaisa ya zayyanewa Dad d’in komai bai b’oye mishi ba!
Dad was very shocked daga jin Abba yana da y’a da Maryam!!
Tabbas shima ya na zargin waenda Abban yake zargi…
Maganar Abban ce ta katse mishi tunani jin yana cewa “Yaya kayi hak’uri da abunda zan aikata, dan Wallahi ko waye yake da hannu, a cikin lamarin nan zan hukuntashi!!Ba zan duba relationship d’in ka da shi ba, gaskiya.”
Ajiyar zuciya Dad ya sauk’e sannan yace “Kayi kwakkwaran bincike, kafin In k’araso, in shaa Allah ni da kaina zan tayaka hukunta masu laifi…..
Daman jikin Mommy ne ya d’an tsaidamu amma da tuni mun iso ma.”
A haka Ummi ta shigo ta sameshi, yana ganinta ya yiwa Yaya sallama ya katse wayar.
A hankali ta k’araso ta ajjiye kafin cikin nutsuwa da karairaya ta hau serving nashi. Sai da ta gama ta ajjiye mishi a kan kafet sannan ta d’ago hannuwanta tace
“Kaga k’unshi da nayi saboda na san kanaso, in je a zana min bak’in flower ko ka fi son shi ahaka??”
Fararaen hannun nata ya kalla da jan lallen ya yiwa matuk’ar kyau amma sai dai shi memokon yaga kyan shi ma, gaba d’aya sai yaji ya tsani jan lalle a take a lokacin!.
“Ki barshi haka.”
Shine kawai abinda ya iya fitowa daga bakinshi.
Mamakin yadda idanunsa suka kad’a suka jazirr!! take
Chan kuma sai tayi murmushi..yanayin yadda ya shigo jikinshi a sanyaye, da kuma yadda yanzu taga yanayinshi tabbas ta gane mai yake buk’ata!
Hakan yasa ta fara k’ok’arin mik’ewa dan ta samu taje ta yi amfani da abunda Mom ta bata.
“Na had’u da Maryam yau...”
Wata mahaukaciyar razana tayi kafin ta koma ta zauna kamar wadda aka jawo da k’arfi!!!.
Kafeta yayi da idanuwanshi…
Yana ganin yadda gaba d’aya ilahirin jikinta yake karkarwa ga wata uwar zufa da take keto mata dukda kuwa sanyin ACn da ya ratsa ko wacece kusurwa ta d’akin.
Ya akai suka had’u?
A ina suka had’u?
Sun yu magana kenan?
Ta fad’a mishi komai?…
Sune tambayoyin da suka taru suka sake gigitata!
D’agowa tayi za tayi magana, sai kuma taga yadda ya zuba mata lulu eyes d’inshi da sukai jaa, wanda sai yanzu ne ta gane b’acin raine, ashe.
Tattaro duk wata basira da wayon da Allah ya bata tayi kana ta had’a da y’ar ragowar jarumta da kwarin jikinta, kafin tace
“Wannan kuma matsalarkace!
Tunda har ka bijirewa Mahaifinki wanda yayi ik’irarin tsine maka a kanta, to me yasa ni zan tsaya damuwa da kishi?”
Tana gama fad’in haka ta fara k’ok’arin mik’ewa, dan tabbas In taci gaba da zama to nan da nan zai b’aro jirginta.
Dukda cewa bata da tabbacin Maryam d’in ta gaya mishi sunada baby tare, amman hatta muryarta rawa take yi, sannan idanuwanta duk sun kawo ruwa! Ga shi kuma Abban ya tsare ta da ido, it’s like akwai abinda yake son fahimta…
Dan haka ta mik’e tayi hanyar k’ofar fita da sassarfa.
Abinda bata saniba shine
tun a reaction d’inta na farko Abba ya riga ya b’aro jirginta, gashi kuma yanzu rashin wayonta na son barin d’akin ya sake tabbatar mishi! Dan haka yayi hanzarin mik’ewa shima, ya rigata isa ga k’ofar ya shiga gabanta ya tsaya!.
Kasa d’agowa tayi ta kalleshi..
He can feel yadda numfashinta suke korar juna daga inda yake tsaye!.
Juyawa kawai yai ya murza key d’in ya zare shi, sannan ya cilla cikin aljihun wandon shi.
A take razana da firgicin da take ciki suka sake hauhawa!
Tun ba ma daya juyo taga yadda ya tamke fuska kamar bai tab’a dariya ba, zata iya rantsuwa tunda aka haifota duniya bata tab’a ganin Abba a irin wannan yanayin ba.
Cikin dakakkiyar muryar da bata da alamun wasa a cikinta yace
“Ummi!! A cikin biyun nan, inaso ki zab’i d’aya.”
Yayi maganar yana mata alamu da y’an yatsun hannunshi na dama daya d’aga mata su daidai setin fuskarta.
Na farko
Ko ki gaya min gaskiya tun farko abunda ya faru…yadda kuka yi kuka rufe ba tare da kowa ya ji ba, da yadda aka y munanan kalaman da ban san na rubuta suba suka isa ga Maryam,
Inason jin komai da komai karki b’oye min ko, alif.
Ko kuma (na biyu)
In yi miki dukan mutuwar da ko Mahaifiyar ki in da ace zata dawo duniya ba lalle ta shaidakiba, sannan in k’ara miki da saki, kuma in kulle ki dake da duk wanda ya taimaka miki.!
Sannan inaso ki sani sharia zan yi ta gaskiya yadda ko Granpa bai isa ya kwatoki ba wallahi, idan kuma ya tilastamin to tabbas zamu iya samun matsala da shi dan ba zan iya yi mishi biyayya wajen wofantar da hukunta waenda suka raba ni da y’ata ba!.”
Wani irin mahaukacin bugawa k’irjin Ummi ya hau yi, especially ma da taji zancenshi na k’arshe.
Amma Maryam an yi shegiyar mata!! Wato fad’a mishi tayi kenan! Yanzu Ina mafita?? K’aryatawa za tayi ko kuma ya zata yi?
Itakam yau ta shiga tara ma ba uku ba!
Ga shi ba Mom a kusa.
“Innalillahi wa inna ilaihirrajiun”
Ta fara maimaitawa tana neman taimakon Ubangiji, dan tabbas shi kad’ai ne zai iya cetonta a hannun Abba a yau.
Tsawar da ya daka mata ne, ya katse mata tunanin, a take ta durk’ushe a wajen ta fara kuka.
“Ba kya ji na ne!!!!”
Ya fad’a cikin hargowa
har wata kwalla tana zuba daga idonshi tsabar b’acin rai.
Shiru tayi in banda kuka ba abunda take yi.
Dukan mace kwata kwata baya cikin tsarin Abba
But Ummi left him with no other choice, bai san lokacin da ya fincikota ya mik’ar da ita tsaye ba!
Bata gama sosa, gefen wuyanta da takeji kamar ta yanke sakamokon janyotan da yayi da hannun rigarta ba, taji sauk’ar wani irin gigitaccen Marin da ya kusan d’auke mata nunfashi, bata gama dawowa dede ba ya sake d’auke ta da wani!
Cikin tsananin b’acin rai yace
“na fahimci option 1 kika d’auka!”
Sannan ya juya ya nufi wardrobe da sassarfa.
Da sauri Ummi wadda take ji kamar an yi mata b’arin wuta a kumatunta duka biyu ta k’arasa jikin k’ofar tana bubbugawa tana neman taimako, dan ta lura Abba baya a haiyyacinshi…
Babu wanda ya jiyota, dan k’ofofin gidan gaba d’aya sound proof ne, ko bayaga haka ma yanayin girman gidan ba lalle a iya jiyota ba!
Bata ankara ba taji ya janyota da dukkan k’arfin shi ya zuga mata belt…wani mahaukacin ihu tayi ta fad’a kan gado ta rarumo blanket da quilt d’in kai ta k’udundunu a ciki.
Cikin zafin nama ya fincike bargunan yayi cilli da su sannan ya shak’o ta, kafin yasa dukkanin k’arfin da Allah yayi mishi ya fincikota daga kan gadon ya tsayar, still yana rik’e da wuyanta da ya yiwa muguwar shak’a!
Ita ya shak’e amman yadda idonshi yayi jaaa zaka d’auka shi aka shak’e!.
Cikin d’acin zuciya yace
“na fasa sakinki da kaiki kotu Ummi kashe ki zan yi kowa ya huta!!”
Ummi kuwa ganin Abba yana shirin kaita lahira ne ya sanya ta fara dukan hannunshi, tana tarin wahala, da y’ar ragowar muryar data ragemata tayi amfani wajen cewa
“Za.z.Zan fa ff fad’a”
Tana kallon kwayar idanunsa waenda take hango tsananin tashin hankali a cikinsu.
Jifa yayi da ita sannan cikin b’acin rai ya juya mata baya kafin yace
“Ina jinki, kuma kar kiyi kuskuren b’ata mini lokaci, dan ba zan baki wani chance d’in a karo na biyu ba.”
Ajiyar zuciya kawai take ta faman sauk’ewa mai had’e da tarin wahala…
Jin shiru ya sanya shi juyowa
yana mata wani irin kallo.
Ganin haka yasata fara magana
“Ranar bayan mun ji labarin sakin da kayi mata….
Muna zaune da ni da Mom, kawai sai ga Daniel ya zo a rikice….dama duk wani abu idan ya faru ya kan fara fad’a mana kafin Granpa, in na dannewa ne mu danne ko kuma mu sakashi ya juya zancen sai mu bashi kud’i.
To kamar kullum haka ranar ma yazo mana da takardar sak’on Maryam, yake cewa ‘k’anwarta ce ta kawo kuma tace dan Allah a baka tana waje tana jira’
Ba komai ne a cikin takardar ba fa ce
‘Baka hak’uri da take yi akan duk laifin da tayi maka har ya kaika ga d’auke k’afa wanda ita bata san laifin ba! Sannan tana buk’atar ka a asibiti zata haihu.’
A lokacin kusan sumewa nayi, dan ni ko had’a shimfid’a baka yi da ni amman ita Maryam gata harda ciki zata haihu! Kuma na tabbatar muddin kaji labarin cikin nan to baza ka tab’a yarda mu koma ba, sannan definitely zaka mayar da ita tunda saki d’aya ne a tsakanin ku.
Rasa yadda za muyi mukai. Murnar mu gaba d’aya sai ta koma ciki......
Tun muna Yara Allah ya yiwa Adama baiwar kwafar duk wani zane da rubutu duk kuwa wahalarshi tsaf zata kwafe tayi irinshi exactly..
Ganin yadda duk na rikice ne yasa ta ce mini ‘inje In d’auko littafin ka’
Na fahimci me take shirin yi shiyasa da gudu, na fita naje d’akinka na kuwa ci sa’a baka nan hakan ya bani damar d’auko diary d’inka.
A hankali yasa hannu ya zarota daga jikinshi kafin yace
“Ki kawo mini abincina sama, kaina yana d’an yi min ciwo.”
Murmushi ta kuma saki kafin tace “ok dear”
Ta juya, shi kuma ya kama hanyar b’angaren shi.
Sai da taga hayewarshi
sannan taje wajen Mom ta rad’a mata wata magana, a take suka kwashe da dariya
kafin Mom d’in tace “ki tabbatar kin yi amfani da abunda na baki.”
Dariya tayi sannan tace “da gudu ma kuwa” kafin ta nufi hanyar kitchen tanata rawar kai!
A nutse ta sake gyara kulolin har da ruwan tea tayi mishi warming da duk wani abunda ta san zai buk’ata.
Haka nan ta had’o abincin a k’aton baske tayi saman itama.
Abba yana shiga d’aki ya kira Dad…bayan sun gaisa ya zayyanewa Dad d’in komai bai b’oye mishi ba!
Dad was very shocked daga jin Abba yana da y’a da Maryam!!
Tabbas shima ya na zargin waenda Abban yake zargi…
Maganar Abban ce ta katse mishi tunani jin yana cewa “Yaya kayi hak’uri da abunda zan aikata, dan Wallahi ko waye yake da hannu, a cikin lamarin nan zan hukuntashi!!Ba zan duba relationship d’in ka da shi ba, gaskiya.”
Ajiyar zuciya Dad ya sauk’e sannan yace “Kayi kwakkwaran bincike, kafin In k’araso, in shaa Allah ni da kaina zan tayaka hukunta masu laifi…..
Daman jikin Mommy ne ya d’an tsaidamu amma da tuni mun iso ma.”
A haka Ummi ta shigo ta sameshi, yana ganinta ya yiwa Yaya sallama ya katse wayar.
A hankali ta k’araso ta ajjiye kafin cikin nutsuwa da karairaya ta hau serving nashi. Sai da ta gama ta ajjiye mishi a kan kafet sannan ta d’ago hannuwanta tace
“Kaga k’unshi da nayi saboda na san kanaso, in je a zana min bak’in flower ko ka fi son shi ahaka??”
Fararaen hannun nata ya kalla da jan lallen ya yiwa matuk’ar kyau amma sai dai shi memokon yaga kyan shi ma, gaba d’aya sai yaji ya tsani jan lalle a take a lokacin!.
“Ki barshi haka.”
Shine kawai abinda ya iya fitowa daga bakinshi.
Mamakin yadda idanunsa suka kad’a suka jazirr!! take
Chan kuma sai tayi murmushi..yanayin yadda ya shigo jikinshi a sanyaye, da kuma yadda yanzu taga yanayinshi tabbas ta gane mai yake buk’ata!
Hakan yasa ta fara k’ok’arin mik’ewa dan ta samu taje ta yi amfani da abunda Mom ta bata.
“Na had’u da Maryam yau...”
Wata mahaukaciyar razana tayi kafin ta koma ta zauna kamar wadda aka jawo da k’arfi!!!.
Kafeta yayi da idanuwanshi…
Yana ganin yadda gaba d’aya ilahirin jikinta yake karkarwa ga wata uwar zufa da take keto mata dukda kuwa sanyin ACn da ya ratsa ko wacece kusurwa ta d’akin.
Ya akai suka had’u?
A ina suka had’u?
Sun yu magana kenan?
Ta fad’a mishi komai?…
Sune tambayoyin da suka taru suka sake gigitata!
D’agowa tayi za tayi magana, sai kuma taga yadda ya zuba mata lulu eyes d’inshi da sukai jaa, wanda sai yanzu ne ta gane b’acin raine, ashe.
Tattaro duk wata basira da wayon da Allah ya bata tayi kana ta had’a da y’ar ragowar jarumta da kwarin jikinta, kafin tace
“Wannan kuma matsalarkace!
Tunda har ka bijirewa Mahaifinki wanda yayi ik’irarin tsine maka a kanta, to me yasa ni zan tsaya damuwa da kishi?”
Tana gama fad’in haka ta fara k’ok’arin mik’ewa, dan tabbas In taci gaba da zama to nan da nan zai b’aro jirginta.
Dukda cewa bata da tabbacin Maryam d’in ta gaya mishi sunada baby tare, amman hatta muryarta rawa take yi, sannan idanuwanta duk sun kawo ruwa! Ga shi kuma Abban ya tsare ta da ido, it’s like akwai abinda yake son fahimta…
Dan haka ta mik’e tayi hanyar k’ofar fita da sassarfa.
Abinda bata saniba shine
tun a reaction d’inta na farko Abba ya riga ya b’aro jirginta, gashi kuma yanzu rashin wayonta na son barin d’akin ya sake tabbatar mishi! Dan haka yayi hanzarin mik’ewa shima, ya rigata isa ga k’ofar ya shiga gabanta ya tsaya!.
Kasa d’agowa tayi ta kalleshi..
He can feel yadda numfashinta suke korar juna daga inda yake tsaye!.
Juyawa kawai yai ya murza key d’in ya zare shi, sannan ya cilla cikin aljihun wandon shi.
A take razana da firgicin da take ciki suka sake hauhawa!
Tun ba ma daya juyo taga yadda ya tamke fuska kamar bai tab’a dariya ba, zata iya rantsuwa tunda aka haifota duniya bata tab’a ganin Abba a irin wannan yanayin ba.
Cikin dakakkiyar muryar da bata da alamun wasa a cikinta yace
“Ummi!! A cikin biyun nan, inaso ki zab’i d’aya.”
Yayi maganar yana mata alamu da y’an yatsun hannunshi na dama daya d’aga mata su daidai setin fuskarta.
Na farko
Ko ki gaya min gaskiya tun farko abunda ya faru…yadda kuka yi kuka rufe ba tare da kowa ya ji ba, da yadda aka y munanan kalaman da ban san na rubuta suba suka isa ga Maryam,
Inason jin komai da komai karki b’oye min ko, alif.
Ko kuma (na biyu)
In yi miki dukan mutuwar da ko Mahaifiyar ki in da ace zata dawo duniya ba lalle ta shaidakiba, sannan in k’ara miki da saki, kuma in kulle ki dake da duk wanda ya taimaka miki.!
Sannan inaso ki sani sharia zan yi ta gaskiya yadda ko Granpa bai isa ya kwatoki ba wallahi, idan kuma ya tilastamin to tabbas zamu iya samun matsala da shi dan ba zan iya yi mishi biyayya wajen wofantar da hukunta waenda suka raba ni da y’ata ba!.”
Wani irin mahaukacin bugawa k’irjin Ummi ya hau yi, especially ma da taji zancenshi na k’arshe.
Amma Maryam an yi shegiyar mata!! Wato fad’a mishi tayi kenan! Yanzu Ina mafita?? K’aryatawa za tayi ko kuma ya zata yi?
Itakam yau ta shiga tara ma ba uku ba!
Ga shi ba Mom a kusa.
“Innalillahi wa inna ilaihirrajiun”
Ta fara maimaitawa tana neman taimakon Ubangiji, dan tabbas shi kad’ai ne zai iya cetonta a hannun Abba a yau.
Tsawar da ya daka mata ne, ya katse mata tunanin, a take ta durk’ushe a wajen ta fara kuka.
“Ba kya ji na ne!!!!”
Ya fad’a cikin hargowa
har wata kwalla tana zuba daga idonshi tsabar b’acin rai.
Shiru tayi in banda kuka ba abunda take yi.
Dukan mace kwata kwata baya cikin tsarin Abba
But Ummi left him with no other choice, bai san lokacin da ya fincikota ya mik’ar da ita tsaye ba!
Bata gama sosa, gefen wuyanta da takeji kamar ta yanke sakamokon janyotan da yayi da hannun rigarta ba, taji sauk’ar wani irin gigitaccen Marin da ya kusan d’auke mata nunfashi, bata gama dawowa dede ba ya sake d’auke ta da wani!
Cikin tsananin b’acin rai yace
“na fahimci option 1 kika d’auka!”
Sannan ya juya ya nufi wardrobe da sassarfa.
Da sauri Ummi wadda take ji kamar an yi mata b’arin wuta a kumatunta duka biyu ta k’arasa jikin k’ofar tana bubbugawa tana neman taimako, dan ta lura Abba baya a haiyyacinshi…
Babu wanda ya jiyota, dan k’ofofin gidan gaba d’aya sound proof ne, ko bayaga haka ma yanayin girman gidan ba lalle a iya jiyota ba!
Bata ankara ba taji ya janyota da dukkan k’arfin shi ya zuga mata belt…wani mahaukacin ihu tayi ta fad’a kan gado ta rarumo blanket da quilt d’in kai ta k’udundunu a ciki.
Cikin zafin nama ya fincike bargunan yayi cilli da su sannan ya shak’o ta, kafin yasa dukkanin k’arfin da Allah yayi mishi ya fincikota daga kan gadon ya tsayar, still yana rik’e da wuyanta da ya yiwa muguwar shak’a!
Ita ya shak’e amman yadda idonshi yayi jaaa zaka d’auka shi aka shak’e!.
Cikin d’acin zuciya yace
“na fasa sakinki da kaiki kotu Ummi kashe ki zan yi kowa ya huta!!”
Ummi kuwa ganin Abba yana shirin kaita lahira ne ya sanya ta fara dukan hannunshi, tana tarin wahala, da y’ar ragowar muryar data ragemata tayi amfani wajen cewa
“Za.z.Zan fa ff fad’a”
Tana kallon kwayar idanunsa waenda take hango tsananin tashin hankali a cikinsu.
Jifa yayi da ita sannan cikin b’acin rai ya juya mata baya kafin yace
“Ina jinki, kuma kar kiyi kuskuren b’ata mini lokaci, dan ba zan baki wani chance d’in a karo na biyu ba.”
Ajiyar zuciya kawai take ta faman sauk’ewa mai had’e da tarin wahala…
Jin shiru ya sanya shi juyowa
yana mata wani irin kallo.
Ganin haka yasata fara magana
“Ranar bayan mun ji labarin sakin da kayi mata….
Muna zaune da ni da Mom, kawai sai ga Daniel ya zo a rikice….dama duk wani abu idan ya faru ya kan fara fad’a mana kafin Granpa, in na dannewa ne mu danne ko kuma mu sakashi ya juya zancen sai mu bashi kud’i.
To kamar kullum haka ranar ma yazo mana da takardar sak’on Maryam, yake cewa ‘k’anwarta ce ta kawo kuma tace dan Allah a baka tana waje tana jira’
Ba komai ne a cikin takardar ba fa ce
‘Baka hak’uri da take yi akan duk laifin da tayi maka har ya kaika ga d’auke k’afa wanda ita bata san laifin ba! Sannan tana buk’atar ka a asibiti zata haihu.’
A lokacin kusan sumewa nayi, dan ni ko had’a shimfid’a baka yi da ni amman ita Maryam gata harda ciki zata haihu! Kuma na tabbatar muddin kaji labarin cikin nan to baza ka tab’a yarda mu koma ba, sannan definitely zaka mayar da ita tunda saki d’aya ne a tsakanin ku.
Rasa yadda za muyi mukai. Murnar mu gaba d’aya sai ta koma ciki......
Tun muna Yara Allah ya yiwa Adama baiwar kwafar duk wani zane da rubutu duk kuwa wahalarshi tsaf zata kwafe tayi irinshi exactly..
Ganin yadda duk na rikice ne yasa ta ce mini ‘inje In d’auko littafin ka’
Na fahimci me take shirin yi shiyasa da gudu, na fita naje d’akinka na kuwa ci sa’a baka nan hakan ya bani damar d’auko diary d’inka.