← Book details So Da Buri Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 37 OF 70

Sashe 37

So Da Buri Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Alwalar tayi ba yadda ta iya, ta kashe famfunan, ta tsaya tana kallon fuskarta a mudubi.

Jin yayi knocking yasa gabanta mugun fad’uwa!
Ita kam yau ta ga talatar kanta, gashi ba daman tace tana fashin sallah!
Da kyar ta iya daurewa ta fice, k’irjinta na dukan uku uku.

Suna k’arasowa, Sakina ta mik’a mata vail d’in da ta cire a jikinta d’azu ta ajjiye
tace “Bismillah”
Fisgewa tayi tana hararar ta.
Murmushi Sakina tayi kafin tace
“Yarinya yau ko idanunki zasu fad’o k’asa sai kin rantse!”….
********************** ⬇ **************************
********** Ai Hausa Novels ****************
*************************⬆ **********************

DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog.

Visit > https://www.aihausanovels.com.ng

Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post.

Email > [email protected]

******* FOLLOW US ******

Facebook: Ai Hausa Novels

Twitter: Ai Hausa Novels

Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels

WhatsApp Number: 08138873799

Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu.

********************** ⬇ **************************
*************** Ai Hausa Novels ****************
********************** ⬆ **************************
……A nan fa ake yinta, ga Jalila ga Al Qur’ani a gabanta ga jama’a kowa ya zuba mata ido…
Parlourn yayi shiruuuu.

Ba abunda yafi bawa Arshaad mamaki irin yanda Auwal ya d’auke wuta diff!!! Don gaba d’aya kamar babu shi a wajen..

Shi kam Auwal yana chaan ya sha’afa da kallon Sakina kamar ya samu tv, sam! Bai damu da kalar harar da take zabga masa a duk sanda suka hada ido ba! Babu abunda yafi tafiya da imaninshi kamar idanuwanta waenda idan ta kalleshi dasu yake ji gaba d’aya kamar an zare mishi lakka bayan fad’uwar gaban da yake tsintar kanshi a ciki..duk wata hayaniyar shi yau ya ji babu ita, yanaso yasa baki a lamarin su Jalilan amman ya kasa, don bashi da wani sauran energy, gaba d’aya jikin shi yayi lakwass!!!.

Sakina kuwa so take ta gama da Jalila ta koma kanshi idan bai daina yi mata wannan kallon k’urillar ba!.
Hudan tana lura dasu, dan haka ta gama aiyyanawa a ranta suna komawa d’aki zata zaiyyanewa Sakinan waye shi!!
Kar ma ta soma bashi fuska dan ita tun zuwan su Munjibir park ta gama aminta da Auwal ba mutumin kirki bane ba!.

...duk sunyi shiruuu, kowa da abunda yake tunani a ranshi.

Nishi suka fara ji sama sama,
da sauri duk suka juya kanta..
Wani lumlumshe ido take yi tana layi, kafin ta tafi luuuu ta fad’i akan kafet d’in!
Da mugun sauri Sakina ta d’auki robar ruwan dake gefenta ta nufeta, ta na zxuwa ta bud’e murfin ta kelaya mata
ruwan mai mugun sanyi dan har da k’ank’ara k’ank’ara ma a ciki!!

Ai kuwa a firgice Jalila ta bud’e idonta tana wani mugun tari dan ruwan har cikin hancinta ya shige sosai….
Da kyar ta samu ta seseta kanta ta fara k’ok’arin mik’ewa,
tana mikewa kuwa ta d’aga hannunta zata zabgawa Sakina mari shi kuma Arshaad a take ya rik’e hannun da sauri.

Wani kalan shock taji a jikinta da wani sanyi a zuciyarta wanda ya sanyata kasa yin motsi!
A hankali ta lumshe idanunta tanajin yanda laushin hannun nashi yake ratsa jini tsoka da b’argonta.

Muryarsa ce ta dawo da ita duniyar su, jin cikin fad’a fad’a yana cewa
“Jalila kin fara isata wallahi ranki zai yi mugun b’aci!
Inada abun yi amman kin tsaya sai b’ata mana lokaci kike yi!!
Sannan meye na yunk’urin marin nata da kika yi?
Ina taimakarki tayi?
Kar ki kaini bango, ranki zai b’aci wallahi kinji dai na rantse!!.”
Ya fad’i hakan cikin tsananin b’acin rai sannan yayi wurgi da hannun nata, ya wuce ya k’arasa ya durk’usa a wajen, ya fara kokarin dafawa….

Kuka kawai yaji Huda ta saka dan haka da sauri ya sago ya kalle ta.
Cikin kukan tace
“Ya Arshaad da Allah fa na had’a ka, nace maka komai ya wuce amman still kak’i ka yarda ka hak’ura, itama Ya Jalilan ku barta kawai, ni na fahimci gaskiya, dan Allah ku daina , Al Qur’ani fa ba abun wasa bane ba..”
Tana gama fad’an haka ta juya ta haye sama da gudu,,tana kuka.

Mik’ewa Arshaad yayi ya dafa kanshi, ya kusan one minute a haka kafin ya juya yana kallon Sakina yace
“Kice mata nace idan cikin ya kai 5 ko 7 months in shaa Allah za aje ayi dna test, plss kar tace a’a,,for me.”
Yana gama fad’in haka bai jira amsar Sakina ba ya juya ya fice.

Haushin su ne ya hana Sakina ci gaba da zama a inuwa d’aya dasu, dan haka ta juya ta haye sama itama.

Da k’arfi Jalila ta sauk’e ajjiyar zuciya, bata gama dawowa dede ba taji Auwal ya fincikota da mugun k’arfi, cikin b’acin rai yace
“Wanne shirme da iskancine ya sa kika biyo shi in the first place??? Mahaukaciya mara kamun kai kawai!! Daga ji ance tazo a tafi ta shige mota ta biyo mutum zungui zungui. Wallahi yau da wani abun ya fito, toda da hannun nan nawa zan illataki, mahaukaciya kawai.”
Ya k’arashe maganar yana sakin ta sannan ya juya yayi hanyar waje.
Da sauri ta mik’e ta bishi…..

Ba k’aramin artabu suka sha ba a wajen ma, daga k’arshe dai ya hak’ura ya mik’ata gida, yanata faman zazzaga mata ruwan bala’i!
Daga nan yace “yayi grounding d’inta! Ko wajen umma kar ta yi gangancin tambayarshi
Daga yau babu inda zata sake fita har sai yayi sorting out ma kanshi solution!”
sannan yace “ko hanya tabi in dai ta hango Arshaad to ta chanja!
Don ya lura sam Arshaad d’in bai hak’ura ba, ita kuma wawuya ce, so kasancewar su tare is very dangerous for him.”
Ita dai Jalila da “to” kawai ta bishi amman a yanda take jin Arshaad a ranta ai ko labari taji ance zai bi ta waje to fa ita mai iya zuwa ta tsayane ta jira wucewarshi.

A gate d’in estate d’in ya tsaya yace “ta fita!”
Allah ya so ta mai gadin yaga motarshi kuma ya ganeta dan haka aka barta ta shige.

Ko da Aslam yazo, Hudan Sakina ta bawa ta kai masa ruwan karatun…
Dinner kam dama a k’oshe suke, gaba d’aya kunyar Arshaad take ji bataso su had’u, iyakar yadda Ya Jalila tayi ta acting ya ishi yasa ta gane gaskiya….ita sai yanzu ma take ganin shiriritarta da ta yarda da su!
A gefe guda kuma na zuciyar ta tausayin Jalilan take ji.
Yayinda gaba d’aya hankalinta kuma yau ya d’unguma ga son ganin Mama
dan har yau Ummu tak’i d’aukar wayarta, wayar Sakina ma ta daina amsawa!
Tanaso ta tambaya amman kuma bata son zuwa k’asan dan haka ta yiwa Abban message.

Ba a fi mintuna uku ba, taga reply dinshi kamar haka
“Ok, no problem, but let it be tomorrow.”

Taso zuwa yau d’in, amman ta tura
“Thanks Abba ❤️”
Kawai, ta mik’e tayi sallah..
Yau basu wani zauna hira sosai ba,,ta dai fad’awa Sakina halin Auwal tace “Don taga yanata kallonta kar yazo mata da shirme”
Dariyan takaici Sakinan tayi kafin tace ,
“First, kin dai san akwai wanda naki dating, right?
Second, ga abunda ya yiwa Jalila sannan ya k’ulla makirci wai Ya Arshaad ne.
And third, wallahi ni bana son irin waennann mazan kwata kwata yana yinsa bai yi min ba at first sight!”.

Ajiyar zuciya Hudan tayi kafin tace “Duk cikin su Ya Arshaad shi ya fita daban i don’t know why.”
Murmushi Sakina tayi kafin tace “d’an halak, gashi yana kiranki.”
Tayi maganan tana mik’a mata wayar ta dake a hannunta.
Karb’a tayi ta amsa
bayan sun gaisa ta fara son sake bashi hak’uri amman sam yak’i yarda, a cewarshi bata laifi a gurinshi……..
Tun Sakina najin hiran su sama sama har bacci ya kwasheta bata san lokacin da suka gamaba.
Ranar ansha soyayya abun ba a magana dan sai wajen 2 tukunna suka yi hanging up, suka kwanta.

Bata samu magana da Sakina ba, kamar yadda ta yanke zata nemi shawarar ta jiya,
sai da suka sauk’o yin breakfast…
Suna zuwa suka tarar ba kowa dan haka suna zama Huda tace
“Daman akwai maganan da nake ta so muyi in mun gama shiryawa”

“Ok, akan me?”
Sakina ta fad’a tana mai d’an juyowa ta bata dukkannin attention d’inta.”

A hankali Hudan tace
“Ya arshaad ne, daman already ya yiwa su Abba maganan!
So yanzu jiya yace, wai ya nake gani,,jiya sun yi magana da Dad wai sun tsaida in anzo saka rannan za asa two months ne ba wani lokaci za a dauka mai tsawo ba!”

“Woow”
Sakina tace tana d’an zaro idanuwanta, kafin tace
“Amma hakan bai yi wuri ba kuwa?”

Da sauri Huda tace “nima dai abunda na gani kenan!
Amman dana nuna mishi tun kafin ma In furta sai naga kamar bai ji dad’i ba.
Wai shima yana so ya tafi wani course, so kafin a juya sabon session yake son samamun admission sai muje chan ni Ina degree shi kuma yana course din, nashi.”

Dai dai nan suka ji sauk’owar Abba, dan haka
a hankali Sakina wadda duk jikinta yayi sanyi jin za a rabata da best frnd d’inta
tace
“Anjima ma ji me su Mama za suce, in munje.”

Cikin girmamawa suka gaisheshi ya amsa da kulawa yana ce musu “ai da sun fara kawai”

Sai da suka kammala ya kalli Hudan yace “ki cewa Arshaad idan ya dawo a office ya zo, ku zo tare Ina son ganin ku!”

Da “to” ta amsa, shi
kuma ya tambaya ko “akwai abinda suke buk’ata zai fita shima” a hankali tace “a’a” sukai yi mishi a dawo lafiya, ya wuce.

Gidan shiru, daga su sai masu aiki…
Tun lokacin da Abba ya fita take nazari a kanshi, kamar akwai abunda yake damunshi, dan har sai da ta yiwa Sakina maganar…
Murmushi Sakina tayi kafin tace “Hudan he just knew you fa, kuma yanzu ana shirin aurar da ke, dole yaji ba dad’i mana.”
Chapter 37 · 0% Book details